Pages

Friday, 22 December 2017

Keep and regrow the edges of ur hair.👧👩

[12/22, 12:25 PM] Baby: Treatments for regrowing your edges.
• Rubbing the thinning areas with oil or oil mixture treatments can help in re-growing hair in those areas. These treatments will reduce the damage on your edges by repairing the follicles and encourage hair growth.
For example, rubbing your scalp with vitamin E is a great way to stimulate growth.
 •The SheaMoisture Raw Shea Butter Deep Treatment Masque is great. You can warm it up a little bit and massage it into your scalp.
• Castor oil (especially Jamaican Black Castor Oil), JBCO is the unrefined version of Castor Oil. This means the full health benefits and nutrients were not lost during processing. A daily or weekly (depending on the severity) deep edges massage will greatly improve circulation and stimulation of the hair follicle.
Other oils you can add to castor oil or use as a replacement are olive, coconut, jojoba and sweet almond oil.
• Peppermint Oil & Jojoba Oil
Similarly to Jamaican Black Castor Oil, Peppermint Essential Oil is an antibacterial known for removing impurities causing growth obstructions. Its cooling effect also relaxes the follicle, promoting healthy hair growth. Since Jojoba (carrier oil) is the oil closest to that of our own natural oils, it is the best choice for a carrier oil.
A soothing carrier oil is needed with peppermint oil because of how potent it can be.
[12/22, 12:25 PM] Baby: • Another great natural and effective mixture is Basil Oil( Scent leaves oil/Efirin in yoruba) and Jojoba. Consistent and weekly pre-poo (before cleansing) with this mixture will improve hairline with major results.
• Aloevera oil or gel is also okay for growing edges.
 • Try a light protein treatment mixed with moisturizer and massage it into your scalp to
stimulate the growth
• Onion and ginger are also very good in regrowing edges.
• Sleeping on a satin pillowcase
Start sleeping on a satin pillowcase instead of a cotton one because the cotton pillowcase will absorb the natural oils and moisture right out of your hair. The friction between your hair and cotton pillowcase can lead to breakage. Your edges need those oils and moisture when they are thinning, so pamper them with the right nighttime treatments.
• At the very least a daily multi-vitamin will aid in hair growth. Also nutritious diets are required.
• Scalp massage
Scalp massage stimulate the skin and encourage the blood vessels to increase blood flow and boost circulation to the scalp and hair follicles. This increased circulation brings more nutrients and oxygen to the hair follicles and may aid in hair growth. Which oils to use is less important than the actual act of massaging and this can be done without oil, as the purpose is to encourage circulation.
When you massage, it is important to only use the pads of your fingers; don't rake over this sensitive area with fingernails. Move around in a gentle, circular pattern for a few minutes each day. Don't press down firmly on your hairline.
How often do you massage your edges? You need to do this once every 2 days for 2 months nonstop.
• Remember I said earlier that tight buns and ponytails are bad for edges! Well, you don't have to give up entirely on styles just to regrow your edges.
There are so many natural hairstyles for thin edges that you can choose from. Twist and braid outs do not require that your hair is pulled tightly. Also, loose high puffs using a shoe string or an old stretched out headband are alternative updos without stressing the edges.
• Hydrate
Hydrating your edges is a major key in regrowth and maintaining health. Spritzing your edges with water or aloe vera juice and adding oil afterward is a great way to make sure your edges remain most hydrated and doesn’t become brittle.
When our hair is dry, it becomes brittle and more prone to breakage.
Moisturizing, as usual, will be the key to maintaining healthy edges and promoting growth.

Regrowing your edges needs time and consistency. If you continue to avoid styles that put too much strain or stress on your hairlines, reduce manipulation and nourish your edges they will grow back but it takes consistency. It may take a while before you notice improvement, but it is well worth the wait.
Read More »

DO U WANT TO KEEP HAIR NATURAL?? Here are some steps to follow.

[12/22, 12:25 PM] Baby: Keeping Your Natural Hair On A Budget.
Natural hair can look a little discouraging because of different kinds of expensive natural hair care products out there.
Yes! Natural hair is an expensive venture if you don't know your way!
You don't need to have so much unnecessary products all over your shelf, and you don't neccessarily have to buy all hair care products you see or hear about.
Don't be a product junkie! The basic things that will ensure you enjoy your natural hair journey and have awesome results is understanding your hair porosity, type and density.
When you know your hair better, you will be able to build your hair care regime, know what works for you and then put it on a budget!
[12/22, 12:25 PM] Baby: But first, what is your budget? Trust me, it is very easy to get carried away with products, it is even the easiest thing!
You need to put your natural hair on a budget. To plan a budget the following tips will help you go about it:
1. You need to allocate a particular amount for products and ensure you follow it.
2. Next, study your hair. Know the kind of products that are applicable and what are not beneficial to your hair.
Find out what works for your hair and stick to it. Product junkism might not allow your hair thrive.
3. Make enquiries before buying any product. Ensure you have satisfiable reviews on such product before you buy it. Often times, some of these products are just hype, nothing else.
4. Finally, you really do not need to go an extra length saving money to get expensive products if you have the basics of doing it yourself.
You can do most of these hair care products yourself! DIY hair recipes are sometimes much more reliable and effective.
You can totally manage your natural hair on your budget. Don’t let anyone convince or tell you otherwise.
[12/22, 12:25 PM] Baby: The basic operations usually carried out in the natural hair journey are:
• Pre poo
• Shampooing
• Deep Conditioning
• Protein treatment
• Clarifying of scalp
• Cowashing
• After wash rinse
• Moisturizing
• Styling.
[12/22, 12:25 PM] Baby: For bad or thin edges, take note of the following:
• Avoid tight hairstyles
Hair edges may eventually get thinner or bald when wearing tight hairstyles frequently, which pulls the edges. The ponytail hairstyles that are also in braids may put stress on hair edges. When wearing braids avoid wearing a ponytail with the braids, because it will pull the hair edges and the edges will eventually get thinner.
• Stay away from gels that contain alcohol
There are gels for natural hair that don't contain alcohol and have no negative effect on edges. For example, Eco Styler Gel
[12/22, 12:25 PM] Baby: • Keep face cleanser and toner from touching your edges.
Most face cleansers contain alcohol, care should be taken when applying on face so that it doesn't touch your edges. The effect of face cleanser and toners that have  alcohol is that it drys out your hairline. Once your hairline drys out it will become weak and eventually break off.
[12/22, 12:25 PM] Baby: • Avoid the use of brush on your edges.
• Wearing tight satin caps with non- satin borders
If your satin bonnet or cap is too tight or is not satin around the edge you are doing more harm than good. Just sleep using satin pillowcase, bonnets or caps that are too tight around your edges are not a good idea.
• Using glues, adhesives, or wig caps
The use of glues, adhesives, and wig caps won't allow your scalp to breathe, and yes it needs air! Some women are even experiencing allergic reactions to the glues and adhesives, which do not always appear immediately. If you are trying to regrow your edges, I suggest you stay away from them.
[12/22, 12:25 PM] Baby: Treatments for regrowing your edges.
• Rubbing the thinning areas with oil or oil mixture treatments can help in re-growing hair in those areas. These treatments will reduce the damage on your edges by repairing the follicles and encourage hair growth.
For example, rubbing your scalp with vitamin E is a great way to stimulate growth.
 •The SheaMoisture Raw Shea Butter Deep Treatment Masque is great. You can warm it up a little bit and massage it into your scalp.
• Castor oil (especially Jamaican Black Castor Oil), JBCO is the unrefined version of Castor Oil. This means the full health benefits and nutrients were not lost during processing. A daily or weekly (depending on the severity) deep edges massage will greatly improve circulation and stimulation of the hair follicle.
Other oils you can add to castor oil or use as a replacement are olive, coconut, jojoba and sweet almond oil.
• Peppermint Oil & Jojoba Oil
Similarly to Jamaican Black Castor Oil, Peppermint Essential Oil is an antibacterial known for removing impurities causing growth obstructions. Its cooling effect also relaxes the follicle, promoting healthy hair growth. Since Jojoba (carrier oil) is the oil closest to that of our own natural oils, it is the best choice for a carrier oil.
A soothing carrier oil is needed with peppermint oil because of how potent it can be.
Read More »

