Pages

Thursday 30 August 2018

Natural toner for oily skin

Cucumber and Lemon Juice Toner for Oily Skin DIY 1 How to: 01. Take a fresh aloe vera leaf. 02. Using a sharp knife, cut the leaf vertically from the middle. 03. Now make them superficial slits on the gel portion of the leaf to extract the gel. 04. Collect the fresh gel in a container. 05. Take two teaspoons of this gel in a separate container. 06. Add 4 tablespoons of cucumber juice to this aloe vera gel. 07. Add 1 tablespoon of lemon juice. Mix well. 08. Pour this mixture into a spray bottle. 06. Apply this toner on your face using a cotton ball. 07. Use this toner two times a day. 08. You need not wash your skin after its application. DIY 2 How to: 01. Boil 3 tablespoons of flaxseeds in ½ cup of water. 02. Boil the water until it changes in color. 03. Strain the water immediately. 04. Store the seeds in a separate container so that they can be used for the next time. 05. Now let the water cool down completely. 06. As the water begins to cool down, it will turn into a gel. 07. Take 3 tablespoons of this freshly prepared flaxseed gel. 08. Add 4 tablespoons of cucumber juice to this flaxseed gel. 09. Add 1 tablespoon of lemon juice. Mix well. 10. Pour this mixture into a spray bottle. 11. Apply this toner on your face using a cotton ball. 12. Use this toner two times a day. 13. You need not wash your skin after its application. DIY 3 How to: 01. Take 3 teaspoons of apple cider vinegar. 02. Add 5 tablespoons of cucumber juice to this. 03. Add 1 tablespoon of lemon juice. 04. Add 1/4th cup of rose water to this mixture. 05. Mix well. 06. Pour this mixture into a spray bottle. 07. Apply this toner on your face using a cotton ball. 08. Use this toner two times a day. 09. You need not wash your skin after its application. How this helps: Cucumber juice – cucumber juice is very beneficial for the skin. This is because cucumber has soothing properties. It helps in the soothing irritated skin. This is very helpful for oily skin since irritated skin produces more oil. Cucumber juice also helps in reducing inflammation. Hence it helps in reducing the size of enlarged pores as well and fights acne. Cucumber juice can also help in fading away pigmentation slowly. Lemon juice – lemon juice contains small amounts of glycolic acid which help in exfoliating the skin. Lemon juice is drying in nature and hence it helps to mattify the skin and make it less shiny. It reduces the oil production and reduces the dullness due to oil deposition on the face. Lemon juice is also rich in antioxidants and vitamin C which enhance the appearance of the skin. the glycolic acid present in the juice helps in exfoliating the skin and fading away scars. Rose water – rose water helps in balancing the pH level of the skin and soothes inflammation. Aloe vera gel – aloe vera gel hydrates the skin. Since it is water based, it does not clog the pores and does not make the skin greasy or heavy. Flaxseed gel – flaxseed gel is a rich source of antioxidants and also contains omega 3 fatty acids which help in making the skin glow.
Read More »

Wednesday 29 August 2018

REDUCE THE PIMPLES WITH BAKING SODA

How to Use Baking Soda to Reduce Pimples Baking Soda is a super-efficient item in the kitchen. From making delicious bhajis to sweet cakes, they are used in many ways. A fluffy ingredient that is used in making everything we like, it can become more preferred when you know this. They can treat pimples as well. Read on to find out how. Remedy #1 with Lemon Juice 01. Take a bowl and add 2 tablespoons of baking soda into it. 02. Add 2 tablespoons of water as well. 03. Cut a lemon and squeeze the fresh juice into the bowl. 04. Mix them all well to form a paste. 05. Apply this paste on your face using clean fingers, giving special attention to the affected areas. 06. Leave it on for about 15 minutes. 07. Wash it off later with warm water and splash cold water to close the pores. 08. Do this twice a week for quick and best results. Remedy #2 with Honey 01. Take a bowl and add 2 tablespoons of baking soda into it. 02. Add 2 tablespoons of honey in the bowl. 03. Mix both ingredients well together to form a smooth paste. 04. Apply this paste on your face using clean fingers, giving special attention to the affected areas. 05. Leave it on for about 25 minutes. 06. Wash it off later with warm water and splash cold water to close the pores. 07. Do this twice a week for quick and best results. Remedy #3 with Coconut Oil 01. Take a bowl and add 2 tablespoons of baking soda into it. 02. Add 2 tablespoons of fresh, raw and virgin coconut oil. Melt it before use to avoid lumps. 03. Blend the ingredients well and make a smooth paste. 04. Apply this paste on your face using clean fingers, giving special attention to the affected areas. 05. Leave it on for 10-15 minutes. 06. Wash it off later with warm water and splash cold water to close the pores. Remedy #4 with Apple Cider Vinegar 01. Take a bowl and add 2 tablespoons of baking soda into it. 02. Add 2 tablespoons of fresh, cold pressed apple cider vinegar into the bowl. 03. Blend the ingredients well and make a smooth paste. 04. Apply this paste on your face using clean fingers, giving special attention to the affected areas. 05. Leave it on for 10-15 minutes. 06. Wash it off later with warm water and splash cold water to close the pores. Remedy #5 with Toothpaste 01. Take a bowl and add 2 tablespoons of baking soda into it. 02. Add a few drops of natural, organic toothpaste into the bowl. 03. Add few drops of rose water to loosen up the paste. 04. Blend the ingredients well and make a smooth paste. 05. Apply this paste on your face using clean fingers, giving special attention to the affected areas. 06. Leave it on for 5-10 minutes. 07. Wash it off later with warm water and splash cold water to close the pores. Remedy #6 with Olive Oil 01. Take a bowl and add 2 tablespoons of baking soda into it. 02. Add few drops of warm olive oil into the bowl. 03. To make the warm olive oil, heat it at first, and later cool it down to a useable temperature. 04. Blend the ingredients well and make a smooth paste. 05. Apply this paste on your face using clean fingers, giving special attention to the affected areas. 06. Leave it on for 15 minutes. 07. Wash it off later with warm water and splash cold water to close the pores.
Read More »

Monday 27 August 2018

Homemade dark spot remover

~GET RID OF YOUR DARK SPOT(effectively)~ 1...Lemon juice, Vinegar, Baking soda 1/2teaspoon In a clean bowl,mix a half teaspoon of baking soda with vinegar and little amount of lemon juice.(making a paste) =>Apply it to the affected area. 2...Turmeric powder 1/2 teaspoon, Clove powder, Sandalwood. Fetch half teaspoon of each above mentioned,mix with little amount lemon juice and honey,making a paste. =>Apply to the affected area. This paste will help u get rid of your acne overnight
Read More »

