Pages

Friday 23 February 2018

SOYAYYARMU 38πŸ‘«

SOYAYYARMU πŸ‘«
    Written by Ganarious.
Page3⃣8⃣.

√•…KENYA NAIROBI,I ❤ u people.

√•…Labarin *KAZAMA CE MATA TA*..Yana nan a ganarious.blogspot.com/

          **          **         **
Hello aka fada daga dayan bangaren.
Muna magana na ne A'isha Al-Mustapha?.
Eh....A'isha Al-Mustapha ke magana da ku.

Ok...kina magana ne da mr. Wiliams daga House of P.O.P ta kasar landon.
Ok...ok..,ta fada a yayinda take da'ga kai kamar yana gurin.
Shekarun baya da suka shude, akwai wata mata me suna Hadiza muhammed, tayi ajiya anan house of p.o.p din.
Wannan ajiyan kuma tayi shi mussaman don ke....a opinions statement sheet din ta,ta rubuta cewan wannan ajiyan za'a baki shine ranar da kika cika 23yrs a duniya...kuma notifications dinmu sun nuna nan da wata biyu zaki cika 23din .
Personal information dinki sun nuna kina zama ne a kasar naijeriya don haka muke sanar maki da ki gaggauta shirin zuwa nan kafin ranar,sabida wasu gwaje gwaje da za'a yi don tabbatarwan ke ce.
Suna gama fadin haka suka kashe wayarsu..
Shiru ilham tayi,ta na son tuno wani.
Mahaifin mamee ya matso kusa ita yana tambayar lafiya? Suwaye ne suke kira?
Sai da ta juya ta dubi Hisham tukun wanda shike idonsa na kanta,sa'anan ta rike hannun kakanta suka karasa kan kujera.
      "Kaka.! Mamar mamee ta kan tafi dani u.k ko?
Kai ya da'ga..."eh, tana zuwa dake, meya faru? Ya sake tambayawa cikin matsuwa.

Tayi ajiya ne a house of p.o.p dake kasar london,ta kuma sanar dasu da cewan su mika mani ajiya a ranar da zani cika shekaru 23 a duniya,shine suke kira don na zo.
Ahaaf...kaji mutanen banxa,ba sai su aiko maki ba,da su ce ki tashi daga nan har kasan landan.!

Dariya tayi masa..."ah'ah kaka ba laifin su bane.
Watau gurin kamar gida ne ko nace kamar banki,zaka iya ajiya anan domin wani ko kuma wa kanka...idan karamin abu zaka ajiye kamar su takarda ko zinari ko lu'u lu'u da sauran su za'a baka akwati da lambar akwati din,dakuma komai na akwatin tau ba me iya bude ta sai kai din,ba'a kuma iya satan akwatin sabida a jikin bango aka kera ta..
Sa'anan idan ababe masu yawa ka kawo,kamar lodi lodi kudi,sai su baka daki,wannan dakin kofar ta ta computer ce,pin din da duk ka sa shi zaka bude ta dashi.
Shiya sa baza su iya aikomin dasu ba,yanxun ma naji suna fadin nazo nayi thumb print,shi yasa nake tambayarka ko mamar mamee tana zuwa dani landan,domin kuwa na tuna mu taba zuwa wani guri da nayi thumb print,alokacin ban san me hakan ke nufi ba,idan har gurine,tau fa lallai sai na yi thumb print din sa'anan zani samu access din wannan abin da ta ajiye din.

Ajiya zuciya yayi "tau gashi kuma kawunki na can,ya baro kasar".
Ahahh..ka manta can nake karatu?

Ah..haka ne fa kuma,tau shi kenan,idan kin koma gida sai ki sanar da mamanki,kiyi shiri ki tafi.
Sai bayan sallan isha'i, sa'anan sukayiwa kaka sallama.
Hisham ne ya maida ta gida.

Jikin mamee yayi sanyi lakaas da ilham ta sanar mata da abinda ya faru a gidan babanta.
tunanin mamarta ya sake dawo mata sabo,ilham bata kan so mamee na yawan tunanin mamarta,domin kuwa duk ranar da ta tashi da tunanin mamarta su kansu basu gane kanta har sai ta kwana da kwanki a sanyaye kuma ba walwala,wata sa'in kuma tayita koke koke.
ko yanxun da ilham ta sanar mata,idanun ta sunyi jajir,ta mike a sanyaye tace wa ilham ta kasance cikin shiri,zata shirya mata komai na tafiyar.