Thursday, 21 December 2017

SOYAYYAR MU👫.
     By Ganarious.
2⃣1⃣
Ki yanke min ko wata irin hukunci amma karki yi fushi dani....ni kadai nasan yanda naji a raina ganin ki haka.Don Allah ina rokonki kar ki karayin irin wannan fushin,nasan nayi laifi kuma a shirye nake da na dauki hukuncin da za'ayimin amma ba da wannan ba.
 Ba san sa'anda hawaye ya zubomin ba,ina me kallonsa nace "kafada min dalilinka na rashin zuwa duba mu..kuma yaushe kaji na haihu?
  Ya sa hannunsa ya sharemin hawayen,sannan yace Bani da lafiya ne!.
Nan da nan na rude,na kuma shiga tausaya masa ..ina fadin "ya jikin?
Na ji sauki hamdala...
Nan ta'ke mu manta komai muka shiga hira irin ta masoya masu shaukin juna...sai da yaro ya fara kuka sannan fa muka tuna yana gun,fillo ya taka zuwa gun gadon ya dauko shi.
  Ya dawo gefena yana me kallon jaririn,nikuma ina shafa kansa(shi jaririn).
Yayi murmushi yace tabdijam...wannan d'an kam ba'ki ne,muka tuntsire da dariya sabida yanayin da yayi furucin.
 Ai nice sak...wannan ba'kin nawa ne....sabida haka sai kawai ka sanya masa sunnan baba na.
 Da sauri ya kalle ni,yace kin so kanki da yawa! Duk da nima zan so haka  .
Wannan kam Baban mahaifiyata ne domin kuwa shima din ba'kin buzu ne ,kamar wannan jaririn.
Ahmadu shine sunan da aka sanyawa yaron,sai nake kiransa da MUJAHEED..wannan  jaririn shima akwai shi da shiga rai.
  Wata biyu nayi na koma gida.
Abu kamar wasa tunda muka koma gida fillo bai leko mu ba,har zamu shiga sati na uku..sai nake tunanin wata kila bashi da lafiya ne kuma...
Sabida tunanin haka na shiyar ranar asabar,tare da yin girke-girke don kaimasa.
Hisham da ilham sashen binta na kaisu sannan na nufi zaria.
Gidan da nayi zama alokacin da nake karatu nan yake zaune shima,don haka ban wani yi wahalan neman gida ba.
Na tarar da gidan a rufe,da alama baya nan kenan.
Na dade tsaye ina tunane-tunanen abinyi sai wata zuciyar na rayamin wata kila yana hanyar kadunan....
A zuciya ta nace ko da yana garin ban san lokacin dawowansa ba...ina cikin wannan tunanin mujaheed ya fara motsi,ya tashi daga baccin kenan.
Wai waiga  na gani ko zan sami gun zama,ai ssi nayi ido hudu da fillo cikin mota.
Motan nan tana gun sa'anda na  wuce domin kuwa ta gefen ta na bi amman tunani bai bani da na kalli cikin motan ba balle mutanen cikinsa.
    Wata fara mace ce a gefe,daga alama itace mai motar don zaune take a kujeran direba.
Muna hada ido da naji zuciyata na ras-ras da karfi...
Kallonsa nake shima hakan,sai kuma ya maida kallonsa ga matar suka ci gaba da maganarsu.
  Na da'de ban dauke idona daga gareshi ba,har sai da mujaheed ya fara kuka...
 na rasa mafita gashi ba gun zama,gashi fillo bai zo ya bude mana kofa ba...duk sai na rude cikin kankanin lokaci.
Kuka yake sosai..niko sai girgiza shi nakeyi ba tare da na sa'ko shi daga baya na ba...muna cikin haka fillo ya fito daga motan,ita kuma ta ja motan ta wuce.
Ya karaso inda nake tsaye ya amshi mujaheed ya bude kofa yashiga ciki ya kwantar dashi.
Ya dawo ya kwashi kaya ya shigar.ya sake dawowa har zuwa wannan lokacin tsaye nake bani ko motsawa.
Ya matso gaba na,muna dab da juna domin ina jiyo numfashinsa.
  A hankali yace 'mu shiga ciki ko!.
Nan ma ban motsa ba,gashi sai ihu mujaheed keyi.
 Ya rikemin hannu ya jani zuwa ciki.
da kansa ya zaunar da ni,ya nufi gun a.c ya kunna sannan ya dawo ya dauki mujaheed yana lallashi,duk da haka yaro ya kiyin shiru.
Ya dawo gefena yana fadin don Allah ki saurari wannan yaron..
Ko kallonsa banyi ba balle na amsa shi. Shi ke kidansa,shi ke kuma rawansa...
...sai da maganar sa ta isheni na na mike a hasale,na fizgi mujaheed ina kokarin goya shi.
Shima ya mike cikin mamaki,yana kokarin rike ni,na fizge hannuna.ya sake kamo hannuna  yace don Allah kiyi hankuri kiyi min magana...
Kuka irin ta ban tausayin nan ce ta ci karfi na ...sai kawai naji ina tausawa kaina.
Da dabaransa ya samu ya zaunar dani.mujaheed kam yayi kuka har ya hakura.
ya sani ga'ba ya kallon ina kuka har sai da nayi me  isa ta.
Sai da kukan ya lafa sannan yace "haba Aisha"....nasan dai kishi ne,amman a duniya kinsan bani da kamar ki kuma ba zani sami kamar ki ba.
Read More »
SOYAYYAR MU👫.
     By Ganarious.
2⃣1⃣
Ki yanke min ko wata irin hukunci amma karki yi fushi dani....ni kadai nasan yanda naji a raina ganin ki haka.Don Allah ina rokonki kar ki karayin irin wannan fushin,nasan nayi laifi kuma a shirye nake da na dauki hukuncin da za'ayimin amma ba da wannan ba.
 Ba san sa'anda hawaye ya zubomin ba,ina me kallonsa nace "kafada min dalilinka na rashin zuwa duba mu..kuma yaushe kaji na haihu?
  Ya sa hannunsa ya sharemin hawayen,sannan yace Bani da lafiya ne!.
Nan da nan na rude,na kuma shiga tausaya masa ..ina fadin "ya jikin?
Na ji sauki hamdala...
Nan ta'ke mu manta komai muka shiga hira irin ta masoya masu shaukin juna...sai da yaro ya fara kuka sannan fa muka tuna yana gun,fillo ya taka zuwa gun gadon ya dauko shi.
  Ya dawo gefena yana me kallon jaririn,nikuma ina shafa kansa(shi jaririn).
Yayi murmushi yace tabdijam...wannan d'an kam ba'ki ne,muka tuntsire da dariya sabida yanayin da yayi furucin.
 Ai nice sak...wannan ba'kin nawa ne....sabida haka sai kawai ka sanya masa sunnan baba na.
 Da sauri ya kalle ni,yace kin so kanki da yawa! Duk da nima zan so haka  .
Wannan kam Baban mahaifiyata ne domin kuwa shima din ba'kin buzu ne ,kamar wannan jaririn.
Ahmadu shine sunan da aka sanyawa yaron,sai nake kiransa da MUJAHEED..wannan  jaririn shima akwai shi da shiga rai.
  Wata biyu nayi na koma gida.
Abu kamar wasa tunda muka koma gida fillo bai leko mu ba,har zamu shiga sati na uku..sai nake tunanin wata kila bashi da lafiya ne kuma...
Sabida tunanin haka na shiyar ranar asabar,tare da yin girke-girke don kaimasa.
Hisham da ilham sashen binta na kaisu sannan na nufi zaria.
Gidan da nayi zama alokacin da nake karatu nan yake zaune shima,don haka ban wani yi wahalan neman gida ba.
Na tarar da gidan a rufe,da alama baya nan kenan.
Na dade tsaye ina tunane-tunanen abinyi sai wata zuciyar na rayamin wata kila yana hanyar kadunan....
A zuciya ta nace ko da yana garin ban san lokacin dawowansa ba...ina cikin wannan tunanin mujaheed ya fara motsi,ya tashi daga baccin kenan.
Wai waiga  na gani ko zan sami gun zama,ai ssi nayi ido hudu da fillo cikin mota.
Motan nan tana gun sa'anda na  wuce domin kuwa ta gefen ta na bi amman tunani bai bani da na kalli cikin motan ba balle mutanen cikinsa.
    Wata fara mace ce a gefe,daga alama itace mai motar don zaune take a kujeran direba.
Muna hada ido da naji zuciyata na ras-ras da karfi...
Kallonsa nake shima hakan,sai kuma ya maida kallonsa ga matar suka ci gaba da maganarsu.
  Na da'de ban dauke idona daga gareshi ba,har sai da mujaheed ya fara kuka...
 na rasa mafita gashi ba gun zama,gashi fillo bai zo ya bude mana kofa ba...duk sai na rude cikin kankanin lokaci.
Kuka yake sosai..niko sai girgiza shi nakeyi ba tare da na sa'ko shi daga baya na ba...muna cikin haka fillo ya fito daga motan,ita kuma ta ja motan ta wuce.
Ya karaso inda nake tsaye ya amshi mujaheed ya bude kofa yashiga ciki ya kwantar dashi.
Ya dawo ya kwashi kaya ya shigar.ya sake dawowa har zuwa wannan lokacin tsaye nake bani ko motsawa.
Ya matso gaba na,muna dab da juna domin ina jiyo numfashinsa.
  A hankali yace 'mu shiga ciki ko!.
Nan ma ban motsa ba,gashi sai ihu mujaheed keyi.
 Ya rikemin hannu ya jani zuwa ciki.
da kansa ya zaunar da ni,ya nufi gun a.c ya kunna sannan ya dawo ya dauki mujaheed yana lallashi,duk da haka yaro ya kiyin shiru.
Ya dawo gefena
Read More »