AMAZING SCRUB FOR YOUR HANDS

*SCRUB FOR THE HANDS* >sugar 3teaspoon, >coconut oil 3teaspoon, >lemon juice half. In a clean bowl,add sugar,lemon juice, and coconut oil. Mix all the ingredients,and your amazing hand scrub is now ready for use. Apply this to your hands, and gently exfoliate your skin for 10minutes. After scrubbing, wash your hands with warm water then, pat dry and moisturise them well. Repeat continuously before going to bed.
Read More »

HAIR BREAKAGE SOLUTION

SOLUTION TO YOUR HAIR BREAKAGE, AND DAMAGED EDGES.!💇🏽‍♀

      Things needed:
*Avocado pear5 (overriped or riped)
*Egg yolks 3
     
            Method.
Peel the Avocado and cut (into pieces) into a blender, Add the egg yolks and blend, making sure the mixture is smooth.
=>Apply, and massage to the  scalp properly.
=>cover with shower cap or cellophane(nylon).
=>leave to stay for an hour and then wash off with warm water and mild shampoo.

Visit👉🏼 ganarious.blogspot.com/ to read and learn more.!
Read More »

Sauki a gidan ki

*~SAUKI A GIDAN KI~*
Burin mu mata,bai wuci mu gan cewan mun haskaka ✨💥ba. Musamman idan aka zo kan fata, shikenan anzo guri.
  Akwai mafi yawan matan da basu ki su kashe (kudi) masu yawa ba don ganin fatan su na haskakawa.
Wasu mata, hasken fata suke so, a yayinda wasu suke so da kuma burin ganin  fatan su sumul-sumul da laushi.
      Ko kin san da cewan akwai ababe da kike amfani da su a gida ko kitchen, ko kike sha ko ci da za su cika maki burin ki?....a maimako kashe kudi, saye sayen mayuka wanda idan mukayi la'a ko nace idan ba'a yi sa'a ba sai su bata maki fata.
Wadannan ababen da zani lissafa maki basu da side effects, ba kamar mayukan zamani ba da wasun su kam kawo cutan skin cancer sabida karfin chemical da ke tattare da su.
Idan har zaki yi hakuri,da juriyar yin amfani da su,fatarki zata haskaka💥.

Shin ko kin lura,ko kin taba cin karo da =lemon juice=, =citric acid=, a cikin ingredients din mayuka ko sabulan da kike saye?
Toh ki sani lemu🍊🍋 , yana  da matukan anfani ga fata.
Yana kashe cututtukan fata,tare da kuma haskaka fata sabida wata sinadirin da ke cikin ta da ake kira da *citric acid*🍊.
don haka kina iya yankan lemu ko lemun tsami ki matse ruwan sa kina shafawa a fatar ki.

🍅 ga tumatur.!
Jure ki dunga shafawa fatarki ruwan tumatur, ko ki nike shi ki shafa, har na tsawon lokaci.

Ina kika baro dankali🥔.!,
Ko kina da labarin cucumber🥒 yana tare da sinadari me haskaka fata?
..zakiyi mamaki idan nace maki caras🥕 da ayaba🍌, ababe ne masu karfi gun haskaka fata?

Shi ko kin san yanda zakiyi da sukari(sugar) don samun laushi da kuma hasken fata?
Akwai ababe da dama da nayi bincike akan su suke kuma gyaran da kuma taimakawa gun gyaran fata.
Ina kuma rubutu a kansu, idan kina son sani ko kowo game da su, toh ki biyo ni blog di na👉🏼 ganarious.blogspot.com/
Idan ma kina da tamabaya game da abubuwan da na lissafa, toh kiyi tambayar ki.
Ma'assalam🤝🏻
Read More »

Thursday 16 August 2018

Page 51 of SOYAYYAR MU👫

SOYAYYAR MU👫
      By Ganarious.
Page5⃣1⃣

          **      **      **
 Kwance ya ke, a yayinda idonsa na rufe kamar me bacci,sai dai da ka gan yanayin kwanciyarsa,zata san cewan ba ba bacci yake yi ba.
Bayan abokansa sun lallashe shi,su ka koma hostel.da isar su suka hada masa ruwa me dumi-dumi domin yayi wanka.bayan ya fito wankan suka cire ankachif da suka daura masa akai, tare da laulaya masa bandeji akai....idan ka ci abinci yanzun sai mu tafi clinic ko?..fadin daya daga cikin abokansa yusuf.
Ba tare da ya amsa Ba,ya haye saman gadonsa tare da rintsa idon sa.
Ababen da suka faru a tsakaninsa da wannan yarinyar da alokacin ma be san sunarta ba su ka dunga dawo masa,kamar yanzun suka faru. "wannan wace irin  shaidaniya ce, tun tasowa ta sa'insa bai ta'ba shiga tsakani na da wani ko wata ba, ballanta wai muyi fa'da,amman yarinyar nan sai da ta kaini karshe..musamman ma abinda tayi min ayau,wanda shike xani iya cewa tozarci,kai.....kai....kai....dole nayi wani abu akanta,sai na koya mata darasi.." duk a zuciya yake wannan  sumbatun...ya cigaba da shawara da zuciyarsa,nan yusuf ya katse masa zancen zucin da fadin "tashi ka ci abinci mu tafi clinic"
Sai da sukayi da gaske sa'anan ya tashi ya ci abinci,amman fa bayan ya gama ci yace shi fa wallahi ba zai tafi clinic ba, ganin yayi rantsuwa yasa suka fita harkansa.

