Pages

Thursday 31 May 2018

Page 45 of SOYAYYAR MU ๐Ÿ‘ซ

*SOYAYYAR MU๐Ÿ‘ซ*
          By Ganarious.
Page4⃣5⃣

√°•_<>gaisuwa ta mussamman ga mutan *KENYA,NAIROBI*...i heart u all.๐Ÿ’–๐Ÿ’๐Ÿ’ž

√°•_<> *NAZHEE YAREEMA*✌๐Ÿผ

√°•_<> baby love *UMAIMAH BASHIR GWANDU*๐Ÿ˜˜๐Ÿคฑ๐Ÿป, Allah ubangiji shi raya min ke.

√°•_<> domin ku mutan kontagora, *GIDAN SARKIN GOBIR* in particular.

√°•_<>inai mana fatan alkhairi yan'uwa marubata har makarantan ma๐Ÿค๐Ÿผ... *assalam*

       **        **        **
 Ilham ta nemi da Cynthia ta zauna su fuskanci juna.

Bayan da ta zauna suna fuskantar juna kamar yanda ta bukata, ilham ta dube ta cikin ido, murmushi tayi sa'anan tace "hannayenki,kafafunki, duk ilahirin jikin ki rawa sukeyi,sabida a tsoroce kike...tayi furucin ne, a yayinda ta dukar da kanta karkashin table tana leken kafar cynthia.

Tayi shiru na dan lokaci, sannan ta cigaba da fadin "kina mamakin yanda akayi na san cewan ke ce ko??
Ta cigaba da kallon ta cikin ido "na san wannan aikin umurnin wa ko wani kika bi.....du ba ki gan halin tashin hankali da suka sanyanki,ina da tabbacin zuciyarki ma tana iya bugawa sabida tsoro,don haka inai maki gargadi da kuma baki shawara,ba sai kin bari wannan maganar tayi nisa ba kawai ki fadi gaskiya,ki fidda kanki.
Idan kuma kina tunanin baza'a iya kama ki ba, toh ki sani ina da hanyoyi da dama da zani bada ke tare da kyakyawan shaida.

Ilham ta sakeyi murmushi me dauke da ababe dayawa, ganin yanayi cynthia.
..."shin wai ko bikiyi tunanin yanda akayi nasan cewan ke ce kika sanya min kwayoyin nan a jaka ba?

Sai a lokacin cynthia ta fara in'in-niyah tana sonyi magana, sai dai maganar ma bata fita.....sai bebanci.
Ogan yan sanda dake tsaye yana kallon ikon Alla ya duko tareda da'fa ta.."calm down....calm down,u can do it ya fada.
Sai bayan da ta dan natsu sannan ta fara magana.
"Gaskiyarki...kamar yanda kika fada,ba sai an tafi da nisa ba,nice na saka kwayoyi a jakarki kuma umurni na bi.

Tsale Hisham ya da'ka tare da dan ihunsa yayisu ne lokaci daya, sa'anan yayi sujjada anan guri yana meyiwa Allah godiya.
Nan da nan gurin ya dauki sautin Alhamdulillah.

Ogan yan sanda ya zauna tare jan kujeransa yana fuskantan cynthia cikin mamaki...."ke ce fa?

Ta da'ga kai,a yayinda take share hawaye.
...eh,nice kuma kamar yanda ta fada, umurnin na bi.
Umurnin wa kika bi?
Wata ce me suna HAJIYA ZUBAIDA.
ilham ta kai kallonta ga mahaifinta, shima din, ita yake kallo wanda a zahiri,tashin hankali ya bayyana a fuskarsa.
Mutan gun kuwa,banda salati ba abinda sukeyi.

Nayi tunanin hakan,shiyasa banyi mamakin jin sunarta ba.
Ogan yan sanda ya nemi sanin,alakar hajiya zubaidada ilham...alhaji buba ne yayi masa bayani, mamaki ya bayyana a fuskarsa,yana mitan me zai sanya hajiya zubaida Tayiwa ilham haka.
Duban mr. Ahmad yayi "zamu bukaci wasu da'ga  ma'aikatan ku,domin bin yan sanda mu zuwa nigeria tare da me laifi....idan sun isa,sai su damkawa polisawan ku da'ga nan suyi harraman chebke zubaidan..
"Tabbas ke mayyace....ya juya ga ilham.
Nan jama'an gurin suka fashe da dariya.
No...no....no......ni ba mayya ba ce,ta maida masa.
Toh idan ba hakan ba ya ya akayi kika san cynthia ce ta sanya maki kwayoyi a jakka?
"Hikima ds basirah..! Ta fada tana duban ogan yan sanda a ido.

Enhennn....karin bayani.
Ka   ga......da farko dai tunda kuka taho dani nan nake addu'a,kuma na dogara ga Allah.....a lokacin da ka sanar da cewan ba wata kwakwaran shaida na shigadamuwa,haka kuma na karfafa addu'ata da Allah ya toni asirin mai wannan aikin.
ko da na nema alfarma a gun ka,ba ni da wata dabara ko hanya, tunani na shine wata sa'ain marar gaskiya baya ba'ta,don haka nayita rokon Allah da ya nunamin alama,idan har me laifin tana cikin su.
   
   A lokacin da nake fitowa,idona kar a kansu ko zani gane wata alama daga garesu.
Allah cikin ikonsa ya nunamin, duk da bani da tabbaci a lokacin.
Bayan da na karaso kusa da su, sai nagan cynthia tana hura iska daga bakinta a takaice dai da ka ganta zaka fahimci cewan bata da sukuni.....don haka rai na yabani kawai itace.
Gashi yanayinta da ta sauran da bambacin,shiyasa kawai nayi amfani da hikimata na tsorartar da ita ba don ina da wata shaida ko hujjan da zani kama ta dashi ba

TAfawa polisawa suka shiga yi,suna yabon hikimarta....daga karshe ,suka sallame ta suna zolayyarta da zama polis.

Bayan an sallami ilham, ta bi su mamee zuwa masaukin su.
a daren ranar Alhaji Buba ya sa hisham gaba ya raka shi masaukin su mamee don gah'nawa da yar' sa ya kuma yi mata sallama,sabida gobe zasu tafi.
Mahaifin mamee ne yayi masu izini da su shigo.
A falo suka tarar da su,ciki harda nazeeha da Amarah.
Ilham tayiwa mahaifinta marhaba da zuwa, tareda  nuna masa gurin zama.
Ya risina ya kara gaida mahaifin mamee,sa'annan su nazeeha  suka gaida shi bayan ya zauna.
Mamee ce ta fara barin falon, sannan su nazheeha suka bi bayanta.

Ilham da Hisham sai Alhaji Buba da mahaifin mamee ne a falon.
Alhaji Buba yayiwa Allah godiya da ya kubutar da yar' sa,sannan yayi rokon Allah da ya tsare ta daga masu shairi irin su hajiya zubaida.
BAyan nan yayiwa ilham nasiha,ya kuma yi mata kare ta, a matsayinsa na uba.
mikewa ilham tayi,cikin farin ciki ta yi taku zuwa inda mahaifinta ke zaune
Ta rusuna a gabansa...."Alhamdulillah,ina godiya ga Allah da yasa ka gane halin hajiya zubaida,ina kuma yi masa godiya da ya maida mana ni'ima,watau ya maida mana da kai....ina rokon ka da ka yafemin laifin da nayi maka, na kin bin umurnin ka.da fatan zaka fahimce ni.

A hankali ya da'ga kai, na fahimta Aisha.
Ka yafe mi?
Na yafe maki...
Na gode baba, inn'shaa'Allah bazan sake sa'ba maka ba.
Da haka suka shagala da hirarraki,sai da mamee ta fito, ta ke sanar masu dare yayi nisa.
Cikin zumudi ilham tace ba sai su kwana nan ba!.

Uwar harara mamee ta jefe ta dashi, ba tare da ta ce wani abu ba.
Alhaji Buba ya mike ya na me yi wa mahaifin mamee sallama,ya kuma fada masa gobe za su tafi.
Nan mahaifin mamee yayi masu fatan alkhairi,sa'ana ya ciro kudi masu yawan gaske ya mikawa Hisham.
Kin karba yayi, har sai da mamee ta sanya baki, tare da matsa masa ala dole sai ya karba.
GABA Dayansu suka yo rakiya,ilham kam ta li'kewa mahaifinta kamar baza su rabu ba.
Bayan sun fito haraban hotel din,Hisham ya tsai da me taxi, sai dai me!. Ilham ta ki sakin mahaifin ta, ta makale shi.
Idan zai shiga mota, sai ta riko shi,tayi hakan ya kai sau uku, na hudun ya juyi yace "kar ki damu,xan sake zuwa na duba ki"...duk da haka ilham bata sakar masa hannun ba.
Mamee ce ta karaso a fusace ta rike hannunta tare da jan ta da karfi.

Kamar kullum, yau ma a gidan mallam lamido yan'uwa da abokan arziki suka yi taro don yi wa Alhaji buba jaje da kuma barka.

A filin jirgin saman birnin tarayya, yan sandan kasar ladon suka damkawa yan sanda ta kasar nijeriya cynthia.
Nan tayi masu kwatancen gidan hajiya zubaida,basu ba'ta lokaci ba, suka tafi a yayinda wasun su suka tafi da cynthia.
A kofar gida suka tarar da ita,ta bude murfin mota tana shirin shiga.
Sunyi parking gefenta,suka fito zuwa inda take.
Assalamu alaikum...daya da'ga cikin su ya fada.

Wa'alaikumussalam ta fada tana yatsine yatsine.
Don Allah ko nan ne gidan zubaida?
Eh....
Toh ko dai ke ce?
Eh...nice ta fada, cikin isa da takama.

"You are under arrest......"
Arrest?..... na me?
Ki biyo mu, idan kin je can din zaki ji.
Ganin cynthia ya sa ta razana,asirina ya tonu ta raya a zuciyarta.

Alhaji Buba ne tsaye kofan gidan hajiya zubaida, a fusace yake kwankwasa kofar.
A guje me gadi ya zo, yana gunguni...
Ganin me bugun kofan ya sanya shi murmushi.
Har kasa ya duka..."sannuvda zuwa alhaji
..."yauwwa, sannunka dai,ya aiki?
taauuh....da godiya,amman tunda ka bar gidan nan gaskiya bani jin dadin aiki a gidan nan.
ba yanda dan adam ya iya sai hakuri...fadin alhaji buba.
"Gaskiya ne".
Me gidan tana ciki?
A'a....polisawa sun tafi da ity a.
Ok...ya fada a takaice,tare da sanya hannu a aljuhu ya ciri dubu daya ya mika masa..."gashi, a aikawa iyali, ba yawa.
Haba dai alhaji......Allah shi sanya albarka.
Da haka sukayi sallama da me gadi ya tafi gida.
Hisham ya ne ma a waya..."hello baba..
Binciko man polis statio din da zubaida take.
tau baba...