SOYAYYARM 👫

SOYAYYAR MU👫.
    By A'ishah M.Gana
         (Ganarious)
1⃣9⃣.
Sai da dare yayi Babana ya sake kiranmu falonsa.
Nan yake fadin dalili kiran mu.dalilin kuwa shine batun makaranta ta.nayi farin ciki da haka domin form din makarantan Nigeria civil Aviation training center wanda a yanzu aka fi sani da The Nigeria college of Aviation technology dake zaria ya miko min,ya kuma kara yiwa fillo bayani.
Sai da nacika form din sa'anan muka koma gida.
Mamata taso na fara zuwa jami'a na farayi digiri idan yaso sai na je nan din,baba yace hakan ma yayi ba laifi..idan na gama nan din sai na shiga jami'a daga nan sai naje kasar germany watau makarantar da na baro.
Makarantar tukun jirgi dake zaria,a jihar kaduna tarihinta ba'a taba samun mace musulma daga arewa ba sai ni.
Na sa himma sosai.tukin jirgi kawai na zaba a matsayin course,shi kuma wannan course din shekaru biyu zuwa uku akeyinta.
Zaria na koma da zama,nakan shiga kaduna akai akai domin ganin fillo sabida shi baya samun lokaci...wata sa'in yana zuwa min weekends ko ni naje.
Na dawo gida a yayinda mukayi hutun farko,na iske binta da ciki nayi mata murna da fatan Allah ya sauke ta lafiya...ita kuma addu'ar ta Allah shi sa da namiji zata haifa,sai ni na haifi mace suyi aure.dariya ta bani sosai don har zuwa lokacin abin yara takeyi.
A wannan hutun shakuwar mu da binta ta karu,har idan fillo ya shigo ya ganta sai ya ba'ta rai wai tana takura masa.
         **        **           **
Ina makaranta fillo ya zo dubani,sai yake fa'damin binta ta haihu ta sami da namiji.
Nayi hamdala tare da ji mata dadi burinta ya cika na samun da namiji.
Sai da fillo ya jira na gama darasin ranar,sa'ann muka koma gida tare.bai so na biyoshi ba,nikuma nace mashi bazani iya bacci ba idan ban gan dan binta ba.
   Sashen Binta na nufa kai tsaye domin ganin jaririn.
 
Subhanalillah!!!...godiya da yabo sun tabbata ga Allah sarkin halittu...ba mahalukin da zai kalli wannan jaririn baiyi Allah zikiri ba..
Na da'de tsaye rike da yaron sai kallonsa nakeyi,so da kaunar jaririn ya mamaye min zuciya cikin kankanin lokaci.
Dariyar Binta da yan'uwata ya farkar da ni hankalina ya koma garesu sai a lokacin na tuna ashe fa bamu gaisa ba.
sai da sukayi da gaske sa'anan na bada jaririn,kafin ko na bada shi,sai da ya sha sumbatu ta ko ina.
Ina kai da komowa,zaria da kaduna  sabida wannan jaririn da ya tafi min da hankalina.
Ranar suna yaro yaci sunarsa Abubakar Assadiq. Bayan suna da kwana biyar na dawo ganin jariri,sai naji yan gidan suna kiran sa "jelodi".. cikin bacin rai nace waya sa mashi wannan sunar binta tace babansa ne.
Nace masu idan har baza su kira shi da Assadiq ba,a dinga kiransa "Hisham"....daga nan sunarsa jelodi ya mutu sai dai Hisham.
 Mamee ta dan ja numfashi,tayi shiru na dan lokacin,daga ni har Hisham ita muke kallo.
Tayi murmushi tace Hisham din kenan  a gaba na yau ina bashi labari.
A lokaci guda muka kalli juna nida Hisham,sanan muka Mayarda kallonmu ga mamee...ita ma kallonmu take tana murmusawa.
      **        ***        ****
Kyakyawan jaririn nan ya shiga raina sosai,ina sonsa.
Duk wani abu da zan samu Hisham ne.kudi na a Hisham suke karewa sai dai idan ban gan abin wasan yara ba...mamarshi ta kaiga yafeminshi sai dai kash! Ina makaranta duk da hakan nakan dawo duba shi.