   Bangaresu ilham kuwa, babu yanda Naziha bata yi da ita ba akan tayi wanka,ko kallo basu isheta ba, ballantana ta sauraresu...safa da marwa kawai takeyi tana sumbatu,ganin bata da niyar sauraronsu,suka nemi guri tareda da zaunawa suna bin ta da ido..a yayinda suke mamakin ilham,wace basu san haka ta ke da taurin zuciya ba, sai yau.
Kiran sallah yasa suka rike mata hannu zuwa masallaci, nan dai kam bata mu'sa ba.bayan sun dawo da'ga masallacin Yusra ta shiga rokon ilham, sai da kyar sa'anan ta shiga wankan,abinci kam ta ki ci,iya naci kam sunyi, akan sai ta ci abinci.
    Bayan sallan magriba, sun dawo da'ga masallaci ta kwanta tare da rufe idanunta, hakan yasa su Naziha sun nufi dakunansu.
Bata jima da kwantawa ba, wayarta ta shiga ruri.
A hankali ta bude idanunta tare da kai hannu ta dauki wayar, tana ganin sunar me kiran,tayi tsuki tare da kashe wayar ta mayar ta ajiye.
   Washegari,bayan sun kammala shirinsu,su ka jero zuwa cikin makaranta.
Dalibai maza da mata, sai kallonsu suke,wasun ma harda nunin su da yatsa..."Turawa fa ba isashen hankali ne da su ba" fadin Amarah.
"wai don sabida abinda ya faru jiya?
"eh...shine suke mana wannan kallon"
Uhmmm....kallo kam yanzun zasu fara shi....fadin ilham.
Da haka sukayi firan su,har suka kai gurin rAbuwa, ko wace ta kama hanyarta.

Ilham bata fi minti goma sha bakwai da shiga hall ba, wata lecturer ta shigo ajin tana tambayar waye "Aisha B.Mustapha"?
Ilham ta mike tare da da'gin hannunta..."here i am ma"
Come with me kawai matar ta fada ta juya ta fice daga hall din.
Ilham biye take da wannan matan har izuwa Admin, inda office din manya-manyan lecturers suke.
A hanyar da zai sada su da office din wani babban malami suka hade da abokin fadanta watau Ameer.
Nan zuciyar ilham ta soma tafarfasa...ji take kamar ta shako masa wuya.
  A tare suka shiga fallon office din,inda matar da umurci ilham ta zauna,ta kuma umurci sekatariyar da ke zaune a gun, da ta shiga office ta sanar wa lecturer daliban sun isa, tana kaiwa nan ta yi tafiyar ta.
Daga ilham sai abokin fadan ta suka rage a gurin,  a yayinda sekatariya ta shige office din ogan ta.
Jim kadan ta fito tana dubansu, tare da fadin "ku taso"
Ilham ce ta fara mike wa,A yayinda Ameer yake biye da ita, suka bi bayan matar zuwa cikin office.
They are here sir" sekatariyan ta fada bayan da sun shiga office din Dr.Abdul'Afeez M.D
Dr. Abdul'Afeez M.D, bayarabe ne da'ga kasar Nigeria, Babban lecturer ne kuma Shine displinary leader ta makarantan. ma'ana, shi ne me kula da tarbiya dalibai.
 Bayan sekatariyarsa ta sanar masa isowar su ilham, ya da'ga mata hannu ba tare da ya da'go ya dube ta ba....don haka ta fita daga office din tareda rufe kofa.

Tsaye suke a gaban teburinsa,suna duban sa, a yayinda yake ta rubuce rubucensa ba tare da ya da'go ya dube su ba.
Kamar wasa har su ilham sun cike awa daya tsaye,wannan bawan Allah be  da'go ya dube su ba,sai rubuce rubuce yake abin sa.
Ranta ya soma baci, sai zancen zuci take tana fadin "ai wannan ma wulakanci ne"
Ga kuma kafar ta dake yi mata ciwo.
Sai da suka cike awa daya da rabi, sa'anan mutumin nan ya ajiye bironsa tare da'gowa ya dube su.
Duban su yakeyi dayan bayan daya. "gida daya kuka fito? Shine abinda ya fito bakin sa.
Kai kawai ta girgiza, a yayinda shi Ameer din yace "No sir"
Amman kun hada dangantaka ko?
Nan ma yace "no sir"
Anyway.....nasan kun san ko ni wane ko?
Yes sir suka hada baki.
Naji labarin kunyi physical fight, haka ne?
No sir, suka sake fadi?
Toh yaya abin yake? Ku nake sauraro.
Shiru sukayi,sa'anan daga baya shi Ameer din ya soma bayani.
Bayan ya gama nasa, ya bukaci ilham tayi bayani itama .
Nan ta fada masa abinda ya shiga tsakaninsu,tun farkon haduwarsu.
"shiru yayi na dan lokaci sa'anan ya soma jawabi.
"A gaskiya, bayan da na samu labari, niyata na kori ko su waye,sai dai banyi zaton kune  ba...
Kai kai Abubakar Hisham Dahiru,dalibi neda wannan makaranta ke alfahari da,a ko da yaushe muna son ka zama abun koyi ga sauran dalibai, wannan abin da kayi yana iya bata maka suna.
Ke kuma...ya fada a yayinda yake dubanta yana nuna ta da yatsan sa.
Aisha wa ake kiranki?
Aisha Mustapha sir.
Ok, Aisha Mustapha.  100level ko?
Yes sir ta fada.
Shin kina da labarin yanda makarantar nan ke alfahari da wannan kuwa? Ya maida kallonsa ga Ameer yana dubansa
Kai ta girgiza tareda fadin " No sir"
Toh tun tarihin wannan makarantan ba'a taba samu ko yin dalibi kamar sa ba, sai ke da muke sa ran zaki mamaye gurbinsa....sabida haka makaranta ke alfahari da ku, domin kuwa kun zamar taurari, haka yasa da na gan ku naji cewan bazan iya zarce hukuncin da nayi  niya akan ku...don haka ina baku hakuri da ku yafewa juna, ku kuma rike junanku hannu bibbiyu, duk da kunce ba gida daya kuka fito ba,amman ai kasa daya kuka fito?kai suka daga.
Nan yayi masa nasihohi, daga karshe ya gargade su da kar su sake ya ji wani abu makamacin haka.
Read More »

Wednesday 15 August 2018

Page 50, of SOYAYYAR MU👫

SOYAYYAR MU👫
       By Ganarious
Page50

√...Assalamu alaikum ya yan'uwa.
Makarantan soyayyar mu,ina me roko da neman afuwa akan rashin typing. A gaskiya nima ba na jin dadin,yanda nake releasing pages., ma'ana idan na saki  wannan page, yakan dauki lokaci kafin na sake saki..
Nasani, nasani, na san dacewan hakan be dace ba,please kuyi hakuri,ku kuma yi min uzuri🙏🏼
Da yaddan Allah,zani yi adjusting.
       Na gode.!
√...ku bini a 👉🏼 ganarious.blogspot.com/ domin samun latest.