Sai da mamee da mahaifinta suka cike sati ,sannan suka dawo.....har ixuwa wannan lokacin hajiya zubaida na tsare.
Mahaifinta da abokansa sai sake sake sukeyi, suna neman duk wata hanya da zasu bi don ganin an basu belin hajiya zubaida.

    Alhaji buba zaune tare da mahaifin mamee....
...."ina tsoron mutanen nan baba,tun ranar da na sami labarin neman belinta da sukeyi, hankalina ya saka kwanciya.
Ina tunani da tsoron abinda  zai biyo baya idan ta fito.!
Mahaifin mamee ya gyara zamq yana me duban alhaji buba....cikin murmusawa yace ..."ka cire damuwa,Allah na tare da me gaskiya a koda yaushe,kuma inn'shaa'Allah baza su sake nasara akan duk wani shairin su ba.

SUNA cikin tattaunawa mamee ta shigo tare da mujaheed da abba.
Abba na ganin alhaji Buba ya nufe shi tare da rungumansa.
mujaheed ma ya karasa ya gaida mahaifinsa.

A Hankali mamee ta karaso cikin falon tana me satan kallon alhaji buba, wanda ta fahimci akwai wani abu da ke damunsa....wata zuciya ta kwabeta da fadin "toh miye naki?
Tsna cikin kallonsa ya da'go,sukayi ido hudu...murmushi ya sakar mata a yayinda ta kauda kanta.

..."baba jibi inn'shaa'Allah zan koma makaranta, niyata idan na sallami kaka swi na zo na sallame ka.
 Shiru alhaji buba yayi yana duban sa,sannan yace "allah shi kai mu,nan ya shiga yi masa nasiha da kuma shawarwari daga baya yai masa addu'o'i, ya juya ya dubi mamee wace har lokacin idon ta na kansa.

"Please idan baza ki damu ba,zan zo sallamansa kafin ya tafi,don haka ina neman izinin zuwa gidan ki.

Ba amsa ba sai zancen zuci da ta shiga yi..."kamar daman ka sa'ba neman izini na kake zuwa.

Alhaji buba ya mike yana yi masu sallam, fatan alkhairi mahaifin mamee yayi masa tare da gargadinsa da ya cire damuwa a ransa...

Tunda mamee ta koma gida take tunanin alhaji buba ta rasa dalilin damuwansa...
Wayarta ta ciro tayi kiran ilham.
Mamee na....
Yes dear kina lafiya?
Lafiya lau hamdanllah.
Toh maasha'Allah, ina nazheeha Da Amarah.
Dariya ilham tayi,..."kin manta kunyi waya just an hour ago?
and so?....sai kar na tambaya lafiyarsu?
Tauh mamee, sun tafi massallaci.
KE kina ina?

Ina daki,bani da tsarki ne
Ok...
Mamee da magana ne?
A'a....i just wanna check on u.
Kiss ilham tayi mata a waya,tare da fadin thats my mum.
yes my love...mamee ta maida mata.
Mujaheed fa?
Yana daki..
Ok..
Kinyi waya da mahaifinki kuwa?
Eh....munyi waya dazun nan.
Me ya fada maki.?ba komai...
OK...
Da wani abu ne?
a'a.
Ok....yadai fadamin yana tsoron abinda zai biyo baya idan hajiya zubaida ta fito daga hannun yan sanda.
Oh..Allah ya tsare.
Ameen.

Yau laraba, itace ranar da mujaheed zai koma makaranta.
tun da suka tashi sallan asubahi, ba su koma bacci ba.
Mamee da blessing ne a kitchen suna hada abin kari, a yayinda mujaheed da abba suka fito waje don wanke motar da zasuyi tafiya da ita.
  06:42am, alhaji buba ya iso, dai dai su mujaheed sun gama wanke motan
Bayan gaisuwa mujaheed yayi masa izini da ya shiga daga ciki.
..."je ka ka sanar wa mamanku, duk abinda ta fa'da sai ka zo ka sanar da ni.
Read More »

Thursday 24 May 2018

Page 44 of SOYAYYARMU ๐Ÿ‘ซ

SOYAYYARMU ๐Ÿ‘ซ
      By Ganarious.
Page4⃣4⃣

๐Ÿ‘‰๐Ÿผ *ALLAHUMMA INNI AS'ALUKA AL'AFIYAH.*๐Ÿ™๐Ÿผ

>mutan KENYA, 1 love๐Ÿ’–..ina godiya sosai.

> *NAZEEHA YUSUF YAREEMA*, Allah ubangiji shi bar kauna, ur comments alone keep on moving the story...

>makarantan soyayyarmu,ina mika gaisuwa ta gareku.๐Ÿค๐Ÿผ

>zaku iya samun latest page release a ganarious.blogspot.com/


       **         **         **
 Bayan da Amarah ta isa makaranta a ru'de,ta rasa sukuni,cikin tashin hankali ta dauki wayar ta,iyayenta ta nema.
Mamarta ce ta dauki waya,bata jira sun gaisa ba ta shiga fada masu abinda ya faru.
Nan mamarta ta bata shawara da ta kira iyayen ilham ta sanar da su.
Ba ta bata lokaci ba,ta nemo lambar mamee..
Mamee ta shiga tashin hankali,a haka ta kama hanyar gidan su,tana isa ta fadawa mahaifinta abinda ke faruwa,ba da bata lokaci ba sanya a binciko masa jirgin yan kasuwa,cikin sa'a kuwa suka samu.

Bayan da Amarah ta gama waya da mamee , lambar hisham ta nemo ta yi kiransa shi ma.
   Kayan jikinsa ne kawai be cire ko ya yaga su ba.
Sumbatu ya shiga yi,yana me bugun kansa sanin hukuncin duk wanda aka kama da miyagun kwayoyi a kasar ladon,sabida haka tunaninsa kawai ya ga'ma rasa ilham...

Sai da ya dan sami natsuwa, sannan ya mike ya nufi gidan kakaninsa ya sanar masu.
Jungum sukayiii....sun rasa mafita.
A halin da suke a yanzun,ba su da isasun kudi,da zai kai koda mutum daya ne kasar ladon.
Shi daman Hisham, bashi da aikin yi. Gwamnati ce ta bashi kyautuka a lokacin da ya kammala karatunsa domin kuwa babu kamarsa...Hisham dalibi ne da makarantar da kasar gaba daya ke alfahari da.
Bayan ya dawo gida nijeriya,ya sayi gida da mota,sauran kudin kuma ya' yita shagalguwa da su yana holewarsa.

Shiru shiru ba mafita, sai tambayoyi da suke masa kamar a gabansa abin ya faru..
Cikin jin takaici ya tashi ya tafi gidansu kareem....ganin yanayinsa ya tabbatarwa kareem cewan ba lafiya.

Zaunar dashi yayi ya na me tanbayar lafiya dai?
Ilham ce..ilham tana prison

What?...Kamar ya'ya tana prison,she just left.
Bani da lokacin ba'tawa, so nake duk wani kudi dake gare ka, ka bani aronsu pls, kuma zan sanya motata a kasuwa.
Ok...ok calm down,yanxun dai na tambayeka mana.

Ina sauraronka...
Ka dubo mameen nata ne?
No...ya fada a takaice.
Mikewa kareem yayi tare da mika masa hannu "tashi mu tafi gidan, lets get the information and what they inn first.

Bleesing tare da mujaheed suke zaune a falo, da'ga alama basu san wainar da ake toyawa ba.
Bayan da sun gaisa suke tanbayar ina mamee?.

Ta fita...fadin mujaheed.
Ok....suka fada tare da juyawa suka fice.

      Zaune take ta hade kai da gwiwa,a yayinda ta zurfafa a tunani..
Jin an da'fa kafadar ta yasa ta da'go..
Dan sanda ne a kanta,ya umurce ta da ta biyo shi zuwa amsa wasu tambayoyi da za'ayi mata,don gudanar da bincike kafin a zarta hukunci.

Da farko su nemi da ta ba su lanbar wani nata da'ga nigeria, ita kuwa a ranta bata son iyayenta su san da wannan maganar, don haka ta bayar da lambar wani mr.Ahmad dake aiki a embassy of nigeria dake a can.
Sunyi kiransa suka sanar masa daliba ce daga kasar najeriya aka kama da miyagun kwayoyi,don haka bayan bincike za'a zarta hukunci a kanta.

Bayan sun gama waya da mr. ahmad suka soma yi mata tambayoyi.
na take shaida masu bata da alaka da wadannan kwayoyin,an kuma sanya mata shi ne a jakarta sabida makirci da shairi irin ta muta ne.

A fusace wani dan sanda ....yace maganar banza,ta yaya zaki ce wani ne ya sanya maki su a jakarki?
.."baka tunanin idan da nice na saka su a jakkata za'a tsayar ko kamani tun a najeriya?...
idan da nice ke da su,kana ganin zani  yi sakacin sanya su inda za a gani...ka tuna fa ana bude jakat,akayi karo da kwayoyin...wannan kadai zai tabbatar maku da cewan a saka kwayoyine a jakata, don haka ina rokon ku da kuyi kwakwaran bincike.....ba ni ce zan fada maku abinyi ba,amman ina ganin mafi saukin kama me wannan laifin shine ku duba cctv cameras da kuma daukan thumb print da'ga jakan.

Shiru suka yi,suna jinjina maganarta me dauke da kamshin gaskiya.
...." kinyi gaskiya yarinya,yanda kika fada kuwa haka zamuyi,don haka yanzun zamu maida ki ciki.
Dai-dai nan mr.Ahmad ya iso,nan suka sanar masa komai,
Shi din ma rokan alfarma yayi, da su yi bincike sosai.

Ganin me kiran ya sanyata murmushi...."hello" ta fada cike da isa da gadara.
"Yes ma"...ina wuni
Lafiya lau cynthia,ya aiki?
Da godiyana kira ne na fada maki,na cike aikin.....tana can yan sanda sun tafi da ita.Don haka jibi jirginmu zai juyo,da fatan kema zaki cika alkawari.
Great job....na gode,kuma  ladan aikin ki na nan sai kin iso.
Ok ma.

Tana kashe wayar,ta fashe da dariya har tana hawaye..."yarinya kin ta'bo mutuwar ki.....mutum daya bazan bari ba cikin yan'uwanki,tunda kikayi sanadiyar rabuwata da mutumin da na ke so fiye  da rayuwata.

Jirgin su mamee na dirw ta nemi Amarah a waya.
Amarah da nazeeha sunje filin jirgi don tarbansu,da'ga nan kai tsaye polis station suka nufa.

Ba a basu damar gah'nawa da ilham ba,a dalilil wata dalilinsu na cewan sai sun kammala bincike.
Mamee da mahaifin ta sun tafi neman masauki ba don son ransu ba, kafin su kammala binciken su.