A lokacin da nake rubuta jarabawar barin makaranta,shima fillo a lokacin yake jarabawar gama sekandiri skul.. duk da anyi masa tsallake.
Taro yayi taro.jama'a a makarantan mu kamar ku'da. Makaranta ta gayyaci mutane daga kasashen tsallake har cikin najeriyan ma...yan'uwa da abokan arziki sun zowa daliban don tayasu murna.
Anyi jawabai aka yayemu da za'ayi, ankuma ba da kyautuka zuwa gwarzayen shekaran.
A cikin mata,nice aka baiwa  kyautar wace tafi kowa fasha da basira fanin tuku.,kuma mace ta farko daga arewa wace ta fara zama matukiyar jirgi.
Mama ta tayi farin ciki sosai,burinta ya cika.

Bayan yan kwanaki da kammala makaranta,muna falo fillo na zaune kaina na saman kafafuwansa yana sosamin kai,gefen mu Hisham ne kwance yana baccinsa don tunda na dawo na karbo shi.
"A'isha"...fillo ya anbaci sunana.
Ba tare da na amsa ba na juyo fuska,muna fuskantar juna.
Mi kike ganin zamuyi yanzun tunda mun gama makarantar.?
Hmmmm...haka ne kuma fa.,na da'go daga kwancen na kara gyara zama nace mashi ai nawa da sauki,idan na nemi aiki zan samu.kaine dai abin zancen yanzun.
To..me kike ganin ya dace muyi yanxun?.
Wannan ba wata matsala bace.idan dai sakamakon ka ya fito kuma yayi kyau ina da tabbacin Babana zai kula da sauran..
Haka ne...Allah dai ya saka mashi da aljannar firdausi,iya abinda kawai zan kwatanta biyansa dashi kenan.
Murmushi nayi nace ko zamu kai masu gaisuwa gobe ne?
Shikenan Allah ya kaimu.
   Kashe gari tunda sassafe muka shiga kitchen ,da shike nakanyi girke-girken kalolin abincin da Babana yafiso,sai mu tafi masa dashi.

Kamar yanda na fada maku tare muke shiga kitchen da fillo,a ranar ma haka.bayan mun gama komai mun tsabtace gurin da mukayi  ayyuka mukayi wanka sa'anan na shirya hisham din shima amman kuma ba dashi zamu tafi ba,sabida wata sa'in rigima yakeyi sosai...don haka muka kaishi gun mamarsa don bada ajiyarsa kafin mu dawo.
A duk lokacin da muka je masu ziyara,Baba ji yake tamkar ranar ce farkon haduwan mu ko yayi kamar wanda ya shekare bai ganni ba.
A falonsa muka muke,bai yarda mu shiga cikin gida ba.
Abincin da muka je dashi shi sukaci.

Mama ta ce ta duba agogo,karfe biyar da minti arba'in da daya ,tace ku tashi ku tafi ko!
Shiru-shiru bamu motsa ba,ta sake magana a lokacin karfe shida dai dai.
Babana ya kalleta ya kalleni muka hada ido,da kamar magana a bakinsa amma ya kiyinsa.
Fillo ne ya mike yace toh mama.
Na sake kallon babana shima ni yake kallo,da alama ba ya son na tafi.
na juya ga mamata nace yauwa mama da abinda ya kawo mu fa .
Cikin mamaki tace lafiya dai?.
Nayi murmushi sabida yanayin kallon da tayimin nace lafiya lau.daman buba ne yace tunda na kammala karatun mizanyi yanzun shine nace sai na nemi shawaranki.
Tayi ajiyan zuciya...ku kwantar da hankalinku,innshaa'Allahu cikin watan nan zan sanar da ku abinda ya dace...shima babana ya sanya baki a maganar.
Mun tashi kenan munayi masu sallama,sai akayi kiran magrib.hajiya babbace tace mu bari a yi sallah sa'anan mu tafi
Hisham ya fara zuwa makaranta da kwana uku  akayi birthday sa na cika shekara biyu..a ranar Babana ya aikowa fillo da takadar shiga jami'a ta Ahmadu Bello university dake zaria.
Fillo yayi farin ciki da haka.farin cikin sa ya sani farin ciki. Gashi daman saura kwana biyar ayi walimarsa ta saukan al'qur'ani maigirma.
  A daren ranar baiyi bacci ba sabida farinciki...daga baya ya mike ya gabatar da sallah nafila sa'anan ya dawo inda nake ya kankame ni.
Cikin kwantar da murya yace A'isha!.
Na'am buba.
Me kike ganin zanyi wa mahaifinki ya fahimci cewan ina me matukar godiya da hasken da ya kawo wa rayuwata?
nayi murmushi tare da kankameshi yanda yayimin nace Addu'ar nan dai da kake yi masa shi zaka cigaba.
Bayan wannan fa?
ka sanya ni farin ciki har karshen rayuwta.
Bayan wannan fa?
Su kadai zakayi masa ya gamsu da godiyarka
Anyi an gama innshaa'Allah.
Yayi waige waige kamar ba dagani sai shi a falon ba.ya matso da bakinsa dai dai kunnena ya rada min wata magana da bata wuce batun haihuwa ba,wai mamarsa ta fara korafi.
Maganar sa ta ta'ba ni,sai dai na daure nayi murmushi nace addua kawai zamuyi.
  Cikin sauki da taimakon Allahu Buba fillo ya samu shi jami'an a.b.u zaria.Babana ne yayi ma sa komai,daga kan gidan da zai zauna har zuwa su abinci.
Bayan kamar wata uku da tafiyarsa makaranta,wataran na tafi gidanmu tunda safe,da shike ranar asabar ce.na tarar Babana da hajiya babba sunyi tafiya tare amman a ranar zasu dawo..mamata ce ke gida,sai yannena da basuyi aure ba sai kanina Al-ameen shima ya dawo hutu ne.
Bayan mun gaisa take fadin kamar kinsan zan aika kiranki.
Banyi mamaki ba,nasan wata abin ta samu kenan..nace sai gani!.
Ta jawo durowa ta ciro wata takarda tace gashi..ki tafi dashi ku duba,sai kuyi shawara.duk abinda kuka yanke sai ku sanar dani.
Takarda ce ta makarantar tukin jirgi dake kasar germany.watau makarantan da na fara zuwa suka maidani baya,ita dince mamata ta kara amsowa.
Cikin murna na tashi na rungumeta ina me sumbatarta tare da fadin wannan karon innshaa'allah zaki sha mamaki mamata.
Daga yanayinta zaku fahimci cewan taji dadin furucina sosai,amma ta daure tace ai sai kinyi shawara da mijinki kar mu shiga hakin sa.
A a mama....Buba  bashida matsala,asalima ya matsamin wai nayi maki magana ,ban daiyi bane don nasan da abinda kike tanadar min.
Dariya tayi tace shikenan Allah shi yi maku albarka.
Ameen na fada tare da kaimata kiss
Babana ya sani kuwa? Na tambaye ta
Yana sane.
Karfe biyu da rabi mamata ta shiga kitchen,na tashi zani taimaka mata da wasu ayyuka,sai na tsinci kaina da jin jiri...na fadama ta,tace na tafi na dan kwanta.
INa kwantawa kuwa bacci yayi awon gaba dani.
SAi da akayi kiran mangariba,Al-ameen yazo ya tada ni wai mama tace na tashi.
SAi a lokacin na tuna banyi sallar azahar ba cikin ambatar salati na mike zuwa bayi donyi alwala.
A falo na tarar da mamata tana cin tuwo
Tana ganin na fito tayi kiran al-ameen wai ya daukomin tuwo na.
na zauna a kasar falonta tare da mimmike kafafuna,don naji dadin cin tuwon
Al-ameen ya shigo rike da tire ya dire a gabana,tuwon masara ce da miyar zogale
Na kalli mamata dake nisa dani nace rabon da nagan anyi wannan tuwon a gidan nan tun ina aji uku a sakandiri.bata amsa ni ta cigaba da cin tuwonta.
Na kai loman farko,zan kai ta biyu sai kawai naji zuciya ta na tashi,da sauri na mike  sabida amai.
Amai na ke kwararawa....cikin tashin hankali da rudani mamata ta biyoni tana fadin ya'ya dai!
Na daga mata.
Kamar zan amayo ya'yan cikina ,har zuwa wannan lokacin tana rike dani,bayan aman ya tsagaita ta wanke min fuska,ta samin ruwa na kuskure baki muka fito falo.shiganmu falo aman ya sake dawowa ta sake biyo ni tana fadin bari na kaiki asibiti dai.
Yayana suleiman ke tukin mota ita kuma tana rike dani a bayan mota.
Asibiti da muka nufa mai zaman kantace wanda abokan juna suka hada kai suka gina ta,ciki harda Babana.
Duk wanda bashi da lafiya a gidanmu nan ake kaishi.
bayan gwaje gwaje da sauransu likita ya fito da sakamako,har zuwa wannan lokacin ina kwance jikinta ....da farko ya mika mata ledan magunguna sa'anan yayi mata albishir,wai ina dauke da ciki.
Tsale tayi tana hamdala.
Muna cikin haka ya shigo cikin rudani,ysna isowa inda muke ya tattaba min jiki yana fadin mamata miye same ki.
Ba komai baba!.
Sai a lokacin ya kai dubansa ga mamata yace me likta yace maku?
Albishir tayi masa tana fadin kasami jika.
Duk sunyi murna daganan muka koma gida.
Mamata bata bari na koma gidana ba wai sai na kara samun karfin jiki amman ta aika a fadawa Baba lamido da sauransu cewan bazan samu dawowa ba sabida bana jin dadi.
    Da sanyin safiya su binta suka diro a gidanmu,sun kuwa yo taron dangi...sun dan jima sa'anan sukayi min Allah shi bada lafiya suka tafi.
Binta suka bari da danta hisham...binta ta matsamin akan na fadamata ciwon da ke damuna nace mata nima ban sani ba.mamatace kawai ta sani.
Kafin binta ta wuce nayi amai ya kai so uku,duk abinda na gani idan har naci ne sai naji zuciya ta na tashi,haka yasa ta gane cikine da ni sai ta shiga zolayata tana fadin Hisham ya sami mata.
Read More »