        **          **          **
Tana cikin kallonsa, ya da'go suka hada ido.
Kau da kai tayi tare da cigabawa da tafiyar ta me daukewa jama'a hankali.
  Matattala da ya dace ta bi, ba tanan ta bi ba,kuma tana sane ta bi daban wanda zai sa'da ta Ameer din.
Tana isa dai-dai gabansa ,ta take masa kafa, ba tare da ta dubi fuskar sa ba.
Ta tsallake shi zuwa gun da aka tanada don zaman yin wa'azin ta zauna.
Tunatarwa me ratsa jiki ilham ta gabatar.
Ita din ce ta rufe taro da addu'a, bayan da ta gama wa'azin,sa'anan dalibai suka soma watsewa.

    Ameerah ta bukaci masu mUkami, ciki har da ilham su tsaya,don wasu shawarwari da zasu yi bayan taron. Don haka Naziha da su Amarah, sun nemi guri suka zauna don jiran yar'uwarsu.
   Ameer ne tare da abokan tafiyarsa,suka fito daga dakin taron, nan ya dakatar dasu yana fadin "kai, ku tsaya"
Tsayawa sukayi, suna dubansa.... Ameer ya sa hannunsa ya rikewa daya daga cikin su hannu..."ku zo mu tafi karkashin bishiyan can"
"wai shin me zamuyi a can din" daya daga cikin abokansa ke neman sani.
Bai amsa ba har sai da suka isa gurin, suka zauna a kujeru da ke karkashin bishiyan
"kar ku damu,ku dan jira na dan lokaci,da abinda nake sonyi ne.

Sun kai kimamin minti goma a gurin. Yayinda shi Ameer din ke tsaye rike da kugunsa yana safa da marwa.

 Yana tsaka da haka ya hangi wasu dalibai mata sun fito daga dakin taron...tabbas sune wadannda yake jira,sabida yanayin da ya nufe su ya tabbbatar da haka.su kuwa, abokan tafiyansa suka bi sa da kallo.

 Tafiya suke suna firan su cikin anashuwa, ba tare da ji alaman takun mutum a bayansu ba...
Ji kawai tayi an rikomata kafada,hadi da janyota da karfi, kafin duk ta kai dubanta ga wanda ya janyo ta,sai kawai ta ji ta wuuf....a kasa, yasa kafa ya kwasheta.
Cikin rudewa su Naziha suka durkusa,domin kamota.shi kuwa ameer din sai neman hanyar kai mata naushi yake.
Abokansa ne suka karaso gurin a guje suna ririkeshi.....'Are crazy? U most be outta of your mind" shine abinda abokansa suke fadi, a yayinda suke kokarin tafiya dashi.
Kokari kawai takeyi, ta gan cewan ta tuge Nikab din da ke laulaye a kanta, a yayinda su Naziha sun taimaka mata  ta mike..
Tana yin nasarar cire Nikab din,ta fizgi hannunta cikin zafin nama, takalmin kafarta ta cire ta bi bayan Ameer da abokansa.
Kafin duk su Naziha su rike ta,ta ruga a guje ta isa garesu, tana kaiwa gurin su suka juyo gabaki dayansu, nan ta kwadawa Ameer din takalminta me tsini a goshinsa.

  Ya salam..! Shine abinda ya fada,tare da dafe gurin da hannunsa.
Su ko abokansa sai innalillah....suke furtawa
Nan suka rike shi,yana janye hannunsa jini ya soma malalowa kamar an bude fanfo.
Kokari suke su zaunar dashi, don yi masa first aid, amman kamar an soka masa tsinke ya zabura, yanufi inda su ilham ke kokarin kwantawa ilham da hankali, ita kuwa tana fisge fisge.
Ganin haka yasa abokansa ririke shi suna ba shi baki, amman inna idonsa ya rufe.....'no,! Ku barni kawai, wallahi sai na kashe ta yau' kawai yake furtawa..
  Guri ya soma cika da masu wucewa,kowa ya zo wucewa yagan diramar da akai, sai ya tsaya.
Ilham kam ido ya rufe,bata ji bata gani, nan ta haukace masu kamar me jinnu akai, sabida sai da ta ture su naziha ga baki dayansu ,ta cire dayan takalminta ta nufe su a guje.
Abokan Ameer na ganin haka, wasun su suka rike ta,amman sai da ta jefa takalmin, cikin rashin sa'a bai takalmin be sami Ameer din ba.
     Da kyar, da kyar da gumi dalibai sukayi nasaran kashe  wannan wutar fa'dan.
Su Naziha sun rike ta zuwa hanyar hostel,ba takalmi ba bu hijabi sai sumbatu takeyi.
Shi kuwa Ameer, yana tare da abokansa suna bashi hakuri,sai yayi fito masu baro baro da cewan shi fa bai hakura ba, sai ya koyawa yarinyar nan darasi a wannan makarantan.
Read More »

Thursday 9 August 2018

KAZA MA CE MATA TA page9

💖💖💖💖
*KAZAMA CE MATA TA*
           💖💖💖💖
Written by *Ganarious*
Page9

√...Makarantan SOYAYYAR MU one love.

√... *Anty ubaida* wannan page din naki ne💝

√...mss-ganarious, a instagram.
√...ganarious98@gmail.com
√...Ganarious book series, group din mu ta facebook.

       **        **        **
  Tsaye yayi na dan lokaci yana dubanta, hade kuma da jin haushin kansa, na rashin yi mata tayi, tun kamin ya fita daga kitchen din.
  "dauko plate ki biyo ni"...shine abinda ya fada tare da daukan fork ya fice.
Dan karamin plate ta dauka,ta bi bayansa.
Tana isa gunsa tayi tsaye, shi ko ya mika mata hannu ba tare da ya dube ta ba.
Ta mika masa plate din, ya raba abincin gida biyu ya zuba mata a plate.
"zauna ki ci anan" ya fada a yayinda take shirin komawa kitchen bayan ya mika mata plate din.
Ta jawo kujera ta zauna ta soma cin abinci,shi ma din abincin yake ci cikin natsuwa.
Itace ta fara mikewa,sa'anan shima ya bi bayanta.
Ya wanke plate din da ya ci abinci da tukunyar,sa'anan ya goge saman inda ya dafa abincin....binsa take da kallo tana fadin  *iya yi  dai,ace duk abinda mutum yayi amfani da,sai ya wanke anan ta ke?tabijam! Ni kam dai.....

A kwana a tashi..... Suwaiba ta cike watanni takwas a gidan engr. Munir.
Sai dai kuma ba abinda ya sauya daga cikin halayenta na kazanta da ko'na kula.