Washegari mamee da babanta tare da nazeeha da amarah suka yiwa polis station sammako...nan suka zauna, zaman jiran a fito masu da ilham.
Suna a haka, Hisham tareda alhaji Buba suka iso.

Alhaji buba cikin girmamawa ya risina ya gaida mahaifin mamee.
Bai gama gaisuwar ba, wani dan sanda ya fito ganin ya doso su, ya sanya gaba dayasu suka mike suka nufe shi da tambayar "me ake ciki?
"A bisa ga binciken mu,mun gano mutane da dama sun ta'ba wannan jakkat...don haka mun dauki thumb print na su.
Yazun zamu tafi airport,don samun wasu information sabida jirgin da ya kawo su zai koma gobe.

hukumar wannan filin jirgin ta baiwa yan sanda izinin gudanar da binciken su.
yan sanda sun bukaci da abasu vedio record wanda cctv camera ta gun ajiyan kaya tayi recording...bayan nan suka dauki thumb print din dukkanin ma'aikatan wannan jirgin wanda uku da'ga ciki sunyi matching da wanda aka dauka a jakkar....don haka suka tafi da wadannan ukun zuwa station dinsu.
Sunyi bincike da kuma yi masu tambayoyi akan wannan jakkan,sai dai sun nuna basu san da komai ba,iyaka aikinsu kawai sukayi...
Polisawa sun tsare su anan,don kara tsundumawa akan bincike.
Cctv camera kuwa cikin rashin sa'a batayi capturing gun jakkar ilham ba....don haka basu sami wata kwakwaran hujja  zai basu damar cewan ba ilham bace.
Ganin basu sami wata shaida ba ya sa sn sake fitowa da ilham don yi wata bincike,sun kuma shaida mata ba wata shaida,don haka dole a hukuntata.

Ilham ta roki alfarman da su bari ta gah'nah da iyayenta,da shike tun zuwanta gurin ta shigan masu rai,gaba dayan su suna kaunar ta.
sun fito da ita,a dai dai lokacin mr. AHMAD ya iso.
Mamee da Hisham har alhaji Buba rige'rigen rungumanta sukai,ilham kam gun mahaifinta ta nufa,ya rungume yar'sa ya na me shafan bayanta.
GANIn haka ya sanya mamee ta ja da baya tana kallonsu.
Sun jima a haka sa'anan ya sake ta,ta dubi mameenta tayi taku zuwa gare ta,. "Bani ba ce..bani bace...ta sake fadi a yayinda take shirin fashewa da kuka.
hannu mamee ta sa nisa le'ben ta'i know...i know,nasan irin tarbiyan da na baki,na kuma yarda da ke.
Ilham cikin kuka ta rungume mameen nata.

Mr. Ahmad ya nemi sanin matakin binciken,nan polisawan suka fada ba bu wata kwakwaran shaida da nuna an saka mata kwayoyin ne a jaka..don haka nan da wasu awanni idan har basu sami wata shaida ba zamu sallami ma'aikatan da muka tsare, ita kuma ilham zata fuskanci hukunci.

NAN da nan mamee da suran jama'an dake gun suka shiga tashin hankali.
Gyaran muryan da ilham tayi ya janyo hankulansu gareta,duk suka maida kallonsu gareta.
TA dubi dan sanda dake yiwa mr. Ahmad bayani..."Idan baza ka damu ba, inason idan zaku sakeyi yiwa ma'aikatan tambayoyi kuyi involving di na,da yardan Allah zan fitar maku da ko wace a cikin su ta sanya man kwayoyi a jakka.
Dariya sosai polisawan suka shiga yi..."ta yaya zaki gane,alhalin mu ba mu gano ba? Fadin dan sanda.
Kar ka damu,nayi maku alkawarin kama ko wace ce.
CIKIN amince wa suka ce "wannan kuma sai gobe,sabida akwai case din da za'ayi yanzun.
godiya ilham tayi,haka iyayenta ma.bayan nan suka basu mintuna su tattauna,sannan suka maida ta ciki.
Mamee ta kwana tsaye tana yi wa yar'ta addu'a,Allah shi kubutar da ita.
Haka sauran yan uwa.
Washegari, misalin karfe goman safe, kowana station.
Karfe goma da rabi,suka fito da ma'aikatan jirgi,bayan an fito da su sun zauna aka koma ciki, don fito da ilham.

    Daga ne'sa take kallon ma'aikatan,tare da tsira masu ido.
Tana zama tace wa ogan yan sanda..."wace ta sako kwayoyi cikin jikkata, tana cikin su"
Dariya yayi, tare da fadin da ban dariya kike fa.....wai shin ko ke mayya ce?
kai ta girgiza ba tare da tamka ba.

"Toh idan ba aikin mayta ba, daga zuwan ki,tun ba'a soma bincike ba, sai ki ce tana cikin su.
"Ganin bashi da niyar daukan maganarta da muhimmaci,yasa ta dube shi rai bace...."na rantse da wanda ya busa min rai wace ta saka kwayoyin a jakkata tana cikin su, yanzun haka a tsoroce.
Shiru yyi sabida sautin muryan me dauke da bacin rai.
Shi kenan miss cute..miss cute shine sunar da suke kiranta tun  s higowarta station  din.
"Yanzun dai zamu soma gudanar da binciken mu kamar yanda mukayi a baya,amma kafin nan, me ne ne hujarki na cewan kina son ayi komai a gaban ki?
Sabida na taimaka maku don ganin kun kama me laifin.
Ok ya fada sa'anan ya soma yi masu tambayoyi.
Wace ta fara amsa tambayoyin, tayi bayani cewan an sami thumb print din tane sabida ta taimakawa ilham a yayinda take daukan jakkarta zata kai gun ajiyan kaya..
Ta biyu da ta uku,kuwa bayanin su daya, cewan sunyi aikin su ne na gera kaya da gyaran zaman su.

Gyaran murya ilham tayi tareda fadin "excuse me".....
Gaba daya suka maida hankalinsu gare ta.
"A bani damar nayi magana"
Da sauri ogan yansanda yace na baki miss cute.


"Kamar yanda na fada a baya,na riga da na gane ko wacece a cikin su ta saka kwayoyin a jakkata....don haka bazani bata lokaci gun bincikan sauran ba , kai tsaye ita zanyiwa tambayoyi.....

Ilham ta da'ga hannunta ta nuna daya daga cikin ma'aikatan da yatsa....ke ce. Ta fada cikin da'ga murya.

Duk gaba dayan su suka maida kallonsu ga wace ilham ta nuna
Ita ko cikin kankani lokaci jikin ta ya soma bari...."ni???...ta fada
eh ke fa...
Nan ta shiga rantse rantse tana fadin ba ita bace.
Ogan yansanda ya nemi da ilham ta yi bayani ko ta kawo hujarta na cewan cynthia ta saka kwayoyi a jakkarta,idan ko batayi hakan ba, maganarta ba ta muhimmaci kuma baza su duba ba,ballantana suyi amfanin da shi.
Read More »

Tuesday 15 May 2018

Page 43of SOYAYYAR MU ๐Ÿ‘ซ

SOYAYYAR MU๐Ÿ‘ซ
      By Ganarious.
4⃣3⃣.


---- *ALLAHUMMA BALIGNA RAMADAN*...ALLAH ka bamu ikon ganin farkonta,izuwa karshenta cikin koshi lafiya,ya kuma bamu ikon Yin ibadu.......

       **        **       **
3:08pm Hisham ya iso,sabida sun ajiye magana shi da ilham cewan a yau za su tafi don yin komai,na tafiyarta da iyayenta.
Tun bayan sallan asubahi yake trying lambarta bata zuwa.
Abba da mamee ke a falon,ya risina ya gaida mameen.
Cikin sosa keya yake fadawa mamee tun a daren jiya yake trying lambar ilham bata shiga ba ko lafiya?
Ok, bara na dubo maka ita ko?
Ta jima tana buga kofa,ba ta bude ba sai da tayi kiran sunanta sa'anan ta bude.

Subhanallah ta fada a rude....rike hannunta tayi suka koma cikin dakin tare da zaunar da ita bisa gadon.
Ta dubi ilham tace "kuka kikayi haka?...mamee ta mike ta mikar da ita, gaban dressin mirror dake dakin ta nufa da ita,"dubi fuskarki".
"Kiyi hakuri....kiyi hakuri mamee,nasan nayi ba dai dai.ina neman gafararki,na sanya ki cikin bacin rai jiya,please kiyi min afuwa ki kuma auna yanda soyayyarki da mahaifinki yake.ki misalta yanda kike jinsa a ranki watakila nima haka nake jinsa....haba mamee.......mahaifina kike cewa ka'to?....nan ta fashe da kuka me karfi.
Banda kallonta ba abinda mamee take yi.

"Tacigaba da fadin duk abinda suka faru ba laifinsa bane..kar ki manta abinda ke rubuce a wasikar ko don wannan zaki tausaya masa,ko ba komai tsakaninku,mu kuma fa?

"Toh me uba....yanzun me kike shirin fada min?

Kiyi hakuri,don Allah ki fahimce ni..na ji zafi sosai da kika kira mahaifina da ka'to,ki kwatanta sanya kanki a yanayin da nake ciki.

"Naji...zan kwatanta...ta mike ba tareda ta kara wani abu ba.
Kije Hisham na falo.
Hijabi ta sanya ta biyo bayan mameen suka fito.
Rudewa Hisham yayi,ya manta da mamee a gurin don da saurin sa ya kama mata hannu yana fadin "whats wrong?
Ta kwace hannun ta,ba tare da ta amsa ba ganin haka yasa mamee ta bar masu falon
Dawowa yayi gefenta "please tell me what the problem is"
Ta sanya dan yatsa ta share hawayenta,nan ta kwashe abinda ya faru a daren jiya ta sanar masa.
Shiru Hisham yayi sabida ya rasa abin fadi.
Ta cigaba da fadin "gaskiya naji zafin furucin mamee...a son rai na na dai daita tsakaninsu kafin na koma makaranta.

"Me ye mafita?"....Hisham ya fada murya kasa kasa.
Kai ta girgiza, na rasa
Ki kwantar da hankalinki, inn'shaa'Allah komai zai zo karshe.

 Tun bayan tafiyan Hisham ,ilham ta zurfafa a tunani, tana me neman mafita.
A daren ranar bata runtsa ba,a matse take ta gan wayewan gari.
  Bayan sallan Asubahi ta shiga wanka ta shirya tsaf, sannnan ta shiga kitchen ta hada masu abin kari ta jera a dining table.
Dakin mamee ta nufa ta tarad-da idon ta arufe,ganin haka yasa ta juya zata koma.
"Karaso mana"....mameen ta fada.
Na dauka bacci kikeyi....inakwana.!
Lafiya lau,da fatan kin sami isashen bacci ko?
Eh..na samu.
Toh,maa'shaa'Allah.