SOYAYYARMU

SOYAYYAR MU👫.
      Written by Ganarious.

Visit Ganarious.blogspot.com/ for latest update.
1⃣8⃣.
  Kai na da'ga alamar eh.
Aisha kinsan ni mahaifinkin ne ko
Nace mashi eh!.
Kin kuma san duk cikin ya'yana na fisonki.
Eh Baba na sani.
"Ina kwana na kuma tashi da damuwa akan yanayin da nagan kin shiga,idan dai ba kinason ciwon zuciya ta kamani bane,toh ki fadamin asalin abinda ke damunki domin na nemi mafita kafin yayi nisa.

A hankali da kamar ra'da nace "Baba ina son fillo"...soyayyar da nakewa fillo ce ta jefani a wannan halin.
   Ba alamar mamaki a fuskarsa,asalima murmushi yayi sa'anan yace daman ne na kara daga bakinki.....
Ya kara fadin"shi fillon yana sonki?
Da sauri na da'ga mashi kai tare da fadin shima yana sona sosai baba.
Shikenan!ina son daga yau ki cire damuwa a ranki,zan zaunar da mahaifiyarki mu tattauna   akan matsalarki.
Gabana naji yayi ras...jin ya ambaci mamata.
Nace dashi baba ya'ya zan yi da zance makaranta na?mama zatayi fushi dani sosai,baba ko na maimaita ba tare da ta sani ba.
Murmushi yayi yace"ko kin maimaita baza ki ci ba....
...na gwalo idanuwana alaman mamakin maganar.
A hankali yake shafan kai na,tare da fadin "tare zamu koma gida gobe,idan Allah ya kaimu.
 Tare muka koma gida da babana sai dai a tsorarce nake,ga faduwan gaba!
   A kofar falonta muakayi karo da ita,tana ganinmu ta gyara tsayuwa tare da rungumar hannayenta.
Babana ya riko min hannuna domin kuwa mutuwar tsaye nayi.
Gefenta muka ra'ba zuwa  cikin falon.ta juwo tana binmu da kallo,sai da ta dauki mintuna sa'anan itama din ta karaso.
Bayan ta zauna ta samin ido kamar tana son gano wani abu,jikina kuwa sai makarkata yake.
Babana ya lura da hakan sai yace dani na tashi na shiga ciki zasuyi magana.
Bani da masaniyar maganar da sukayi a tsakaninsu.
A tunane na hukunci mai tsauri mamata yankemin,sai dai labari ya sha bambanci.
  Ban Saki jiki ba sai da na cika sati mahaifiyata ba ta canza min ba..a sati dayan ban hada ido da fillo ba,haka yasa ni kasa samun natsuwa a zuciyata.
Zaune nake a falon Babana ina karatun littafin turanci.Babana ne ya shigo,mamata na biye da shi,na sauko daga kan kujeran na rusuna ina masu sannunsu da dawowa.bayan na gaida su,na tashi zan fita a falon,babana yace na zauna za suyi magana dani.
    Yace dani "nasan kina son karatu sosai Aisha!..matsalarki daya shine son dan fillanin nan..
Aisha ina son kinsan cewa duk wani abu da kike so,idan dai mai faranta maki raine toh shi nake so kuma shi zanyi maki.
Na karanci irin soyayyar da kike yiwa dan fillanin nan kuma nayi kokarin fahimtar da mamarki.Rashin amincewar mu da soyayyarku wata illace babba,don haka ni da mahaifiyarki mun amince wa soyayyarku....idan har shima yana sonki yanda kike sonsa.,batare da cutarwa ba.
a shirye nake da na aura mashi ke...bayan auren sai ki koma makaranta,kiyi karatun ki hankali kwance.
  Na fashe da wata irin kuka me kunshe da farin ciki da kuma bakin ciki.
cikin kukan na mike a sanyaye zuwa gun babana  Na rungumeshi.
Mamata dai kallonmu takeyi ba tare da ta ce wani abu ba,amma jikina ya bani bataji dadin zancen ba.
             **          **        **
Bayan kwana hudu da Yin maganar,babana ya umurci fillo da ya shirya domin za suje ruggansu tare.
Tare da Baba Lamido suka dawo.Bayan sun huta gajiyan tafiya ne Babana ya tara mu a falonsa.ciki har da kannen sa,yannena,mamata da hajiya,fillo da Baba lamido.
Bayan addu'a da godiyar Allah! Babana yace kafin ya fara bayani,zai so yayi fillo wata tanbaya.tambayar kuwa itace 'kana son Aisha kamar yanda take sonka?
Da sauri da sauri yace "eh'eh,ina sonata...inason ta sosai"
Toh maa shaa Allah. shi nakeson ji nake kuma son yan uwanka da nawa yan uwan suji domin su duka su zama shaidu.
ya juyo gareni yace Aisha ke fa?
Kaina na jinjina batare da na fadi wani abu ba.
Shikenan..ya fada sa'anan ya cigaba da fadin ya tara su domin su gani su kuma shaida zai baiwa fillo diyarshi.
Diyata kwaya daya tak! Wacce nafiso,ban hada da komai ba.farincikin shine nawa farincikin.
idan bayan auren dan fillo yayi mata ba dai-dai ba,shi ma fa ba zani raga masa ba.shiyasa na tara ku anan ku zama mani shaida'
Sa'anan kuma bayan auren inason ta cigaba da karatun ta.
Ya kalli fillo yana fadin ina fatan zaka iya da kuma amincewa da bukatuna.
Eh na amince baba,na kuma gode maka,Allah ubangiji yasaka maka da gidan aljanna.
ya kuma kai kallonsa gun Baba lamido yace masa idan fa hakan baiyi maka ba,kai da yan'uwa toh muna marhaba da duk wata shawaran da zaku kawo.
Sun zurfafa zancen,daga bisani kanin mahaifina yace wa Baba Lamido su turo magabatansu,idan sunyi shawara.