    Kamar yanda engr. Munir ya fada mata da ta dunga yin abincin ta ita kadai, shi yana nasa..haka rayuwa ta ci gaba da tafiya a tsakaninsu.
Aikace aikacen gida kuwa, kamar share share da goge goge shi ta sakar ma wa. Sashenta ne kawai baya gyarawa.

    Zaune suke shi da amininsa Sa'ad.
Sa'ad ya dubi abokin sa yace "da alama kana cikin damuwa,har ka rame fa.!
Siririya tsuki engr. Munir yayi tare da fadin ai dole na yi rama...wallahi bani ko son na wayi gari mu hada ido da ita.
Sanin abinda ke faruwa ya sa sa'ad dafan kafadarsa yace ''why not ka kara aure toh''
Wallahi nayi tunanin haka,matsalan shine bani da ra'ayin mata biyu ko fiye da haka.
Toh yanzun miye mafita?
Kawai sakinta zani yi idan har zan sake aure.
Nop....ba ka yi haka ba.....
Ai dole hakan ce mafita,idan ma banyi hakan ba ina kake tunanin zani saka matar da zan aura? Ko ka manta yanda tsarin gida na yake ne?
...ganin hankalinsa na neman gushewa sabida bacin rai,yasa sa'ad ya shiga kwantar masa da hankali, da haka har sukayi sallama ya nufi gida.

   Daga wajen gidansa yake jin hayaniya,sai mamaki yake 'anya daga gidana ne kuwa?'  don haka ya nufi hanyar sada shi da cikin gidan a hanzarce.
Baje suke,su da ya'yan su, a yayinda wasu kwance saman kujerun wasu zazzaune saman kafet,ya'yan nasu ma wasu tsatsaye sukayi saman kujerun suna tsalle, suna guje guje.
Da sallamar sa ya shigo..nan wasun su suka shiga gyara zama,ana rufe jiki.
"sannunku dai""...engr. munir ya fada a yayinda yake kara kallon yanda suka maida masa falo.
Nan suka wage baki gaba dayansu, suna amsa masa Gaisuwan.
Bayan yan gaishe gaishen, ya nufi sashen sa.
Zama yayi saman gadonsa tare da da'fe goshinsa. Ya kai kimamin minti goma sha shidda a zaune, sa'anan ya mike ya shiga bayinsa.
Jim kadan ya fito ya sanya kayansa marar nauyi, sa'anan ya nufi kitchen.
Ganin yanda suwaiba ta bar masa kitchen kaca-kaca, alhalin ya tsabtace shi kafin ya tafi gurin aiki.
Ransa ya baci sosai, ji yake kamar ya tafi falon ya riko mata kune yana ja,har sai sun iso kitchen din.
Tsuki yayi,yashiga gyaran kitchen din...bayan ya maida komai inda ya dace,sai ya daura ruwa dai-dai wanda zai dafa masa kus-kus dai dai cikin sa.
Nan yayi tsaye yana me jiran kus-kus din har sai da ta dahu.
Yana cikin zubawa a plate suwaiba ta shigo.
"sannu da aiki."  ta fada.
Kallo ma ,bata ishe shi ba, ballantana ya amsa mata gaisuwan.
"daman kai suke ta jira fa tun  da'zun"
Nan ya da'go yanai mata kallon kasa-kasa 'su wa kenan?
Yan'uwana mana.!
Ni suke jira?
Eh....sun zo neman taimako ne.suna cikin mawuyacin hali na yunwa ga shi azumi ya zo, shinnasa suka garzayo nan...

Minana.!.....wata murya suka jiyo
A lokaci daya engr. Munir har suwaiban suka juya bakin kofa.
Inno ce tsaye..fuskan nan a murtuke,ko da me karatu zai dube ta a lokacin sai hanjin cikinsa ya ka'da
Nan ta karaso cikin kitchen din, inda engr. Munir da matarsa suwaiba suke tsaye.
Sannu da zuwa inno...fadin engr.
Ba tare da ta amsa masa ba, ta dubi suwaiba. "mi kunne na ke ji? Ya taimaka wa yan uwanki? Ci da sha,da dawainiyarsu kike son daura masa? Toh ba zai yiyu ba. Kuma ki saurara ki ji'yah.! Ke ce dai kinka zama tilas ya ciyar,don haka kar ki fara ki da'ura masa wani nauyi...inno na kaiwa nan ta harari suwaiba, tare da nunin kofa da hannunta "je ki ma'zah ki watse su,su koma inda sunka hito"
Cikn bacin rai suwaiba ta raba gefen inno, ta turo baki ba tare da tayi magana ba.
Sha sha sha kawai ta fada a  yayinda take duban engr. Munir, nan ta shiga yarfa masa nasa masifan " kai kuma.! Kar ka sake ka yarda su maida ka wawa.,kana ji ko?
Kai ya da'ga mata.!
Da gunguni suwaiba ta shiga falon,idanun ta sunyi jajir.
"lafiya dai"....sun fada.
Ku tashi ku tafi, umurni ce daga uwar miji na.
Toh..!
Kar ku damu,inn'shaa'Allah zan biyo ku.
Nan suka mike ko waccensu ta shiga hada tarkacen ta.
Inno ce ta shigon falon ta samu daya daga cikin kujerun ta zauna tana me duban su kasa-kasa, ba tare da ta tamka masu ba, su din ma haka.
Hakanan kuma da zasu tafi, basuyi mata sallama ba,ce cewa suwaiba kawai sukayi" toh muntafi" nan tayi masu rakiya .
Rai bace ta shigo falon, bayan da tayi masu rakiya,kai tsaye hanyar dakin ta ta nufa.
Keh....zo nan.!
Da kamar ba za ta je kiran innon ba, sai kuma ta nufi inda take zaune, a dai dai lokacin engr. Munir ya fito daga inda yake la'be yana kallon duk abinda ke faruwa.
Read More »