        **         **           **
Ganin mahaifiyarta bata da niyar sassautawa babanta, ya sa ta bashi shawaran da ya bar mata gidan na dan lokaci ya koma daya daga cikin gidajensa.
yaji dadin shawaran da diyarsa hajiya zubaida ta bashi..daman ko ya rasa kwanciyar hankali,ta kowani bangare baya samun sauki ga mutanen gari har na anguwa da suka sa shi gaba ana fadin daman sana'a 419, ya ke ya tara dukiyoyi haka?,yan uwa ko dariya suke masa, ga matar sa  da tun ranar da ya tako kafar sa gidan ta hanashi sukuni.
Sai da hajiya zubaida ta tabbatar da tafiyar mahaifinta sa'anan ta kwashi kayanta ta sallami mahaifiyarta.
gidanta ta nufa,da isar ta ta tambayi me gadi ko alhaji buba ya zo?.
A'a,bai zo ba ...me gadin ya maida mata.
Cikin gida ta karasa,ta tarar masu aikinta sun gyara ko ina tas.don haka ta shiga kitchen ta daura girki.bayan ta gama,ta shirya kulolin abincin a basket.
Kai tsaye gidan goggoji ta nufa da kulolin.
A falo ta iske Alhaji buba,da mahaifiyarsa goggoji,da kuma wasu jikokinta.
Ta samu guri kusa da alhaji buba ta zauna suka kara gaisawa.
Bayan nan suka shiga yin hira,irin ta anjima ba gan juna ba din nan....a cikin hiran take tambayar sa dalilinsa na rashin zuwa gida.
Shiru yay bai amsa ba.
sai da gari ya fara duhu,sa'anan ta ce da alhaji buba da ya tashi su tafi gida.
Kai ya girgiza tare da fadin, "gidan nan ba gurin zuwa na bane....nan ya sanar da ita duk abinda mahaifinta ya fada..
Ta shiga lallashinsa tana fadin bacin rai ne ya sanya shi fadin haka,yan kam kowa ya san baka da laifi a abinda ya faru.

Ganin bashi da niyar tashi,ya sa ta mike ta dauki jakarta tayi masu ssllama.
Ta nufi gida cike da takaicin abinda mahaifinta yayi mijin ta da take so kamar ranta.

Washe gari ta nufi gidan da mahaifinta ya koma da zama.bayan ya gama cin abincin da ta kawo masa,yayi mata godiya yana me tambayar yaya mamanki?
Cikin bacin rai ta amsa,ta kuma nuna masa bata ji dadin abinda yayi wa mijinta ba.
"Ai tau mijin naki ne sanadin duk abinda ya faru.
"Amman ai ba laifinsa bane...yanxun haka wani ne meyi maka hassada ya shirya wannan makirci din.
Shiru yayi, daga  baya ya ce zanyi tunani akan wannan lamarin.
A'a baba..! ga Gaskiya ka gani karara...ni fa bani son abinda zai girgiza min zaman aure na gaskiya, kuma mijina ya tsorarta da furucin ka.
Tau naji, yanzun me kike son nayi masa?
So nake ka bashi hankuri akan cin zarafin da kayi masa,ka kuma manta da abinda ya faru sabida ku daidaita.
Tau naji...ya fada.

Daga gidan mahaifinta,gidan Baba lamido ta nufa.
Ta tarar suna meeting akan auren hisham da hindo.
BAyan meeting din baba yusuf yayi kiran hisham ya sanar masa da cewan sun sanya ranar daurin aurensa da hindo.
Hisham ya rude kwarai da gaske,gidan mamee ya nufa,a bakin titi sukayi karo, zata fita shi kuma zai shigo,ta tsaida motar ta,shima ya tsaiyar tare da fitowa ya nufota.
Har kasa yake yana me gaida ta....kafin ya sake magana tace "su ilham na nan,ka karasa gida ko....zani na dubo babana.
"Tau a dawo lafiya,ina  kuma gaida shi.
Ya koma cikin motarsa ya karasa gidan mameen.