Yan'uwan fillo sunyi shawarwari a tsakaninsu,sunyi murna sosai tare da yiwa babana godiya.
Wasun su sun zo domin yin maganar auren,nan ma Babana ya sake yi masu kashedi akan su jawa dansu kunne.
Kafin su koma ruggansu,babana ya dauke su zuwa "my precious estate"
My precious estate da ke hanyar mando,estate ne da mahaifina ya gina shi da sunana.da farko mahaifiyata ta shawarce shi da ya sanya yan haya sai a dinga saving mani kudin hayan...
Shawarar ta chanza sabida babana ya kyautarwa yan'uwan fillo estate din.
Ya umurci baba Lamido dasu dawo nan din da zama sabida shi dai kam bazai aminta da zamana a rugga ba.....cikin gine-ginen akwai sashen da aka ke'ra min,shi wannan sashen gini ne da yasamo asali daga korea.
Wani lokacin na raka babana wata semina na yan' kasuwa da masu kamfunoni,bayan seminar aka kai mu masauki,watau wata karamar hotel ne amman fa tun daga wa'jen hotel zaka rude sabida tsarinta.
Na wangale baki ina me kara kallon ginin ba abinda nake fadi sai'waw....'waw.
Babana kuwa sai murmushi yakeyi ya jin dadin gani na haka.
tsarin ginin ya tafi da hankalina,har muka dawo bani da zance sai na ginin...hakan yasa babana ya ke'be min  gefe daya a cikin estate din aka keramin ginin.

      **             **          **
Ba'a bata lokaci gun sanya ranar aurenmu ba.sabida makarata da zani koma.
     Labarin aurena da fillo ya bi gari,wasu na yabo da jinjina wa babana,wasu kuma na zaginsa,wasun ma suna mamaki har sun kai ga tsaidani a hanya don jin zancen daga bakina ko dagake ne.

Daga lokacin da aka sanya ranar aurenmu nake cikin farin ciki da anashuwa,shima fillon haka don kuwa sai da yayi sadaka da shanayensa biyu.
Mahaifiyata dai ba yabo ba fallasa.tana zani iyacewa tana son auren zani iyace wa kuma bata so ta dai amince ne sabida dalilan babana cewan idan na sami abinda nake so zan natsu nayi karatu hakan yasa ta kwantar da hankali ta tarbi zancen hannu bibbiyu.
Kawayen mamata da yan'uwan basu barta ba.suna fadin yaya za'ayi na auri wanda yafito daji!...sunaye iri-iri ba wanda basu kira fillo dashi ba.
Haka suka sa mamata gaba suna yarfa mata ruwan bala'i...idan sunyi mata sai kuma su dawo kaina suyi min...
Anty amina mamar ya'nazeer tayi magiya,tayi roko wai a fasa auren da fillo na auri nazeer dinta don shi yafi dace wa dani kuma a shirye yake ko yazun nan,amma babana ya kara jadada mata sai wanda nace ina so....tayi kira na gefe daya tace na kara tunani akan wannan auren.

Yan'uwan fillo karka-kaf dinsu sun dawo 'MY PRECIOUS ESTATE'da zama.
Ana sauran kwana hudu daurin aure ya'nazeer ya iso a birkice.sumbatu yakeyi kamar taba'be..sai fadin yake wabillahillazhi idan baki fasa auren dan dajin nan ba zan sace ki,ko na kashe kaina amma zan fara kashe ki sai kowa ya rasa.
Na tausaya mashi,na kuma tsorarta da furucinsa sai dai na fahimta ba'a cikin hayacinsa yake wadannan maganganun ba.
Baba na ya zaunar da ya'nazeer yayi masa nasiha sai dai kirikiri ya'nazeer shi bazai taba hakura dani ba.

           **        **       **
Allah ya kaimu ranar aure,an kuma daura lafiya.
Duk wani mahalukin da ya halarci wannan auren yasan ni yar gata ce ta mussaman.
Sai a ranar mamata tayi kuka domin kuwa yan'uwanta sun sat gaba fiye da zaton ku
.....tana kuka tana ce masu ya'ya suke son tayi da rayuwarta!
Ina kwance a dakina tare da kawayena na jiyo hayaniya,har zan fito sai kuma na fasa don a zatona yan taron bikin ne ke hayaniyar..sai ga wata yar uwar ta shigo,nake tambayarta "hayaniyar me akeyi"
Nan take fadamin wai mamata ce da yan'uwanta suke sa'insa, ba tare da na sauriri abinda zata fada ba na mike a guje zuwa falon mamata na kuwa yi sa'a har zuwa wannan lokacin basu daina fadamata maganganu ba.
  A gabansu na zube  ina fadin ba laifinta bane,ita ma bata son auren! Wallahi itama bata so,nice dai nakijin maganarta...don Allah kuyi hankuri
Anty saudat,itace babbansu,ta taso daga inda take zaune..tana kaiwa inda nake takaimin mari...
...kiyi wa mutane shiru! Ashe baki da mutunchi ehee! Baki da kunya har kike fadin bata so amman kin bijire mata! Ko maza sun kare a duniya ne...ehe!
toh bari kiji..tunda kin ki nazeeru,mu ma din bamu sonki. Je ki ki auri jahili amman fa duk abinda ya biyo baya ki nemi mamarki da babanki...ba mu ba ke!
A haka dai sukayita surutansu,ni kuwa ba abinda nakeyi sai kuka.
suna gamawa anty saudatu tace da sauran kannenta su tashi su tafi,ba tare da sun sallameni ko sanyawa auren albarka balleshi wai shawarwari ko rakiya.
Bayan tafiyansu na tashi nakoma inda mamata take zaune na rungume kam..ina fadin mama ki yafe min.
       **         **         **
A lokacin da za'a kai amarya watau ni kenan..Babana yayi kiran fillo da iyayensa da wasu daga cikin yan'wan babana din,da yannena da su hajiya.bayan godiya ga Allah s..w.t da ya nuna mashi ya kuma bashi ikon aurar da diyarshi.yayi bayanai akan yanda yakeji a ransa sa'anan daga baya ya jawa fillo kunne akan ya rike amana.