Friday 3 August 2018

Taimakon kai

DA TAIMAKON KAI NA





  Da karfi ta budo kofar,sai bayan da ta shiga cikin dakin,sa'anan tayi sallama.
   Asiya,wace ke a kwance, ta da'go tana yatsine-yatsinen fuska "me ye haka kuma?"  ta fada.
"a gaskiya ya'Asiya dabi'unki suna damuna,ma'ana dabi'an ki ta sanya hotunan tsiraici a shafinki ta sada zumunta ta instagram...
Ke! Dakata!
Shiru zahra tayi tana dubanta.
''kin sa min ido,kin takurawa rayuwa ta,kin hana ni sakat. haba! Ko iyayena da nake karkashin su, sun shafa min lafiya.....ballantana ke.
Eh!...idan dai gaskiyar da nake fada maki ne sa ido, na ji na dauka don bazan fasa ba. Gaskiya- gaskiya ce ya'Asiya.ki duba fa ki ga,kin zama abin kwatance da magana a gari,kin zubar mana da mutuncinmu. Ke ce   sanya hotunan banza a instagram, ke ce me cinkoson samari har mazan aure,ke ce yawon bin kawayen banza gogaggu ko nace yan duniya...haba! Ya'Asiya kina ganin Na'imah yanzun ta soma kwaikwayon halayen ki,koma dai nace kin soma sanya ta a hanya
Toh! Sai me? Na sha fada maki da ki daina fadamin yanda zan tafiyar da rayuwata....
Nan fa zahra da yar'uwarta su ka soma mussanyar magana.suna tsaka da haka mahaifiyar su ta shigo.
''me ke faruwa" halan dai zahra ce?
Wa ne tou,idan ba ita ba! Fadin Asiya.
  Ba tare da mahaifiyarsu ta nemi sanin abinda ya hada su ba, ta rufe zahra da masifa, har ta kai ga fadin "anya kuwa ba'a sauya min ke a asibiti ba kuwa ? "domin  kuwa ni bani da sa ido da hassada,haka shima mahaifinku..Amman kin gan ki !  Ta fadi hakan a yayinda take nunin zahra da yatsa "banda bakin ciki da hassada da kike yiwa yar'uwar ki,ba abinda ke cikin kirjin nan"
Idan da sabo,zahra kam ta saba da irin haka.sai dai takan yi bakin ciki a duk lokacin da mahaifiyarta ta furta haka.
"haba inna !... Ki sani fa mu amana ne gare ki. ki daina biyewa son zuciya da rudun kyal-kyalin duniya,ki'mar mu da mutuncin mu sun fi....
   "rufe min baki"....marar kunya,ni za kiyi wa wa'azi,watau duk abinda muke yi ba dai dai bane ko ?
....toh, wabillahillazhi'!  Idan kika sake yi min magana makamacin haka, duk abinda ya biyo baya,ke kika saya.
 Allah ya huci zuciyarki inna,don Allah ki gafarta min.
  A daren ranar zahra bata runtsa ba.tunanin rayuwar da yar uwarta ta daukan wa kanta takeyi,ga kuma mahaifiyarsu da ta mara mata baya.
Ganin sai juyi takeyi a shimfida,ya sa ta mike. Ta fito tsakan gida tayi alwala sa'anan ta koma cikin dakinsu.sallah ta gabatar tare da rokon Allah da ya shiryi yan uwanta, ya kuma ganar da mahaifiyarsu.
  Bayan da tagama addu'o'in ta, wayar ta ta jawo ta shiga yanar gizo tana binciken damammaki da gwamnati ke  badawa. Cikin sa'a kuwa tayi karo da wata dama,inda gwamnati ke neman mata wadanda suke da baiwa, suka kuma iya aikin hannu.
Ganin gwamnati zata dauki nauyin su zuwa kasar waje, domin karo ilimi da fasaha akan abinda duk kayi, domin al'umma su amfana.
Ba ta bata lokaci ba, ta cike fom din akan sharada da dokokin su.
   Washe gari da sanyi safiya ta nufi dakin mahaifinta bayan da ta idar da sallan asubahi. "inakwana abba !
Lafiya lau,da fatan kin wayi gari lafiya ? Fuskar sa dauke da murmushi yake amsa mata gaisuwar.
"abba inason zani je abuja yau"
"yo me kuma zaki je yi a abujan ?
Kitso zani je yi wa wata amarya da kawayenta.
Tau Allah shi tsare.
Amin ta fada,tare da mikewa ta nufi dakin mahaifiyarta.
Bayan sun gama gaisuwa ta ce "inna ina son zan je abuja yau"
Tau ! A dawo lafiya.
Zahra tayi shiru na dan lokaci tana duban innarta...sa'anan tace "baki tambaye ni abinda zai kai ni ba"
Eh ! Sabida ni banida sa ido.
Ganin yanda innarta ta maida mata da maganar,ya sa bata ja maganar da tsawo ba. ta mike ta fice zuwa dakinsu, inda ta tarar da sauran yan uwan na ta sharban bacci abinsu.ko sallah basuyi ba. tayi siririn tsuki tare da cire hijabin jikinta..sa'anan ta fita cikin gida ta soma aikace-aikace.
Sai da ta tabbatar ko ina yayi tsaf-tsaf sa'anan ta shiga wanka bayan tayi masu abin kari.
Bayan ta kammala shirinta,ta shiga sukayi sallama da mahaifinta.