"Inason zani je gidansu Amarah,da'ga nan zan je cafe.
Ido waje mamee take duban ta, da sanyi safen nan zaki je gidan mutane?
Amarah zatayi tafiya ne,jirgin karfe tara zata bi,shiyasa .
Tau a dawo lafiya.
Gidansa Amarah ta nufa,ta amshi wasu takardu sa'anan ta tafi gidan mahaifin mameen.

Ta roki kakanta watau mahaifin mamee, da ya yafe wa baban ta...nan yake sanar mata ai ya  yafe masa,ya kuma tausayamasa tun bayan da ta karanta masa wasikar kakarta.

Daga gidan kakanta,cafe ta nufa,tayi scanning wasikat sa'anan ta turawa karkaf din dangin mamanta wasun su ta e-mail ta tura masu,wasu kuma ta whats app.
Ta nema da suyi masa afuwa....ta jima zaune bayan da gama turamasu,tana tunanin abin yi....
Da'ga cafe gidan su goggoji ta nufa,a waje ta tarrar da Malam Lamido yana ssuraron radio,ta risina ta gaida shi, cikin sakin fuska ya amsa mata.
me ke tafe da ke yar'nan?
Uhmmmm...wata shawarace na zo da ita.!

Toh.ina jinki
"Me zai hana ka hada kan wasu da'ga cikin yan uwa,su je su baiwa mahaifiyata hakuri?...
Dariya yayi "kinyi tunani me kyau yar'nan,....daman kuma mun riga da mun yanke shawaran Yin hakan....gobe wasu zasu taho daga rugga,gidan mahaifinta zamu fara zuwa da yardan Allah.
Toh,Allah shi ba mu yawancin rai
ameen...
Ta mike ta shiga cikin gidan,a falo ta gan mahaifinta kwance bisa dogon kujera,da alama ya zurfafa a tunani.
Sai da ta isa gab da shi,sa'anan yasan da shigowarta.
A'isha ce...ya fada a yainda yake kokarin mikewa zaune
Nan da na tausayin sa ya lullube zuciyarta.
"Baba lafiya?...ta tambaya cikin Yanayin tausayi.
lafiya lau A'isha.!
Zama tayi kusa da shi tana me duban fuskarsa,a yayinda zuciyarta ke raya mata watakila yana tare da damuwa ko ciwo.
..
Sai bayan i'shai,ilham ta koma gida,kallo daya mamee tayi mata ta dauke kai,bayan ta gaida mameen ya haye sama tare da rufe kofar dakinta.
Dangin Alhaji Buba zun taho daga rugga....washegari su nufi gidan mahaifin mamee don neman yafiyarsa..
Daganan suka je gidan mameen,sun sami kyakyawan tarbo da basuyi zato ba,ta kuma yafe masu.

Zaune suke a dining chairs suna cin abincin dare,kararrawa ta fara ruri,gabaki dayansu suka juya suna kallon kofan,bkessing ce ta ruga zuwa bude kofan.
Bayan ta duba tagan wanda ke tsaye,sai ta dawo ta sanarwa mamee mutumin nan ne da rako abba ranan.
Nan ilham ta dubi mamee suka hada ido,dauke kai mamee tayi ta ci gaba da cin abincinta.
GANin mamee bata da niyar yin magana,yasanya ilham ta mike a hanzarce ta nufi bakin kofan.
Murmushi ta shiga yi masa tareda bashi izinin shigowa.
kai tsaye gun dining ta nufa dashi,ta jawo masa kujeran da ke kallon nata,gefen sa kuma mujaheed ne,sai da yayi sallama sa'anan ya zauna.
Ya'yansa kawai suka amsa masa sallamansa,ban da mamee.
yana zama ilham ta dauki plate ta zuba masa abinci,ta ajiye a gaban sa tareda fadin bisimillah..
Mujaheed ya mike,ya dan matsa kadan tare da fadin kowa ya dubeni...kuyi murmushi zanyi mana selfiee.
Gaba dayansu suka dubeshi dauke da murmushi a fuskarsu...

Bisimillah baba....ilham ta kara fadin,ganin bashi da niyar cin abincin.

Gyaran muryan yayi yace alhamdulillah,ban sani ni zaki zubawa abincin ba ,da nace karki zuwa domin kuwa a koshe nake.
Daman nazo ne na sanar dake,zani rabu da hajiya zubaida,kuma inason duk wani abu nasu dake gurina ,ko gurin wani nawa na maida masu.
        Ban manta ba mahaifinta ya tura makudan kudi a lokacin da aka kawo masa tallan wannan kafanin....ina fatan kina da masaniyan inds kudaden suke don haka inason ki taimaka ki mika min wannan kudin na hada na maida masa.

Kai ta shiga girgizawa....kayi hakuri baba,banason nayi jayeya da kai,duk wani abu da saka sanya ni yi a shirye nake da nabi dokar ka.... don Allah baba ka fadi wani abu da kake son nayi maka banda wanan..sabida baza ni maida masu da wannan kudin ba
Kallonta yake yi"sabida me?
Sabida na ta'ba kudin....
Wannan bai ds matsala,zani yi kokarin ganin na maida wanda kika ta'ba,sai ki bani saura....
A'a baba..! Kayi hakuri,kudin nan ba ta koma hannunsu ba, kuma shine a matsayin ko nace shi zai fanshi rashi ko nace raba mu da tayi da kai..ni da kannena zamu raba kudin.

KAR kiyi haka ilham........nayi alkawarin zani kokarta,don ganin na share maku ababen da suka faru a baya.,ya shiga lallashinta da maganganu masuvratsa jiki.
Kuka ta saka..."kayi hakuri baba,don Allah karka tilasta ni da na maida wanan kudin, besides wannan kudin baya kasar nan,sa'anan wadanda suka tayani aikin a lokacin na biyasu,don haka Kadan ya rage...
Tana kaiwa nan ta mike ta haye sama.
Tsaye take a jikin windon dakinta tana jiran fitowarsa...ta jima a gun sa'anan ta hange shi ya fito tareda abba da mujaheed....
ajiyan zuciya tayi"kayi hakuri  babana,bana son na sa'6a maka....

Cikin satin nan Alhaji buba ya aikawa hajiya zubaida da takardan saki.Tashin hankali..๐Ÿค”..

A cikin satin kuma ilham ta soma shirye shiryen kimawa makaranta,tana me takaicin yanda plans dinta ke rushewa....
Mamee ce tayi sallama ta shigo ta samu guri ta zauna tana me duban ilham har sai da ta tsargu.
"Kiyi hakuri ilham,ki bi maganar mahaifinki ki maida masu da kudin su...nan mamee ta shiga lallashinta tana me yi mata nasihohi.,kuka ta shiga yi nan ma.

A kwana a tashi yau saura kwana uku ilham ta tafi.
Ta gama aikace aikacen ciki gida,ta shirya ta nufi gidan su Amarah, daganan suka kwashi jiki zuwa gidan su nazeeha wace tunda sukayi hutu ta tafi garin su bata dawo ba sai yanzun da zasu koma makaranta.
nazeeha ta tausayawa ilham sosai jin ababen dake faruwa da ita bayan tafiyarta,nan ta shiga lallashi tare da karfafa mata gwiwa..da haka sukayi ta shawarwari da hira irinta kawaye.

Yan'uwa da abokan arziki sun yo rakiya.
A airport ilham ta tarar da nazeeha da Amarah,tare suka tafi gurin screening,bayan da an tabbatar da basu dauke da miyagun abubuwa sannan aka basu damar tafiya.

5:02 suka dira a babban birnin tarayya ta kasan landon,sikin farin ciki suka jawo jakunansu zuwa gurin screening, sai dai me, jakar ilham taki tafiya,hakan na nunin jakar na dauke da wani abu...don haka polisawa sukayo caa suka mamaye gurin domin enjinin na ta wata kara.
Bude jakar sukayi,ba su wani je da nisa ba,sukayi karo da cocaine.
Nan suka kama ilham suka tafi da ita station dinsu.
Tashin hankali da rudani sun ziyarci nazeeha da Amarah, yau wai abinda suke ji suke kallo a t.v shi ya faru da aminiyarsu.
nazeeha ta dubi Amarah tace "ki tafi makaranta da kayan,ba'ra na bi na gan wace police Station din zasu tafi da ita.

Toh nima dai nazeehan zani bi,don ganewa idona yanda za'a kwashe...kuma ku biyoni,mu bi nazeeha,ko bi Amarah zuwa makaranta
Read More »

Monday 14 May 2018

Page 42 of SOYAYYAR MU๐Ÿ‘ซ

SOYAYYAR MU๐Ÿ‘ซ
         By Ganarious.
Page4⃣2⃣

*Assalamu alaikum.!ya yan uwa..ina mai yi mana fata, da rokon Allah da ya gafarta mana dukkan zunubanmu.*AMEEN YA'RABBIL'ALAMEEN.

*visit ganarious.blogspot.com/ fo more and more.

*one love๐Ÿ’ž๐Ÿ’ž...
Mutanen *Kenya* kuna raina a kodayaushe.

         **        **      **
Bayan day an bude taron da addu'a, malam lamido ya ya nemi sanin dalilin wannan taron.
Goggoji tayi gyaran murya..."daman ya'yan bubane suke son magana da ku..
Ba tare da ta jira abinda jama'an gurin zasu fada ba,ta juya ga Hisham.
"Shiga ciki ka kira su"

Da sallamar su suka shiga falon.
Sai dai falon a cike yake babu ko gurin zama,wasu ma a tsatsaye suke....nan ilham ta shiga gaishe su,hakan da tayi yasa kannenta sun bi bayanta suna gaida jama'un.

Shiru tayi bayan gaisuwan,ta rasa ta inda zata fara bayani, ganin idon kowa na kanta ya sanya tayi karfin hali ta soma magana.

  Dafatan zaku bani aron natsuwa da hankalinku,domin kuyi wa maganata kyakyawan fahimta.
Ina me neman alfarma,da ku bani lokaci don yi magana ba tare da  an katsai ne,ko shigar min maganata ba.

Da farko dai ina sane da cewan kun san wacece ni,a dalilin Hisham.
Ta nuna mujaheed dake gefen ta da yatsa, wannan shine mujaheed kanina,yana karatunsa a kasar korean.
Sai kuma wannan muhammad.
Na sami labarin farkon haduwar mahaifiyata da mahaifina har izuwa rabuwansu.....shiru tayi na dan lokaci,sa'anan ta ci gaba, a yayinda ita ake kallo.
Ta da'go ta dube su"kuyi hakuri da duk abinda zan fada,don Allah kar kuyi wa maganata wata fasara"..."na zaunan nai tunanin cewan fa albarkacin so da kauna da mahaifiyata take yi wa mahaifina ya shafe ku gabaki daya,har ku ka kai wannan matsayin a yau..nasan komai Allah ke yi,kuma ko ba'a dalilinta ba, idan a rubuce yake da zaku shigo birnin ,ko neman ilimi,ko aiki, da sauran su ba makawa hakan zata faru.amman fa ku duba rawar ganin da mahaifinta yayi don ganin ya haskaka rayuwar ku,ko ba komai kun sami kari da wayewan kai akan addinin musulunci.....akasin da aka samu,shine butulci da kuka yi mata ga baki dayanku,har shi mahaifinmu.
Ba ku waiwaye ta da ya'yanta ba....mun rasa soyayyar da shakuwa irinta mahaifi da ya'yansa.
Bayan da na sami labari irin rayuwar kunci da mahaifiyata ta shiga bayan rabuwarsu,Nayi kuka na kuma yi bakin ciki.haka yasa na yi alkawarin daukan fansa,ma'ana duk wandanda sukayi sanadin sanya ta kunci,sai na sun dan-dani kunci kamar yanda suka sa ta.