Yan uwan babana sai wasu daga cikin kawayen mamata sai kawayena ne sukayimin rakiya.
Yan uwan fillo sunyi murna sosai da aka kaini,sunyi kwaliaya irin ta su dai.
Kawayena sun kwana tare dani sabida walima da za'ayi da safe.
Duk sun watse bayan walima...sai a lokacin fillo ya shigo.
Kallo daya zakayi mashi ka fahimci cewan yana cikin farin ciki,sai godiya ma Allah yakeyi yana fadin Allah nagode maka na gode ma baban Aishetu...aljannace kawai zaka saka mashi dashii..kallonsa kawai nakeyi inajin son sa har a raina.
Aurenmu na neman sati uku,amman wani abu na ma'aurata bai shiga tsakaninmu da fillo ba,dalili kuwa shine karanci ko nace rashin ilimi addinin islama a tattare dashi..da kaina na bashi shawarwari neman ilimi da neman sanin yanda ake ayyuka kamar su wanka da sauransu...ba musawa sai ma farin ciki dayayi da bayanai na.
  Akwai masallaci da kuma makaranta a cikin estate din.Babana ya samo mallamai,ya basu gidajen da ba'a shiga ba.domin koyar da yan'uwan fillo.

Zaman jin dadi da annashuwa mukeyi...ba renin hankali a tsakaninmu,ina girmamashi..a matsayina na matarsa wacce ke kasa dashi.
Ban taba kawo wa rai na gatanci na ko kudin babana zai rufe min ido na kaskantashi ko maidashi kasa dani ba.Asalima sarki na maida shi domin kuwa komai nike mashi,nice ke  shafa mashi mai ajiki,nice ke yanke masa farce da sauransu.
shi din ma haka yake baya kaunar ganin na matsa kusa dashi.idan ina kitchen zai biyo ni tare muke komai,idan na gama aiki muyi gyare gyare tare..baya bari nayi aikin gida ni kadai,haka duk inda zani je,tare muke zuwa.
  Binta abin so Ya samu ta dawo birni da zama,kusan kullum tana sashena...godiya kaw sai da nayi da gaske sa'annan ta daina wai nice sanadin zuwan ta birni...tare muke jerawa zuwa islamiya da ita.
  Bayan watanni biyu izuwa uku da yin aurenmu,Banana Ya aiko muzo gida nida fillo.
Ya jidadi sosai da ganinmu sabida farincikinsa a bayayyane yake..
Naje zan rungumeshi,ya tsaida ni yana fadin ai yanzu  kin wuce nan...na ba'ta fuska tare da komawa gefe, shi kuwa fillo tunda muka isa gidan kansa a duke
Bayan gama gaisuwar da  babana ya umurce mu da mushiga cikin  gida don gaisawa dasu hajiya.
Read More »

Sunday, 24 September 2017

SOYAYYARMU👫


             By Ganarious.
17
Ji nayi an zare littafin dake hannuna,haka yasa na da'go.mamatace tsaye a kaina muna ha'da ido na sauko kasa inayimata sannu da dawo wa.ta sami daya daga cikin kujeru ts zauna tana kallona.
  Ta dauki tsawon lokaci sa'anan ta tambaye ni tunanin me nake haka da take sallama ban amsa ba ko bansa da shigowarta ba ko!
    Shiru nayi ban amsa don bani da abin fadi... tayi ajiyar zuciya sa'anan ta cigaba fadin"ni da Babanki mun zauna don neman mafita akan matsalarki"
Nan na kalleta,watau kallon rashin fahimtar me take nufi da hakan.
Read More »

SOYAYYAR MU👫..

            By Ganarious.
16
Da yatsa nayi mata nunin   dakin fillo,sai saukan mari naji a kunci na.na dago kai muka hada ido da ita sai kuma ta hau duka tana shuri na..
Ranar ce ta farko da mamata ta kai hannunta jikina da sunar duka!.
Kaina na tsakanin gwiwowina ina kukan zuci,jin an daina bugun ne yasa na da'go.
fillo na gani duke a gaba na Babana kuwa yana rike da mamata ya janta zuwa cikin gida.na juyo muka hada ido da fillo,murmushi nayi masa   sai dai shi bai mayar min ba.sai ya tsiramin ido.muna cikin haka babana ya dawo cikin rudani da'gani yana fadin ina ke maki ciwo...sai a lokacin na sami damar yin kuka duk da daurewan dana so yi.
Read More »

SOYAYYARMU👫

         By Ganarious.
15
Haka mukayi ta rayuwa kullum safe sai na kaiea fillo abinci kafin na tafi makaranta,idan kuma na dawo sai na shiga gun sa munyi hira kafin na shiga ciki.idan kuma na shiga ciki Allah Allah nakeyi na idar da sallah na dibi abinci na a plate natafi dakin sa na zauna ina ci muna hira.duk da kashaidin da mahaifiyata tayimin.
Weekends kuma mu tafi yawon ganin gari da sayayya,a maimakon librabrin da muke zuwa da safiya.
Read More »

SOYAYYARMU👫

         By Ganarious
14
Alhamdulillah,maa Shaa Allah...Haj.Fateema A.Bayero(mrs Bash gwandu) ta sauka lafiya.mun sami babby girl me suna umaimah,Allah shirayamana ita kan addinin musulunci.ameen.
Jama'a makarantan soyayyarmu ina muku barka da sallah.Allah shi maimaita mana.
ina me baku hankuri akan rashin typing akan lokaci.kuyi hankuri.
Gaisuwa ta mussamman ga haj.Sa'adat Ahmad(a.k.a sa'adat mubi 4real,basu labari).
Read More »

SOYAYYAR MU👫.


          By Ganarious.
13
A sanyaye nake komai tun bayan tafiyarsu Malam Lamido.
Da zarar na zauna sai na fara tunanin dan fillo.wata sa'in na shiga dakin da suka sauka nayi zaune ina tunano fuskar sa da murmushinsa ni karan kaina na kasa gane me ke damuna.
Mahaifiyata kuwa har tambayata take wai ko lafiya.! Ko so kike ki koma rugga.
Yan gidanmu sun samin suna wai "yar rugga"
Read More »

SOYAYYAR MU👫

By Ganarious.
12
Falon Babana musake komawa tare dasu Malam Lamido,Nan nasake yimasu bayanin malam Lamido da fillo.
Babana da abokansa sunyi mashi godiya sosai.sai alokacin babana ke bayanin ai daman Gobe za'a yi shari'a ta karshe a kotu,amman tunda Allah yasa gaskiya ta bayyana,toh wadannan yaran da iyayensu kawai za a kamomin.
Read More »