         TUSHEN LABARI
Malam Hassan mutumin suleja ne da ke jihar neja. Bagware ne kuma manomi. Ya auri Hindu wace yar asalin kasar nijar ce.
Hindu da iyayenta sunyo hijira ne da'ga kasar su,a inda mahaifinta ya samu aikin gadi (watau tsaro)wata kamfani me zaman kanta.
 Malam Hassan mutun ne me zafin nema,ga hakuri da taimako. Gashi da tausayi,domin kuwa tasauyi ce ta kai shi ga auran Hindu wace suke fama da matsanancin yunwa.
Allah ya albarkace su da ya'ya hudu. Uku mata,da da' namiji daya.
Watarana !  Malam Hassan yana shirya gonar sa, a dalilin damina da ta gabato,sai maciji ta sare shi.tun daga wannan lokacin ba shi da isashen lafiya,ga kuma rashin karfin jiki. A lokacin sai inna(Hindu) ta  dauki nauyin gida. Ta soma toya wainar masa a kofan gidansu tana saidawa,cinikin wainar masan suke chefanen gida ta kuma baiwa yara kudin makaranta.
  Asiya ce yar ta, ta fari. yarinya ce me kyan gaske,ba dan Adam da zai dube ta,bai kara dubanta a karo na biyu ba. A lokacin da Asiya ta shiga aji uku a sakandiri maza suka fara cinkoso akanta,gashi kuma makarantar su hade suke maza da mata. Dalibai har malamai,duk sonta sukeyi suna yabon kyan halittarta,haka ko ba  karamar fadada mata kai yakai ba.
A lokacin da Asiya ta shiga aji hudu,wani dalibi dan aji shida ya saya mata waya me tsadan gaske,yana kuma saya mata duk abinda take bukata.
Tunda Asiya tayi waya, ta soma yin facebook,da instagram da dai sauransu...nan da nan idon ta ya da'da bude wa, tana ganin hotunan mata wayayyu sai ta soma kwai-kwayonsu tana sanya hotunanta maza har matan suna yabon ta. Daga nan sanu a hankali ta soma sanya hotunan tsiraici wai duk sabida neman suna...cikin kankanin lokaci, ta zama tauraruwa a yanar gizo.
Da haka Asiya ta soma musanyan Addireshin ta da samari,tana basu damar zuwa ganin ta,su kuma kawo mata tsaraba. wasun har kyautan kudi suke bata.
  Ko da Asiya ta shiga aji shida,ido ya da'da budewa sosai,ta hadu da maza masu aji da kudin gaske. Ta zama sananniya,idan ka hadu da ita ka rantse yar wani minista ce.
 Hindu(mahaifiyar su) abin nema ya samu,bata kwaba mata,asalima yar ta Asiya na matukar birge ta sabida ta dauki nauyin gidan,a yayinda inna ta daina yin masan ma.
 Zahra wace da'ga Asiyan sai   ita, yarinya ce  me kwazo, ga zafin nema da tausayi Kamar mahaifinta.
A lokacin damahaifin ta bashi da karfi,innarsu kuma tana toya wainar masa, sai ta soma yin kitson kudi, watau idan tayiwa mutun kitso, sai ana biyaa,dan abinda ta samu sai ta baiwa innarta a hada a yi cefanne. itace kuma mai taimakon mahaifiyarta saida wainar,ba kamar Asiya ba, wace aikin ta bai wuci tayi wanka, ta ca'ba ado, ta fita zuwa gun kawaye suna zuwa yawon shakatawa.
  Wannan abinda Asiya takeyi, yana matukar batawa zahra rai. Tayi ban shawara,da nasiha akan Asiya ta daina yawon bin kawaye, a duk lokacin da ta soma bata shawara, toh fa !  Sai anji kansu. ita kuma mahaifiyarsu ta goyi bayan Asiya,tana me gargadin zahra da ta fita hanyar Asiya.
Mahaifin su kuwa bashi da ikon magana,sabida tas !  Inna take zaginsa tana tunasar shi bashi da bakin magana sabida bashi iya daukan nauyinsu ko ciyar da su. don haka,shiru yake yi duk lokacin da yaji hayaniyar zahra da Asiya.
  Na'ima wace daga zahra sai ita,yarinyace da bata wuci shekaru goma sha biyar ba. Itama din fara ce kamar Asiya.kusan komai nasu iri daya da Asiya. Zahra ce baka a cikin su, sai dai ba'a bar ta a baya ba a kyau. ta kuma fita daban cikin su sabida halin Asiya iri daya ce da ta na'ima koma nace Asiyar ce ta sa na'ima a hanya.
 Zahra ta kasance tana sha'awan da son yin aikin hannu.duk wani abu da ya shafi kirkire-kirkire ko ka'ge da hannu tana zumudin koyansa. Haka yasa ta soma koyan din.
Kudin kitso da ta tara,ta sayi waya madai'daici,ba ta komai da wayar,iya bincike-binciken ababe da zata karu dasu...da wayarta ta koyin yin sabulun wanka,wanki da mayukan gashi da ta jiki da sauransu.da kudin kitson ta ta ja jari ta soma yin sabulan wanka masu gyaran fata tana saidawa. A wannan lokacin zahra ta bude shafi a facebook,da instagram tana me tallace-tallacen sabulan da takeyi. Ta karfafa bincike akan gyaran fata,cikin kakanin lokacin ba tare da ta tafi makarantan gyaran fata ba ta kware a dalilin wayarta.
Mahaifiyarsu zahra(inna) tana matukar bakin cikin zahra har tana kiran ta da yar' wahala,sabida taki bin hanya mafi sauki domin samun kudi.