Matakin farko akan mahaifina na fara....na kuma yi nasara sabida sace takardun kamfani da akayi gun sa, ni ce na shirya hakan.

"Nan da nan falon ya dau salatai,kowa sai salati yakeyi,suna tafa hannun irinta idan abin al'ajabi ya faru din nan.
Ita ko hajiya zubaida mikewa tayi tsunbul,kamar an tsakale ta....."ke.!kehhh ke ce? Ta fadi hakan a yayin da take nunin ilham da yatsa.

Kwarai kuwa.!...ni ce, koma ki zauna,domin kuwa yanzun zani faro maganata.

Nan ta koma ta zauna jiki a mace.
"Tabbas ni ce na shirya duk abinda ya faru....na kuma yi bakin ciki a lokacin da Hisham ya sanar wa mahaifiyata   abinda ke faruwa,ta dakatar dani,ta kuma haneni da aiwatar da shiri na na daukan fansa akan kowanenku......a yau ina son na sanar da ku wata siri da baku sani ba game da hajiya zubaida.

Nan ilham ta kwashi komai game da wasikar da kuma rayuwar mahaifiyar ta bayan rabuwarsu da mahaifinta ta sanar masu.....falo ya dauki hayaniya,daga masu jimamin wannan maganar,da masu tausayawa mamee da dai sauran su.
Ilham ta share hawayen da ke makale a idonta,ta juya zuwa ga hajiua zubaida....."kin cuci mahaifiyarmu,kin cuce mu, a sanadiyar son zuciya da makirci irin naki mun rasa soyayya da kulawa irinta mahaifi da ya'yansa.
Kanina muhammad bai taba gani ko jin dumin mahaifinsa ba...kin raba mu da mahaifinmu,na muzguna,an saka shi gidan yari akan laifin da baiyi ba......wace hukunci kike tunanin ta dace da ke?....
Hajiya zubaida sai rawan sayi takai,ganin haka ya sanya alhaji buba yayi gyaran murya sa'anan ya soma magana "ko kadan baki laifi ba....na chanchanci abinda da ya fi hakan ma da'ga gare ku.
Gaskiyar maganarki...da'ga ni har yan uwana albarkacin mahaifiyar ki muke ci har izuwa yanzun,don haka ina me neman afuwanku da ke da kannenki da ku yafe min....
Nan ilham ta fashe da kuka ba tareda ta bari baban ta ya karasa maganarsa ba...."me yasa hajiya zubaida tayi mana haka?....me yasa tayi wa mahaifiyata haka?
Alhaji buba ya mike yayi taku zuwa inda take tsaye" kiyi hakuri, ba laifinta ba ne...na da'de  da dawowa hayyacina,sai dai a lokacin komai yayi nisa baya gyaruwa shi yasa na hakura da na zauna da ita,ba tareda tasan na dawo hayacina ba.

No..no...baba da ka komawa mahaifiyata a lokacin...kai kawai take bukata a lokacin.
Kai ya girgiza.....bazata saurare ni ba a lokacin.

"Toh baba mu fa?.....me yesa baka zo neman mu ba?
Ya share hawayen da ke shirin zubo masa..""da'ga ranar da na rabu da mahaifiyar ku,har izuwa yanzun,kuna rai na.
dai dai sekan dayan ban taba mantaku ba,da ku nake kwana da ku nake tashi,ganin ba abinda zani baku na rayuwa ya sanya a koda yaushe ina me yi maku add'ua.
kuka takeyi sosai...
Mutan falon kuwa jikin su yai sanyi,wasu ma har suna sharan kwala.

""Baba ka yi hakuri,ni bazani yafe wa wannan matar ba".
Cikin rudani ya dube ta"haba ilham,kiyi hakuri mana"...

Ta girgiza kai.."kayi hakuri baba,kar kace na ki bin maganar,zan mata hakuri amman fa da sharadi, shine ta rabu da kai,idan kuma ba haka ba wallahi sai nayi mata abinda bata ta'ba zato ba a rayuwa don sai ta gwammaci lahira da duniya.
Kai ya da'ga..."shikenan,i will look into that, ya fada ayayinda ya yi taku zuwa gun da abba da mujaheed suke tsaye ya rungume su.

Maganar goggoji ce ta janyo hankali mutan falon gareta.
Tayiwa Allah godiya da ya kawo wanan raar sa'anan ta nemi alfarman  da su janye maganar auren hindo da Hisham.
Baba lamido ya da'go tare da fadin "kai goggoji....ya ya kike son toh muyi da jama'a?....an riga da an gayyace su fa.
Wannan ya rage naku,ni dai fatan na ku bar wannan yaron ya auri wace yake so
  Da haka taro ya watse wasu na banbami,wa su na mamaki.
Ita kuwa hajiya zubaida,ba wanda ya gan wucewarta,sai nemanta akayi aka rasa.
Abba makale yake da alhaji buba,don haka ya nemi da ilham ta bar masa shi na dan wani lokaci.

DUbu dari ilham ta baiwa goggoji.."ki rabawa mutanen rugga su sami na komawa"
Cikin mama goggoji take kallon kudin."keh yar' nan .....ina kika samu kudi masu yawa haka?
Murmushi tayi......zan fada maki inda na samu idan na sake dawowa.

A falo suka tarad-da mamee tana shan fruits,hankalikwance..
Ta juyo ta dubi ilham nan ta karanci duk abinda ke tattare da ita....
Mujaheed ya nufi dakinsa, ita kuma ilham ta zauna a daya daga cikin kujerun,ta jima zaune ba tare da tacewa mamee uffan ba,hakan ita ma mamee.
Mikewa tayi ta haye sama..mamee ko ta bi ta da kallo,daga baya tayi ajiyan zuci,tare fadin "sun bar mani da' na acan"

Washe gari har goman safe, ilham bata sauko ba,ganin haka yasa mamee ta bi ta har daki.

Inakwana mamee.!ta fadi haka a lokacin da take saukowa daga gadon ta rusuna gaban mamee.
Samun guri tayi ta zauna ba tare da ta amsa ba.

Inakwana mamee..!
Me ya hanaki bacci?...mamee ta fada
Nayi bacci.
Ban yarda ba.....ga idon ki.
Wallahi,nayi mamee..
Toh naji.....jiya kun dawo,ba wanda yace min wani abu cikin ku,! Ina da'na yake?

Danki yana gurin mahaifinsa...
Shiru mamee tayi,da farko bata so yin tambayar ba, sabida ta karanci komai, amman kewan abba yasa yin magana.

Ilham ta matso dab da ita..."mamee..
Yes dear.
don Allah ina rokon ki da ki yafe wa mahaifin mu,ko don albarkacin mu da kuma abinda ke rubuce a wasikar da kaka ta bari....wallahi ba laifinsa bane.
Mikewa mamee tayi ta ficce da'ga dakin

Bayan sallan la'asar Hisham ya iso gidan sai da be karoso cikin gidan ba.
A waya yayi kiran ilham ta fito,kar kashin bishiya suka zauna.
"Hope u r ok"
I'm fine alhamdulillah....
sure?
yes sure..!
toh whats new..nasan ababe dayawa suna gudana a kwakwalwarki yanzun.
Yes my half...ta fada tanai masa kallon so,.....ina da'da son ka sabida duk yanayi na kana fahimta.
Ya murmusa tare da tsakalan hancinta....Oh yes! Ya fada, toh yanxun me ke tafe a mind dinki.
Uhmmm.....kawai dai ina tunanin yanda zani hada kan iyayena ne kafin na koma makaranta,and i wnt that should be done as soo as possible.

Great idea.,ina bayan ki.
Thanks...ta fada.
Bayan nan suka shiga hiransu na masoya.

        **      **    **
Tun bayan da hajiya zubaida ta bar gidan su goggoji take kwance a gadon asibiti,saura kiris ta rasa rayuwarta sabida *shock* da ta kamata.
Bude ido tayi tagan ilham a kanta,cikin mamaki take kallonta.
Ita ko murmushi ta shiga yi mata...."don Allah kiji sauki,sabida samun saukin ki alkhairi ce a garemu, don haka "get well soon matar babana!....
Kwanar ta bakwai suka sallame ta.
Ita da mahaifiyarta ne a zaune,ba abinda takeyi sai kuka me ratsa xuciya...a duniya babu wanda take so kamar alhaji buba, gashi tana shirin rasa shi.
"Na rasa me ke faruwa, duk farin cikin mu na nema ya gushe....
Kiyi hakuri komai zai dawo normal.