SOYAYYAR MU

         By Ganarious.
11
A rugga kuwa bani da wata damuwa da ta wuce nagan iyaye na,Idan da sabo toh na saba dasu.na koya masu ayyuka dayawa,na kuma koyi wasu ababen a gunsu.haka nayi rayuwa a cikinsu har Allah ya kawo wani da zai je birni.
  Ana gobe zamu tafi,mukayita hiran bankwana dasu na kuma yi masu alkawarin sake dawowa.a hiranmu nake cewa Bintu idan ta haihu zan raini dan,na kuma kai shi birni.taji dadi sosai don a rayuwarta ba abinda ke mata dadi kamar ayi zancen birni,ko a cemata yar birni.
Read More »
SOYAYYAR MU👫
    By Ganarious.
8⃣
Bayan na bude takardan sai na gan rubutu kamar haka.'hahah..idan har kin tashi kin gan wannan takardar toh ki godewa Allah..ba mu sonki,bamu kuma kaunar ganinki.shiyasa mukayi maki hakan.sai mun hadu a can.
  Sai a wannan lokacin na tuna abinda su hafsat sukayi min.kuka na shiga yi sosai ina fadin menayi suka tsaneni haka!
Fillo kuwa ba abinda ya kai sai kallo na...sai da nayi me isata sa'anan nayi shiru domin kuwa kaina ya fara saramin,kamar jira yake nayi shiru sai yace min na tashi mu tafi tare da yimin addu'a da fulfude wai Allah reene,Allah seyne!.
   Tafiya mukayi sosai sa'anan muka isa ruggan su.yan uwansa sunyi mamakin ganin fillo tare da dani,sai na zama masu abin kallo.
Da fillatanci yayiwa iyayenshi bayani.
Na dade tsaye don kuwa dan fillo da yan uwanshi gabaki daya suka shige wani daki sai wasu kananan yara da suka firfitoo suna kallona kamar sun gan wata halitta.har na fara jin haushin biyoshi danayi.ina a tsayen,sai gasu sun fito amman kuma basu cemin komai ba,ko ga guri zauna ma ban samu ba...shima din fillo haka yazo ya wuce ni bai ce komai ba...hankalina duk yatashi ina tunanin me mutanen nan ke shirin yi dani.
 Guri na samu na dan tsuguna,ba abinda nake tunani sai sallolin da Ke kaina..ina cikin wannan tunani na hangi wata budurwa zatayi sa'ata a girman jiki,amman a shekaru mu ba tsara bane.itama din dai kallona takeyi har tana tuntube,da hannu nayi mata alama da tazo."don Allah ina zanyi fitsari?"nace da ita.
Bata amsa ba sai kallona takeyi na sake yi mata magana nan ma bata amsa ba ta juya ta wuce abinta,..gashi fitsari ya matseni sosai.
Nabkoma na tsuguna ina tunanin wannan wata rin rayuwa ce...sai kawai kuka ya zo min...amman kuma mutanen kamar dabbobi sai kallona sukai daga ne'sa.
   Kuka fa nake sosai,sai ga dan filli ya dawo shi da wani mutum.suna isowa na mike sauri nace fitsari nake ji wannan mutumin yace a kaini bayan ruggansu nayi fitsari   sa'anan na dawo.
Wannan mutumin dogone me kyan gaske gashi fari tas dashi,sai kuma Allah ya bashi abinda mata ke kira dimple...ya tambayeni duk wani abu da yake son sani game da haduwata da dan fillo kuma da dalilin da yasa aka bar ni a daji..na kuwa fada mashi komai da komai daga kan abinda su hafsat sukayi min har yanda muka hadu da dan fillo.na kuma rokeshi da ya taimaka min na koma gun iyayen A kaduna.
'toh naji zamu taimaka maki mu maida ki gun iyayenki sai dai ba wanda zai je birni cikin yan ruggan nan.amma idan ansamu za'a mai dake gida.
Shiru nayi ina me rokon Allah a zuciyata da yakawo min mafita.

Wani daki suka kaini wai nan zan dinga kwana,da kamar nace masu bazan iya kwana anan ba amma ba yanda zanyi dole na na shiga ciki a takure na zauna.
A sannu sannu na fara sabawa dasu sai fai wasun su ba su jin hausa sai fulfude...Na rame sosai don kuwa tunda na shiga ruggan bana iyacin abincisu duk da kokarin danakeyi na turtusa kai na amman abin ya ki don kuwa idan na tursa kaina to amai ne zai biyo baya,hakan asa iyayen fillo cewa a dinga ta'cemin nono shanaye.
  Nafi shakuwa da dan fillo,idan za shi kiwo sai na bishi idan har ba zai dade bane.
Read More »
SOYAYYAR MU👫
      By Ganarious.
9⃣
Wataran muna gun kiwo ni da shi sai nace ni dai har yau bansan sunarka ba..ya kalle ni cikin murmushi sa'anan yace sunana Mustafa amma bakiji ana cemin buba ba?.
Na girgiza kai tare da fadin a'a ni ban ji ba,asalima ban taba ji ko lura da wani ya kira ka ba.
"toh kishee min buba"
Toh malam Buba,nace mashi ina murmushi...
Can kuma nace amma mamarku da yaranta sunyi daban kamar ita tana da surki da buzaye ko?
Eh...buzuwace.
Cikin mamaki nace....kai,!tabdi jam amman ya'ya akayi hakan ta faru?
  Ho...ni ma din ban sani ba.
Na dade ina mamakin yanda akayi bafulace ya auri buzuwa.amma kuma combination din yayi kyau sabida yaranta suna da kyau kamar larabawa ,ga gashi har gadon baya,mazan kuma gashin su yayi luf-luf yakwanta masu.
     **    **  **
Akwana a tashi har nayi sati biyu a wannar ruggan,ina cikin na uku amman ba wani labarin batun komawata...a lokacin ne yayan Buba fillo ya dawo daga kiwo ana kiransa Dahiru.shima yayi mamakin ganina nan aka bashi labarina,cikin kankanin lokaci muka fara shiri da shi...ina cika sati hudu akayi auren dahiru da diyar maigari(mai gari Laamido shine wannan mutumin da yayimin alkawarin maidani ranar d na zo ruggan da buba fillo).shine ya'yansu baban buba(dan fillo).diyar shi bintu da dahiru cousins ne kenan.
Amarya bintu da bata wuce shekara takwas ba sai mamakin abun nakai,ita ma mun shaku,duk da na girmeta nesa ba kusa ba idan muna hira sai nace mata wataran zan kaita birni,sai tayi ta murna.haka dai nayita zama da wayannan mutanen a sannu a hankali.
    ***   ***   ***
Su hafsat ne sukayita tafawa suna murna yau burinsu ya cika."kai ku zo mu tafi fa kar a tafi a barmu"fadin hafsat bayan sun gan cewan bana cikin hayyacina.da gudu suka bi bayan sauran daliban cikin sa'a kuwa suka iske ana shiga mota ne..
Sun isa masauki(hotel) ana fitowa don shiga cikin dakuna,shine Awwal ke tambayar su ina Aisha?
Sun dan dauki lokaci sanan Rabi'a tace ai ba motar mu take ba.ka dudduba motoccin mana,kana wani tanbayarmu.ta karashe maganar ne kamar Me fada.
Bai musa ba ya koma inda aka ajiye motor A daman kuma motan yake amma kowa ya sauko bai ganni ba.sai kuma yakoma gunsu yace aisha fa bata ciki.
Toh miye na mu a ciki.?inji Hafsat
Ban gane miye naku a ciki ba.tare na barku a dajin kunga ai dole ne na tambayeke kenan.
Tsaki sukayi gaba dayansu suka juya zasu tafi..sai ya sha gabansu..Awwal yaro ne da baya daukan renin hankali ko gun yan'uwansa maza.
"wa kukeyiwa tsaki? Ya tambayesu tare da nuna masu dan yatsan.
 Gefenshi suka sake bi batare da sunce mashi komai ba..
Read More »
Designed by Jide Ogunsanya.