  Kwanan Zahra biyu ta dawo da'ga Abujan. Cike da farin ciki ta shigo gida.kai tsaye dakin mahaifinta ta nufa. bayan sun gaisa yayi mata marhaba da zuwa, ta ce "abba nayi wa amarya da kawayen ta kitso,kuma sunyi min alkhairi,dubu dari fa suka bani."
Cikin farin ciki ya sanya wa kudin albarka.
Ta mike ta na fadin abba yau romon danyen kifi (fefesuf din danyen kifi) zani yi maka.
Ta nufi gun inna ta sanar da ita abin alkhairin da ta samo.
Cikin bata fuska inna tace "kamar wani abin kirki kika samu, wannan a gun yar'uwarki,ai chanji ne"
Jiki a sanyaye Zahra ta bar gun inna. A dare ranar,sai da ta ware dubu goma tayi masu fefesuf(romon) danyen kifi.
Washe gari sauran kudin ta dauka taje ta sayi keken dinki.
Sai dai kash ! A ranar bata sha ta da dadi ba,sabida Asiya ta dau alwashin zahra baza ta ajiye keken dinkin a dakin su ba,sabida karansa zai dameta,uwa'uba zai bata masu tsarin daki.
Inna me taya bera bari,ta ari ta yafa.sai masifa take yi tana kiranta yar'wahala, wai zahra ta wuci matsayin da ta zama tela.
 Ganin sun hade mata kai, yasa ta dauki keken zuwa dakin mahaifinta. nan ya shiga lallashin ta.
A hankali ta soma kwarewa..bayan da ta kware ta soma sayan yadi da cinikin sabulu da ta kitso.
Sai tayi dinke-dinke tana sanyawa a shafinta na instagram da facebook, tana kuma kaiwa garin abuja idan sun gayyace ta zuwa yin kitso.
  Watarana tana zaune tana hade-haden sabulai, kwatsam sako ya shigo wayarta, tana dubawa ta gan cewan wannan fom din da ta cike watannin baya ne,inda ake sanar da ita tana daya daga cikin wadanda aka zaba zuwa kasar ingila. Iyaye da abokan arziki sun tayata farin ciki,da kuma fatan alkhairi.
      BAYAN WATANNI TARA
Bayan watanin tara Zahra ta dawo da'ga kasar ingila. nan ta tarar da abin mamaki, domin kuwa ga baki daya gidansu ya sauya ka rantse gidan wani hamshakin me kudi ne. Da ta tambayi inna wane ne gwanin yi masu wannan hidiman ,sai dai me !  Inna ta rufe ta da fada.
Ta shiga gun mahaifinta ta tambayeshi, nan yake sanar mata wanda zai auri Asiya ne yayi masu wannan jigilan.
  Bayan watanin biyu da dawowar Zahra gwamnati ta ba da guri zahra na koyar da mata duk wani abinda ta koya daga can kasar ingila,sa'anan ana biyar ta.
Sannu a hankali Zahra ta soma zama tauraruwa domin kuwa kasuwancinta ta daukaka,ga masu koyi da ita. Nan maza suka soma kawo kai,sai dai ba wanda take kulawa haka na kara batawa inna rai,tayi masifa tayi masifa zahra bata saurareta ba.
Saurayin da Na'ima take so ya fito yace  shifa ya shirya aure,Zahra ba ta so ba, amman da shike bata da baki a gidan, ba yanda ta iya don haka aka soma shirye shiryen bukin Na'ima.
Alhaji salis mazaunin Abuja,wanda ke matukar kaunan Asiya shi ya dauki nauyin komai na bukin,shi ne kuma wanda ya gyara masu gida.
Bayan sun aurar da Na'ima,ya rage Asiya da zahra,duk da kokarin da Alhaji salis yake yi,bai sa Asiya ta natsu ta tsaya gareshi ba,sauya samari takeyi kamar kaya.
Kwance suke Asiya na waya...bayan da ta gama waya Zahra ta dube ta tace '"Ya Asiya"
Duban zahran tayi ba tareda ta amsa ba.
"don Allah ki natsu mana,ki daina yaudaran kanki da wannan kyan halittan da Allah yayi maki..
 Ba tare da Asiya ta bari ta kai maganarta ba,ta soma yi mata masifa.
Suna tsaka da haka wani yaro yayi sallama.
Zahra ce ta dubo shi..."wa kake neme ?
Ana sallama ne da Anty Asiya.
Jeka,gatanan zuwa.
 Bai fi minti goma da fitar Asiya ba,Zahra to soma jin hayaniya da'ga kofar gidansu,cike da mamaki ta sanya hijabi ta nufi zaure. Tana fita tayi riski Asiya kwance kasa a yayinda dai dai lokacin wasu mata suka shiga mota ,sukayi tafiyarsu.
Cikin rudani ta duka tana duba yar'uwata wace ke nishi sama sama ta ruga cikin gida tayi kiran innarsu,dagan nan sai asibiti.
 Satin Asiya biyu a asibiti aka sallame ta,amman kash !  Matan nan sunyi mata illa, domin kuwa sun watsa mata wani abu me cin fata ,a fuska,sai dai sa'anta guri kadan ya taba.
 Washe gari bayan an sallamo ta daga asibiti,zaune take tana kukan takaici a yayinda kawayenta da suka zo dubiyarta suna ta aikin ban baki da hakuri.
Zahra na tsakan gida tana hade-haden sabulu sai kwatsam yan sanda suka kunno kai tare da wata mata biye da su. tana ganin su ta nufe su tana tambayar lafiya ? "ke ce Asiya ?
Kai ta girgiza,dai dai nan innarsu ta fito daga dakin ta "Asiya bata nan" ta fada.
Matar da ke bayan yan sanda ta soma masifa..."ku tafi da wannan din,idan sun kawo Asiyan, sai ku sao ta"
 A'a.....mahaifinsu ya fada a yayinda ya iso gurin da rarrafe.
Duk suka juaya suna dubansa..."sai dai ku tafi da mahaifiyar Asiya din, ga ta !  Ko kuma ku bincika gidan,na tabbata tana nan ba inda ta tafi.
Nan yan sanda suka soma bincike,suna shiga dakin su zahra suka riski yan mata zuru zuru,amman ba Asiya,sunyi sunyi da su da su fadi inda Asiya take suka ki fadi,.nan matar ta hasala "ku tafi da su duka,idan ankawo Asiyan sai a sako su. Jin haka yasa wata daga cikin su ta fadi inda Asiya take,don haka yan sanda suka fito da ita suka tafi da ita.
Tashin hankali gun inna har zahran ma. Zahra da inna sun nufi folis station din da aka nufa da Asiya don jin laifin ta.
Nan yan sanda ke sanar dasu wannan matar, matar Alhaji salisu ce,saurayin Asiya. Kuma Alhaji salis yana hannun hukuma an tsare shi sabida satan kudin da yayi,matar sa kuma ta matsa masa da ya fada mata abinda yayi da kudi, ya kuma shaida mata Asiya ya kashewa kudin don haka tana bukatar a biya kudaden sama da miliyan goma
Dafe kirji inna tayi a yayinda Zahra tayi siririyar tsuki...ina ta juyo ta dube ta.
Dai dai nan matar Alhaji salis ta shigo. zahra ta dube ta tace "kina da wata shaida cewan ya baiwa Asiya kudi ?
Ba sai na nemi shaida ba,sabida mijina ba zai yimin karya ba.
Toh shikenan naji,zamu hadu a kotu kenan,har cin zarafi da kika  yi mana sai kinyi bayani. fadin zahra
Ta juya ta rike hannun mahaifiyarta suka fice.
Bayan sun koma gida zahra ta fashe da kuka "Abinda nake hangowa kenan inna, ki dubi yanda mutane ke kallon mu yanzun da muke dawowa ? Sunayi mana zunde.
Toh meye mafita yanzun ?    
Wallahi ban sani ba...fadin Zaha.
Tau meye sa kika cewa matar na za'a hadu a kotu ?
Uhmmm....kar ki damu,na san abinda nakeyi,koda ta amince mu tafi kotun,zamu tafi din sabida ba wata kwakwaran shaida da zata bayar cewan Alhaji salis ya baiwa Asiya kudi fiye da miliyan goma.
Humm...toh shikena.
Mahaifinsu da ke sauraronsu yayi gyaran murya, ya soma gargadin Zahra da ta cire hannunta a sha'anin inna da Asiya.
Cikin ikon Allah Zahra tayi ta fadi tashi don ganin an sako masu yar uwa,cikin sa'a kuwa Asiya ta fito.
 Zahra ta cigaba da gudanar da harkokin ta da sana'aoin ta,ta zama daya tamkar dubu.

Suna
-Aisha M. Gana

Copy/paste
Read More »
Designed by Jide Ogunsanya.