   Ilham kwance take,tana  chatin da kawar ta nazeeha yusuf yareema...nan nazeeha ke sanar da ita sati me zuwa zata tafi makaranta.
ilham ta roke ta da ta dakatar da tafiyar ta sabida su tafi a tare.
Neman Hisham tayi a waya..yana dauka ta nemi da yazo tana son ganin sa.
Bai dauki tsawon lokaci ba ya iso gidan,a falo suka zauna.
Nan take sanar dashi chatin dinta da nazeeha.
Oopss...ya fada.
Next din kenan zaku tafi.
Nop....nace mata ta jira mu tafi tare...kasan me?
Kallonta yakeyi,ba tareda ya amsa ba.
So nake ni da iyayena da kannena gabaki daya mu tafi zuwa aikin umrah kafin na koma.
Thats not bad..ya maida mata.
mamee ce zata biya maku?
Nop...ni ce, domin kuwa harda mahaifina nake son zamu tafi tare.
Ido waje yace da wani kudi?
kudin mahaifin hajiya zubaida....matsalan yanda zan yi convincing makes,itace  kawai matsalata
"A gaskiya,ki de'6o da zafi,....ban tsammani zakiyi nasra wannan karon ba,sai ba sun nemi sanin inda kika sami wadannan kudaden.
sai na fadamasu...ba shikenan ba?
haka ne....toh yaya kike ganin zamu soma kenan?
So nake muje muyi komai na tafiyan,idan komai yayi set sai kawai na sanar masu da batun tafiyan.
the idea,is not bad,amman ina shakku fa..
SAI gab da magrib Hisham ya tafi.
bayan sallan i'shai kowa ya fito falo,ciki harda blessing....karar-rawar kofa ce ta ja hankalinsu,nan blessing ta mike ta nufi kofan..Abba ne tsaye tare da alhaji buba.
blessing tayi masu marhaba,abba rike da hannun mahaifinsa yana jansa da su karasa ciki,amman ya ki.
ganin an dauki lokaci ba'a shigo ba ya sanya ilham tambayar blessing wanene?
Abba ne...
"Toh ya shigo mana!...ta fada a fusace.
shiru shiru bai shigo ba,don haka ta mike a fusace ta nufi gurin.
a sanyaye ta rusina ta gaidashi taredA fadin bisimillah baba...
a'a..ba sai na shiga ciki ba,daman na dawo da muhammad ne.
please baba ka shigo daga ciki mana,ta marairace tana me rokonsa haka yasa ya shiga ciki.
kiris ya rage zuciyar mamee ta buga, tabbas  fillonta ne.
Ta dafe tana me karaton addu'oi,don samun natsuwa...
tare suka karo so cikin falo,ilham tayi masa nuni da kujera tare da fadin bisimillah.
mujahees ya mike ya dawo kusa da shi,ya gaishe shi..ita kuwa ilham ta hanzarta zuwa kitchen...jim kadan sai ga ta ta fito rike da tire me dauke da kayan fruits,a gabansa ta ajiye tare da fadin bisimillah.
Murmushi yayi yace na gode..
shiru-shiru ba wanda ya sake magana a cikin su,yaran duk sun lulube babansu.
ganin bashi da niyar shan fruits din yasanya ilham ta sake yi masa magana.
"Kar ki damu,ciki na cike yake....so nake ki bani dama na gaida mamarki,sai a sa'anan suka juya gun mamee, wace banda dane dane waya ba abinda takeyi...tayi kamar ba ta san da mutane a gun ba.
shiru ilham tayi ta rasa abin yi...
baba ku gaisa kawai...fadin mujaheed
"Hajiya A'isha inawuni..
ba ta da'go ta dube inda yake ba ballantana ta amsa
yayi gaisuwa kamar sau uku bata amsa ba don haka ya mike yayiwa yaransa sallama.
gaba dayan su suka bi sa don yi masa rakiyah.

A KOFar falo suka tarar da mamee tana huci, suna karasawa gab da ita ta kaiwa ilham mari.
"Uban wa yace ki shigo min da ka'to cikin gida na?....ko gidan ubanki ne?
ilham rike da kuncinta tana duban mamee, karo na farko kenan da ta kai hannunta ga jikinta.
cikin muryan kuka tace "babana ne nkuma ka'to?
Eh.....idan ba ka'to bane shi,toh meye shi....watau ni zakuyi wa butulci ko?
toh da'ga ranar me kamn ta yau ba bu ku babu wannan mutumin..
sa'anan daga yau kar ki taka kofan falon nan da sunan fita,sai da izinina.
Tana kaiwa nan ta juya ..
NAn ilham TA fashe da kuka me ratsa jiki,kannenta  kuwa sai lallashi da ban hakuri
washegari ,har karfe dayan rana ilham bata fito ba,mamee ta shiga damuwa domin kuwa tayi da ta sani bayan da ta koma dakinta..ta rasa dalilin aikata hakan alhalin tayi farinciki ganin ya'yanta tareda da mahaifinsu.
Read More »

Saturday 12 May 2018

KAZAMA CE MATATA6

๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–
*KAZAMA CE MATATA*
           ๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–๐Ÿ’–
Written by Ganarious.
Page6

å Mutan Kenya,one love.
                 **          **

  A zaton engr. Munir kwana uku kacal ya ishe sa Gama aikin da ya kai shi can jihar potakot, sai dai abin ya sha bambam da zaton sa.
Abu kamar wasa,har yana neman kwana shidda kenan.

Zaune yake yana tunanin yar' mutane da ya baro a gida wace tun zuwansa bai ji duriyarta ba ko da a  wayane...gashi bata da wayan.
Wayarsa ya fiddo ya nemo lambar inno,bugu daya ta dauka kamar jiraye take da kiran nasa.
"Assalamualaikum....
"Wa'alaikumussalam....
Inakwana... ya fada.
Kwan lahiya,ya ya aiki?
Da haka suka yita gaisuwa,ya na me tambayarta mutan gida.
Shiru yayi bayan gaisuwan,yana tunanin da'ga inda zai fara tambayarta lafiyar suwaiba.

Injin dai lahiya ko? Ta fada.
Fargawa yayi daga dan tunanin da yakai..."eh lafiya lau ,na kira ne naji yanda kuke, na kuma sanar maku cewan aikina a nan zai iya daukan tsawon lokaci,don haka bazani samu dawowa yanzun ba.

Toh..toh...wai sabida wani dalili? Ga yar mutane ka ajiye, wa kake tunanin zai dauki nauyin ciyar da ita? Kudin da ka bari guri na sai da ta gan bayansa, sa'anan hankalinta ya kwanta.
Duk a fadace take wannan magana.
A sanyaye yace "kiyi hankuri inno, ba ina nufin zani dauki tsawon lokaci bane,nan da kwana hudu zuwa biyar zani dawo da yardan Allah.
Allah shi kaimu,ta fada a takaice.
Ameen.
Nan yayi mata sallama jin yanayi ya tabbar masa da idan ya cigaba da tsawai ta maganar toh kunnensa ba zasu kwashi me dadi ba.
Dan siririn tsuki yayi,bayan da ya kashe wayar...."inno ba za ta ta'ba canja hali ba!....ya furta a yayinda yakevjin takaicin irin halinta.

Lambar kanwarsa khadija ya nema,bayan da suka gama waya da inno.
"Yaushe zaka dawo?" Ta tambaya bayan sun gama gaisuwa.
Uhmmm....sai ranar da duk kuka ganni.
"Toh amma kwana uku kace zakayi  a can.

Eh..haka ne! A tunani na aikin zai zo da sauki, amman da yardan Allah mun kusa samun settin na'urorin.

Toh Allah shi taimaka.
"Ameen kanwata,na gode da addu'ar ki.
Haba yaya.....godiyar me kuma,ai ni wajibi ne a dunga yi maka addu'a.

Cikin dariya yace "toh naji,Allah shi karbi addu'o'in ki.
Ameen yaya.

"Yauwa fareeda na gida?
"A'a .....ba ta nan,da abinda zata yi maka ne?

Eh....idan ta dawo,ta je gidana,zan bugo ta wayar ta,nayi magana da suwaiba.
Toh,zani fada mata.

 Bayan sallan magriba,fareeda ta nufi gidan engr. Munir.
Sai da kai kimamin mitin arba'in tana buga kofa, sa'anan suwaiba ta fito ta bude.

A fusace fareeda ta dube ta "haba anty suwaiba...zaki rantse da Allah,baki ji duk bugun kofan nan da nayi ba?
Tayi dariya,kyawawan hakoranta sun bayyana...."kiyi hakuri,walle na dauka nan makwabta...ko a yanzun din na fito ne don aikan me gadi,ashe ke ce  ke kwankwasa kofat.

Cikin yatsine fuska fareeda tace "toh gaskiya  ki dunga dubawa a duk lokacin da kika ji ana buga maki kofa,ba kawai kiyi tunanin makwabta ake bugawa kofa ba.
Tana kaiwa nan ta ratsa ta gefenta ta shiga cikin falon.
Tsaye tayi chakk!...tana duban falon...ta girgiza kai,tareda fadin tabdi jam,a lokacin suwaiba ta karaso inda take tsaye tana me tambayar ta "mi halan?"

A gaskiya bazan boye maki ba,idan da ya'Munir  ne ya shigo ya tarar falonsa haka,baza ki kwasa me dadi ba.

Mi na na kika nufi da haka halan?
Abinda nake nufi shine wannan falon yayi dau'da,tsarinsa ma a yanzun baiyi ba, duk da dare ne,bai hana dattin falon ya nuna ba.
"Keehhh...kiji tsoron Allah,yau fa na share falon.

A hakan? Farida ta fada cikin fidda idanuwa.
"Shin wane irin dau'da na kika nufi?.
Ba tareda da fareeda ta amsa ta ba ,ta nemi daya daga cikin kujerun ta zauna.

"Ya'munir ne ke son yayi magana da ke,don haka ya umurce ni da na kawo maki waya.
"Kai,don Allah?......amman na ji dadi walle...
Bayan nan shiru ya ziyarci falon,ba me ce da wani kala,asalima kowa da abinda yake rayawa a zuci,fareeda na kaico da halin kazantar suwaiba da kuma tausayawa yayan nata.
A yayinda gimbiya suwaiba na lullube da farin ciki a zuciyarta,duk a matse take da ta ji muryarsa.
Suna a haka engr. Munir ya kira, fareeda ta dauki wayan ta mikawa suwaiba.
"Hello" ta fada cikin matsuwa.
"Hello kina lafiya?
lahiya lau nake muniru,ya ya aiki?
Alhamdulillah...
Madallah...kwana uku kace zakayi,sai gashi kana neman ta shidda kenan , gashi kayan shayi da barmani sun kare,idan kuma na je gun inno don karban kudin da ka bari gurinta sai tayi ta masifa,idan ko ta gama masifarta abinda take bani bai wuci dari uku ko hudu ba..
Ba ta tsai da maganar ta ba har sai da ta gama kwararo masa matsalolinta,sannan tayi shiru.
"Kina nufin kayan shayin sun kare cikin kwanakin nan biyar?
eh..walle ko,sun kare.
Shikenan naji,shi kudi da na bar maki kuma fa?
su ma din sun kare wallah.
What??..sun kare fa kikace?
Eh wallahi, Allah sun kare.......
Hmmmm...lallai,yanzun me kike bukata?
Kayan shayin da kudin rikewa a hannu.
Shikenan,za a kawo maki gobe da yardan Allah, don haka kar ki sake zuwa amsan kudin gurin inno.
Toh ko ai da sauran kudi a hannunta.
A fusace yace "na dai gargade ki.
Da haka sukayi sallama da shi.
Tunda ta soma wayan fareeda ta sa mata ido,mamaki da takaicin suwaiba duk ya ishe ta,ba wata magana me dada zuciya sai korafi da bani?tabdijam ashe ya'munir na dauke da katon aiki.

Washe gari engr.munir ya  turawa  khadijah kudi cikin account din ta.
Ya kirata a waya ya sanarda ita yanda zata yi da kudin,ya umurce ta da ta sayawa suwaiba kayan shayi,sa'anan sauran kudin ta ba

DAga kasuwa  gidan suwaiba suka nufa.
Zaune take,ta baje sai baran gasashiyar gyada takai tana me taunawa.
duk ko'ina na falon bawon gyada ne...daga gefe kofuna ne da ta sha shayi da su,kai kuma ledojin biskit da ta sweet.
      Guri khadijah ta samu,tana me bin falon da ido.

