Pages

Thursday 21 December 2017

SOYAYYAR MU👫.
     By Ganarious.
2⃣1⃣
Ki yanke min ko wata irin hukunci amma karki yi fushi dani....ni kadai nasan yanda naji a raina ganin ki haka.Don Allah ina rokonki kar ki karayin irin wannan fushin,nasan nayi laifi kuma a shirye nake da na dauki hukuncin da za'ayimin amma ba da wannan ba.
 Ba san sa'anda hawaye ya zubomin ba,ina me kallonsa nace "kafada min dalilinka na rashin zuwa duba mu..kuma yaushe kaji na haihu?
  Ya sa hannunsa ya sharemin hawayen,sannan yace Bani da lafiya ne!.
Nan da nan na rude,na kuma shiga tausaya masa ..ina fadin "ya jikin?
Na ji sauki hamdala...
Nan ta'ke mu manta komai muka shiga hira irin ta masoya masu shaukin juna...sai da yaro ya fara kuka sannan fa muka tuna yana gun,fillo ya taka zuwa gun gadon ya dauko shi.
  Ya dawo gefena yana me kallon jaririn,nikuma ina shafa kansa(shi jaririn).
Yayi murmushi yace tabdijam...wannan d'an kam ba'ki ne,muka tuntsire da dariya sabida yanayin da yayi furucin.
 Ai nice sak...wannan ba'kin nawa ne....sabida haka sai kawai ka sanya masa sunnan baba na.
 Da sauri ya kalle ni,yace kin so kanki da yawa! Duk da nima zan so haka  .
Wannan kam Baban mahaifiyata ne domin kuwa shima din ba'kin buzu ne ,kamar wannan jaririn.
Ahmadu shine sunan da aka sanyawa yaron,sai nake kiransa da MUJAHEED..wannan  jaririn shima akwai shi da shiga rai.
  Wata biyu nayi na koma gida.
Abu kamar wasa tunda muka koma gida fillo bai leko mu ba,har zamu shiga sati na uku..sai nake tunanin wata kila bashi da lafiya ne kuma...
Sabida tunanin haka na shiyar ranar asabar,tare da yin girke-girke don kaimasa.
Hisham da ilham sashen binta na kaisu sannan na nufi zaria.
Gidan da nayi zama alokacin da nake karatu nan yake zaune shima,don haka ban wani yi wahalan neman gida ba.
Na tarar da gidan a rufe,da alama baya nan kenan.
Na dade tsaye ina tunane-tunanen abinyi sai wata zuciyar na rayamin wata kila yana hanyar kadunan....
A zuciya ta nace ko da yana garin ban san lokacin dawowansa ba...ina cikin wannan tunanin mujaheed ya fara motsi,ya tashi daga baccin kenan.
Wai waiga  na gani ko zan sami gun zama,ai ssi nayi ido hudu da fillo cikin mota.
Motan nan tana gun sa'anda na  wuce domin kuwa ta gefen ta na bi amman tunani bai bani da na kalli cikin motan ba balle mutanen cikinsa.
    Wata fara mace ce a gefe,daga alama itace mai motar don zaune take a kujeran direba.
Muna hada ido da naji zuciyata na ras-ras da karfi...
Kallonsa nake shima hakan,sai kuma ya maida kallonsa ga matar suka ci gaba da maganarsu.
  Na da'de ban dauke idona daga gareshi ba,har sai da mujaheed ya fara kuka...
 na rasa mafita gashi ba gun zama,gashi fillo bai zo ya bude mana kofa ba...duk sai na rude cikin kankanin lokaci.
Kuka yake sosai..niko sai girgiza shi nakeyi ba tare da na sa'ko shi daga baya na ba...muna cikin haka fillo ya fito daga motan,ita kuma ta ja motan ta wuce.
Ya karaso inda nake tsaye ya amshi mujaheed ya bude kofa yashiga ciki ya kwantar dashi.
Ya dawo ya kwashi kaya ya shigar.ya sake dawowa har zuwa wannan lokacin tsaye nake bani ko motsawa.
Ya matso gaba na,muna dab da juna domin ina jiyo numfashinsa.
  A hankali yace 'mu shiga ciki ko!.
Nan ma ban motsa ba,gashi sai ihu mujaheed keyi.
 Ya rikemin hannu ya jani zuwa ciki.
da kansa ya zaunar da ni,ya nufi gun a.c ya kunna sannan ya dawo ya dauki mujaheed yana lallashi,duk da haka yaro ya kiyin shiru.
Ya dawo gefena yana fadin don Allah ki saurari wannan yaron..
Ko kallonsa banyi ba balle na amsa shi. Shi ke kidansa,shi ke kuma rawansa...
...sai da maganar sa ta isheni na na mike a hasale,na fizgi mujaheed ina kokarin goya shi.
Shima ya mike cikin mamaki,yana kokarin rike ni,na fizge hannuna.ya sake kamo hannuna  yace don Allah kiyi hankuri kiyi min magana...
Kuka irin ta ban tausayin nan ce ta ci karfi na ...sai kawai naji ina tausawa kaina.
Da dabaransa ya samu ya zaunar dani.mujaheed kam yayi kuka har ya hakura.
ya sani ga'ba ya kallon ina kuka har sai da nayi me  isa ta.
Sai da kukan ya lafa sannan yace "haba Aisha"....nasan dai kishi ne,amman a duniya kinsan bani da kamar ki kuma ba zani sami kamar ki ba.

No comments:

Post a Comment

Designed by Jide Ogunsanya.