"Anty bisimillah,ga gyada."
A'a na gode,.....a yayinda khadijan ta kago murmushi.
Ke fareeda ga gyada...

KAI ta karkada,fuskar nan kuwa a murtuke.
Ga shi,kayan shayi ne ya'munir ya ce a sayo maki,sa'anan ga wannan dubu biyar...

Ahhh'ahhh'ahhh....kai Allah me sona,toh sanunku da kokari,na gode...yaushe zai dawo ne?
gaskiya bani da masaniyar ranar dawowansa,amman dai cikin kwanaki nan zai dawo,da yardan Allah..
Fareeda dake zaune,tukun da suka shigo batayi magana ba sai a lokacin.."a jiyan da kikayi waya da shi baki samu damar tambayarsa ranar dawowansa ba,sai korafi da a baki,yanzun da ya baki kike tunawa da kiyi wannan tambayar ko?tunda bukatar ki ta biya
shiru tayi ta na duban fareedan..
Kehhh...khadija ta fada a yayinda take da'gawa fareedan hannu.
TA JUyo ta dubi suwaiban, zai dawo cikin kwanakin nan,kinji ko?
Toh Allah shi kawo shi lahiya.
Ameen,khadijah ta fada a yayinda take mikewa .ita ma fareeda ta mike tana yatsine yatsine.
Read More »

Thursday 10 May 2018

REMEDY FOR MOUTH ODOUR(bad breathing)

*REMEDY FOR MOUTH ODOUR (BAD BREATHING)*.

Suffering 4rm mouth odour,throat infection (bad breathing )?
Disgusting right? U always felt embarrassed.

Alright.!here we go,I have something special and simple  for u.
If really u r lucky, and take time to do it u would  be happy and say goodbye to bad breathing.
            *THINGS U NEED*
1-cloves,
2-apple cider vinegar,
3-cloves or mint oil.
          *HOW TO USE*
when u r up from ur bed in d morning, get 4-5 pieces of cloves, throw into ur mouth and chew...make sure it's well chewed until completely dissolve and then leave it in ur mouth for like 4-5 minutes and pour it out.
After this,u can brush ur tooth,using toothpaste.

And when u r off to bed, u can fetch a little portion of ur vinegar, dissolve it with warm water, pour into your mouth, squeeze and squeeze leaving it for like 3-4 minutes as well,and then u pour it out.
U can take ur cloves or mint oil after or anytime any moment.
Repeat this procedure, until d odour is completely off.
Read More »

PAGE 41,OF SOYAYYAR MU๐Ÿ‘ซ

*SOYAYYAR MU๐Ÿ‘ซ*
         By Ganarious.
Page4⃣1⃣

        **         **        **
Har cikin ransa yake jin kukanta, ji ya'ke kamar ya tashi ya rungumeta ya lallashe ta,sai dai ba hali ganin mamee da Babanta.
Su mamee kuwa,idanuwansu sunyi jajir,sai tunanin zuci su kai.
Ganin gari ya fara duhu,ya sanya Baban mamee lallashinsu, yana me yi masu nasihohi,daga karshe yayi wa margayiya addu'a sannan suka tafi....
Daga mamee har ilham basu runtsa ba a daren ranar, kowa da abinda yake rayawa a ransa.

Washegari bayan Hisham ya gama waya da ilham ya tabbatar tana lafiya,ya mike tare dayin wanka ya shirya..kai tsaye gidan kakaninsa ya nufa.
Yana shiga yayi karo da Baba yusuf...
Da sallamarsa ya shiga,wanda maimakon baba yusuf ya amsa, sai ya shiga yayyafa masa masifa,zaginsa yake sosai cikin da'ga murya...ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba,tashin murya sa ne ya fito da malam Lamido(kakan Hisham)...sai da malam Lamido ya baiwa baba yusuf hakuri sa'anan ya sassautawa Hisham.
sai bayan yayi shiru sannan hisham ya risina yana gaida su, nan ma bai amsa ba.
Malam Lamido ya amsa tare da tambayarsa lafiyarsa kuwa?...kwana hudu kenan ,muna nemanka,babu kai ba labarinka hakan yasa hankulanmu sun tashi, gashi kuma ba'a samuka a waya...ina ka shiga??
Kuyi hakuri...tafiyace ta kami ni ba zato,kuma inda na tafi din babu network..shiyasa ba ku samu na a waya.
yana kaiwa nan Goggoji ta shigo..tana ganin Hisham ta shiga yiwa Allah godiya, da farin cikinta ta shiga tambayarsa abinda ya faru.
Hisham dan lelen Goggoji,cikin kankanin lokaci ta hada masa abinci kala kala..ko wani idan ta shigo ta ajiye a gaban sa sai ta ta'ba shi ko tace me kake so dan nan?
shi ko a takure yake,duk ya matsu ya gan wucewar Baba yusuf..
Suna a haka wayar Baba yusuf ya shiga ruri.
Farin cikinsa ya bayyana ganin Baba yusuf ya mike,yanai wa malam Lamido sallama.
Ya kai bakin kofa sai kuma ya dawo,yana me nuni Hisham da dan yatsa"karfe takwas yayi maka a gida na,katin gayyata suna gu na,don haka ka zo ka amsa."
Toh ya fada...a yayinda kirjinsa ke bugun uku-uku...ba abinda ke zuwa masa a rai,sai amincewan da ilham tayi da aurensa.
Mikewa yayi ya nufi inda goggoji ke zaune, tana kwa'don zogale..ganin Hisham na sanya ta farinciki,don haka ta shiga yi masa murmushi a yayinda take mika masa kujeran zama...."ka gaji da jira ne ka biyo?

A'a .....wata magana nake son zamuyi da ke.

Toh..toh ango.
Shagwabewa yayi.."gaskiya da wace nake son na aura,don Allah kar su tilasta min auren wace bana so."

Ta kwantar da murya tace 'idan baka so toh babu me tilasta ka....

Zaki tsaya min kenan?
Kai ta daga..."kwarai kuwa dan nan,mud'din ina raye,ba bu me saka dole.
Ya mike ya rungumeta tareda sumbatar ta a goshi."Allah shi bar min ke"
Ameen,ta fada tana dubansa.

Ya koma gun zamansa ya zauna,yana me sosa keya....."yauwa goggoji, hummm kinsa tun tasowa ta da girmana ban taba rokon ki wani abub ba ko?

Shiru tayi tana dubansa,sai can  tace "toh fadi, me kake so yanzun?
Kujerar sa ya matsar gab da nata "so nake don Allah ki gayyaci duk'kanin dangin mu zuwa wannan gidan ranar asabar, masu mata kuma su zo da matan su.
Da mamaki goggoji ke dubansa "akan wani dalili?

Wata muhimmiyan sanar wa ce ta taso,don haka kar ki samu damuwa,ki gayyatou su kawai.

Ta sauke ajiyar zuciya tare da fadin "toh shi kenan,na yi yanda kace din.
Cikin farin ciki ya sanya hannu cikin aljuhunsa ,dubu goma sha biyar ya fid'do, gashi ki sayi goro.

"Kai dan nan....ina kake samun kudi ne?
Keya ya shiga sosawa a yayinda yake kokarin mikewa..."zan fada maki,idan na sake dawowa.

Daga nan,gidansu ilham ya nufa.
Ya dade tsaye yana matsan kararrawa,ba'a bude masa kofa ba.
Ya taka zuwa gun megadi yana me tambayarsa "mutan gidan na ciki kuwa.?

Eh toh....hajiya dai bata nan,amman ina da tabbacin ilham da me aiki suna ciki.
Godiya yayi...sa'anan ya ciro wayarsa don yayi kiran ilham.
A dai-dai lokacin kiran ke shiga,suka ji horn,ya juya yana duban gate a yayinda me gadi ya ruga zuwa bude gate din

Motan mamee ce ta kunno kai,ilham ce ke tukin gefenta mujaheed ne,sai mamee da abba da ke zaune gidan baya.

Bayan motan ta tsaya,ya nufe su.
risinawa yayi don gaida mamee.
Abbane ya fito cikin hanzari ya makalkale shi.
Ya mika wa mujaheed hannu sukayi sallama,yana meyi masa barka da isowa.
Ya kai kallonsa ga gimbiyar sa,wace tunda ta fito daga motan shi take kallo.
Gira ya da'ga mata ba tareda yace mata wani abu ba.
lokaci daya suka shiga falon su duka,sai dai mamee ta riga su shigewa.
Kalolin abincin da blessing ta shirya basu kirguwa,mamee ce ta bada ordan da tayi su mussamman domin tarbon mujaheed...don haka ta shiga jero su a  tsakiyar falon domin kuwa dining table bai daukan su.

MAmee ce ta mike,ta shige dakinta, bayan da sun gama ciye-ciye, da shaye -shayensu.
Shima mujaheed ta tashi ya nufi dakinsa,don hutawa.
Ilham da Hisham sai abba ne a falon.
Wayar ilham ce ta shiga ruri,ta sa hannu ta janyo jakarta,ta ciri wayan.
Ganin me kiran yasa ta yin dariya tana duban hisham,shima din ita yake kallo.
"Guess who the caller is"?
Uhmmm....u know I'm good @ dat, amman waye...
It's naaazeeee....
Dariya ya shiga yi,ya mike ya dawo gab da ita,"dauka ki sa a handsfree"
"Hey u darling"...ilham ta fada cikin muryan zolaya.

Mtsssssw.....r u tryinna make fun of me,wallahi i'll definately slit ur throat...fadin naziha daga dayan bangaren.
Naziha yusuf yareema,kawar ilham ce...a makaranta suka hadu,sun kulla abotane a lokacin da suka fahimci cewan a garin kaduna suke zaune,duk da nazeeha ba yar asalin garin bace.

Kafin ilham ta amsa,Hisham yayi karaf....."har kin gama fushin kenan?
Oh i see...abinda zaka fada kenan?.
Nan nazeeha ta kashe wayarta ba tareda ta jira abinda zasu fada ba.
Dariya suke yi....'i cant wait to see my darling,nazee" fadin ilham.
Yaushe zata dawo ne..
May b sai hutu ya kare.....

Sai bayan sallan i'shai Hisham yayi masu sallama,har zuwa gun motan sa ilham tayi masa rakiya,nan yake shaida mata ranar asabar danginsa zasu hadu a gidan kakaninsa,da yardan Allah
Cikin farin ciki,tace Allah shi kaimu.

       ***        ***      ***
Ranar asabar bayan sallan asubahi ,daga masallaci Hisham ya garzaya zuwa gidan kakaninsa.
A saman dakali ya tarar da inna,mahaifiyar mamansa Binta,ya gaidata,tare da tambayarta goggoji.
"Tana daki,ta maida masa.
Ya tarar bata dakin nata,sai dai dakin cike yake da danginsu na rugga...wasu na bacci wasu kuma idon su abude,don haka ya gaida su sa'anan ya fito ya nufi cikin gida,inda yake sa ran ganin goggoji.

Zaune take tana wanke wake,da alama kosai take shirin yi

A hankali yake taku,ba tare da ya bari taji takunsa ba....har ya iso bata san da zuwan sa ba,don haka ya sanya hannuwansa ya rungumeta,tare da sumbatar gefen kuncin ta.

Kai...kai.....da sassafen nan?
Dawowa yayi gabanta "ya akayi kika san cewan nine?
Sabida duk fadin duniyar nan,babu me sumbatata,idan ba kai ba...don haka ko cikin mafarki naji an sumbace ni,toh lallai kai ne.

Dariya ya shiga yi"har a mafarki fa kikace?"

Kwarai kuwa dan nan.
Ya dora hannunsa bisa kafadarta tare da kwantar da kai,"kin san me?

A'a dan nan, sai ka fada.
Ko kin san da cewan wannan sumban da nake yi maki shi ne jigo da kuma karfafa soyayya da shakuwarmu?...a duk lokacin da zani sumbaceki,zaki ji soyayaar da kike mun ya karu.na kasance ina sumbatarki tun ina dan karami,hakan yasa soyayyarki a zuciyata ta bambamta da ta sauran dangi....bani da kamar ki,har cikin raina nake jin ki fa....kuma na san da cewan a gunki ma haka abin yake.

Haka abin a dan nan,....a koda yaushe soyayayrka na da'da karuwa ne....bani da kamar ka duk cikin ya'ya da jikokina.ban baiwa kowa matsayin da na baka ba....don haka inai maka fatan alkhairi a kodayaushe,Allah shi albarkaci rayuwaka.
Ameen ya fadaa.

TOH yanzun me ke tafe da kai da sanyi safiyar nan?
Hummm....na zo duba ki ne kawai,na so zuwa jiya, amman Allah bai nufa ba,shi yasa nayi maki sammako don da ke na kwana a rai na...
Na kuma kawo maki lemuka da zaki baiwa baki.
Toh.....ta fada a takaice.
Ya bakin? Ya sake tambayawa....
Lfiya lau,kusan dukan dangi sun zo,yan cikin gari ne ba su isowa,suma ina sa ran isowar su zuwa nan da dan lokaci.
Allah shi kawo su lfy....ya fada yana shafan fuskarsa da hannayensa.
Ni zani tafi,sai zuwa anjima zan sake dawowa.
To shi kenan,Allah shi tsare min kai.
Ameen ya fada a lokacin da ya soma tafiya.

Yayi taku kamar biyu zuwa uku,sai kuma ya dawo, "ba wani abu da kike bukata?
"A a ....
Yayi murmshi...ba kuma wata matsala ko?
A a dan nan, babu sai su kawunka da suke haukan banza,wai ala dole na fada masu dalilin tara jama'a

Kar su damu,saura kiris..
Ya maida mata.
Yana fitowa daga cikin gida ya yi kiran ilham a waya,bugu daya ta dauka.

Albishir yayi mata,ya sanar da ita burin zai cika, don haka bayan sallan azahar ta shirya zai zo ya dauketa.
Bayan sun gama wayan tayi ajiyan zuciya,tana me kara tausayawa babanta  wanda soyayyarsa ta mamaye zuciyarta,tun bayan da tasan abinda haj.zubaida da mahaifiyarta suka aikata akansa.
Tana matukar tausaya masa da danasanin kuncin da ta sanya shi,duk ta karamar lokaci ce.
ta mike tana me tunanin ko ta sanar da mamee abinda take shirin aikatawa...
Kaita girgiza...nop,mamee baza taje ba,ko ta tafi zata batamin tsarin abun.
Dakin mujaheed ta nufa,rubuce-rubuce ta tarar yana yi,ta jayo kujera gabansa
"Me kuma ake rubutawa"?
Kin mance ni young scholar ne....ya tattara takardun ya maida gefe.
Ya maido hankalinsa gunta "da magana ko"?
Kai ta da'ga ,ta sa dan yatsa ta share hawayen da suka tarun mata a ido.
Cikin yanayin tashin hankali yace "whats wrong"?
Ka shirya zamu tafi wani guri,tana fadin haka ta mike.
mikewa yayi ya sha gaban ta..."whats wrong"?
Zanyi maka bayani idan mun dawo.
Daga dakin mujaheed,dakin mamee ta nufa, kwance suke ita da abba.
A sanyaye ta haye gadon ta shiga tsakanin mamee da abba.
A duk lokacin da ilham da hau bisa gadon mamee toh tabbass da abinda ke damuwarta,ko idan bata da lafiya.

Ganin haka ya ss mamee ta juyo tana dubanta...."ya ya dai? Ta fada.
Ta sa dan yatsa ta share hawaye...."hajiya zubaida ta cuce mu! A sanadiyarta mun rasa kulawa da soyayyar uba.

HAnnunta mamee ta rike"ki daina fadin haka,ki sawa ranki haka Allah ya rubuto zai faru da ku..duk da na fahimci abinda kike nufi,amman fa karki wasu suna tare da iyayensu,ko nace mahaifinsu kuma basu sami gata,tarbiya so da kulawa irin wanda kuka samu ba.a duk lokacin da na gan ki kina kukan rashin uba sai nake ganin kamar baki gode da fadi tashi da nayi da ku ba...nayi iya yi na don kar kuyi rayuwa maraici did i not try?

Rungume mamee tayi ta shiga rera kuka.."kinyi kokari sosai mamee,Allah shi kadai zai iya biyan ki,please kiyi hakuri ba zan sake fadan haka ba...

NO..no...na fahimce ki namesake,just that inaso kema ki fahimce ni,bani son wannan feelings ya zama part of u..u understand.?
Kai ta da'ga..na gane mamee bazan sake ba.

DA haka mamee ta dunga bata magana da nasihohi masu ratsa jiki tana kuma bata misalai,suna haka mujaheed ya shigo da sallamarsa.
Ganin yanayinsu yasa shi karasowa saman gadon.
Daya bayan daya yakebduba fuskokinsu....whats happening here? Ya fada
Ilham ce ta mike tana tayarda abba daga baccinsa...tashi ka shiga wanka ka shirya zamu fita.
Ya mike cikin gigin bacci ya fada bayin mamee.

Bara naje nayi wankan,nima.
zo mana.....mamee ta fada a yayinda take kallon ilham cikin ido.

TA dawo ta risina gabanta....
"Kina ganin bani bukatan sanin wani abu?
ta murmusa,domin kuwa tasan inda maganar mamee ta dosa.
"Kinsan bani boye maki komai,inason zamu fita da kannena,idan mun dawo inn'shaa'Allah zan sanar maki.
Shikenan Allah ya tsare.
Ameen ta fada tare da ficewa daga dakin.

Bayan da ilham ta fito wanka ta da'de tsaye gaban wardrob dinta ta na me tunanin kayan da ya dace ta saka don  birge babanta....amman kuma kayan ya zamana very simple.
Ta ciri kaya sunfi a kirga,duk basuyi mata ba...don haka ta maida su.tare da yanke shawaran zuwa gun mamee don tambayar ta wacevirin kaya take sakawa ta birge mahaifinta.

A gaban wardrob ta tarar da mamee tana nemawa abba kayan sakawa,shi ko abban akwance yake lullube cikin bargo.
Tayi tsuki sai dai be fito ba tana me karasawa gun mamee a dai dai lokacin ta ciro kayan sawansa.
Mamee..! Ilham tayi kira.
Ba tareda ta dube ta ba ta amsa.
Wani irin kaya kike sakawa lokacin baya ki birge mahaifinmu?

Bazani iya tunawa ba...ta amsa a yayinda take taimakawa abba don ganin ya saka riga.
Ilham ta dade tsaye tana duban mamee daga bisani ta juya ta koma dakinta.
Doguwa riga ce tayi karo dashi,yana daya daga cikin dogayen riguna da tayi ordering daga *GANARIOUS CLOTHING*,Bayan da ta kammala shirinta ta sauko kasa,nan ta tarar da mujaheed da abba,fitowar ta kawai suke jira.
Mu tafi ko?.....ta fada tana dubansu.

Har sun kai bakin kofa sai kuma ta dawo ta nufi dakin mamee.
.......mamee don Allah ki bamu aron motanki.
Kai ta girgiza,ba tareda ta dubi inda take ba.
matsawa tayi kusa da mameen..."please mana mameen mu.
A'a nace,nasan tukin ki,idan ba ina cikin mota ba ba amince maki tukawanshi ba.
Please mamee i promise zanyi tuki cikin natsuwa...
a'a nace,ta fada a fusace..
Nan ta mike jiki a sanyaye ...tana kaiwa baki kofa ta juyo sukayi ido hudu da mameen,nan ta marairace fuska.
Mamee ta yi mata nuni da gaban madubi..ma'ana ta dauki makullin.
"Becareful" ta fada.
"I promise "ta maida mata cikin farin ciki

Suna fita tayi kiran Hisham,ta fada masa ba sai ya zo daukan su ba.
Kasuwa suka nufa, nan tayiwa mahaifinta shopping,daga kasuwa suka tsaya a gidan su Amarah...
Amarah kawar tace da suke karatu tare,nan sukayi sallan azahar,sa'anan suka tafi gidansu Goggoji.

Jingine yake a jikin motansa,sai duban agogo yakeyi.
Daga nesa ta hango shi, ta murmusa a ranta tace "isowar mu kake jira"

Yana ganinsu ya nufe su, gefen abba ya je tare da bude masa murfin motan.
"Laah.Ya'Hisham kai ma ka zo ashe".
Eh...ai nan ne gidanmu.
Wannan mutumin ma nan ne gidansu?

Eh...idan ka shiga zaka ganshi.
Tsale ya daka'naji dadi'

TA backyard suka shiga cikin gidan,a lokacin kowa da kowa na babban falon gidan.

Dakin goggoji suka shige,nan ma ba kowa...don haka hisham yashiga falon yayi kiran goggoji gefe don sanar da ita isowarsu ilham..... ya kuma sanar da ita ilham ce son magana da yan uwan.
Cikin mamaki tace "kai dan nan,wata irin magana ce da sai an tara  jama'a har daga rugga?
Nan ilham ta matso,ta rikewa goggoji hannu "kiyi hakuri,so nake su ji maganar daga bakina.

Toh shikenan ,ku biyo ni mu tafi falon.
A' a ki fara zuwa a bude taron da addu'a ,bayan nan sai ki sanar da su yaran Alhaji Buba ne ke son magana.
Shikenan,bara na shiga na sanar da su.

Jama'a mabiyan wannan labari,ina me baku hakuri....don Allah kuyi hakuri kuyi min uzuri,inn'shaa'Allah zani yita kokari kawo maku sabuwar page.
thanks.๐Ÿ™๐Ÿผ๐Ÿ™๐Ÿผ
Read More »
Designed by Jide Ogunsanya.