YAU ma kofan falon abude take,yayi ssllama tare da kuntsa kai.
zaune take kan dining chair tana shan fruits salad.
     Kamar yanda a duniya ba wanda ya kai sa sanin ilhma,haka ita ma tafi kowa sanin sa,ta san Hisham kamar yunwar cikinta.
Tana ganinssta fahimci hankalinsa ba'a keance yake ba.
Daga lokacin da yayi sallama take kallonsa har ya kai gun kujeru ya zauna.
kallonsa takeyi,tana son matsawa gunsa don jin meke tafe dashi,sai kuma ta basar.
zaune yayi yana dane dane wayarsa,sai huro iska yake ta bakinsa,daga baya yayi ajiyar zuci,
TSIntan kanta tayi da mikewa zuwa gunsa.
TA Zauna kan kujeran da ke fuskantarsa, nan ya dago kai ya dube ta tare da kirkiran murmushi
" me ke faruwa?...shine abinda kawai ta fada.
Shiru yayi bai amsa ta ba,sun dade a haka, ta kuma karanci irin yunwar da ke tare dashi don haka ta mike don samo masa abinda zaya ci.
ganin ta mike yasa shi rike hannunta,a tunaninsa fushi tayi sabida be amsa ta ba.
ta juyo ta dube shi,idanunsa duk sun canza.
"Please ilham ki ceci rayuwata ki amince da aurena....
uhmmmm.....kawai tayi ta cire hannunta daga nasa ta nufi hanyar kicin.
JIM kadan ta dawo rike da tire da abimci akansa,a gabansa ta ajiye tare da fadin bisimillah.
kai ya girgiza"bazani iya ci ba.
"Kaci mana ko da kadan ne" ta sake fadi.
Kai ya sake girgizawa ba tare da ya ce wani abu ba.
Ta sake mikewa ta nufi dinning inda take zaune kafin ya shigo,fruiys salad din da take sha ta dauko,ta mika masa tana fadin tau ga fruits.
Nan ma kai ya girgiza.
"Kasan dacewan kana tare da yunwa kuwa?...ta fada rai bace.
Bai amsa ba,kuma bai karbi fruit din ba.
Ajiyewa tayi ta nufi kitchen,jim kadan kuma ta fito rike da roba yogot da kofi,ta iso gabansa ta bul-bula yogot din cikin kofi.ta matsa kusa da shi ta sa masa kofin a bakinsa,ya dube ta tukun sa'anan ya bude baki.

6:00pm mamee ta dawo,nan ta sanar masa ai nan da kwana uku ilham zata tafi london.
Ya juya ya dubi ilhamsuka hada ido, sannan ya maida kallonsa ga mamee yace mata idan baza ki damu ba,zani so na rakata.
Mamee tayi shiru na dan lokaci,saanan tace shikenan Allah shi kaimu.
Ba tare da ya sanar wa kowa daga cikin iyayensa ki yan'uwa ba ,ya bi ilham zuwa kasaar london.
Read More »

Thursday 22 February 2018

SOYAYYAR MU 37

*SOYAYYARMU πŸ‘«*
By Ganarious.
         Page3⃣7⃣

√• Mutan *KENYA*,One lovvvveπŸ’

√• *HIDAYAT ABIODUN YUSUF* u r kinda of  perfectly lady every good man is praying for.!...I pray u meet a perfect spouse as u..Ameen ya'rab.

√• visit πŸ‘‰πŸΌ ganarious.blogspot.com/,for your skin Kia tips,hair treatments tips and all others.

             ***         ***
Kwana uku ilham tayi,a ranar da ta dawo mamee bata tunkareta da maganar su Hisham suka zo mata dashi ba,sai kashe gari bayan ta huta gajiyan tafiyat.

Zaune suke a falo,a yayin da mamee ke operating wayarta,ita ma ilham haka.
Shi kuwa abba ya kan dinning table ya na karatun littatafansa.
Wayar ilham ce ta shiga ruri...tana da'gawa ta fara magana ba tareda da ta bari anyi magana da'ga  dayan bangaren ba..'i'm discussing something very important with my mum,will surely get back to u when i'm done'..abinda ta fada kenan ta kashe wayar.
Hakan ya sa mamee suspecting dinta don daman bata ta'ba haka nan ba...
A hankali ta mike ta haye sama,satan kallonta mamee keyi,sai da ta shige dakinta sa'anan mamee ta mike ta lallaba ta bi bayan ta.
A bakin kofan ta tsaya tana me sauraron,domin kuwa waya take,sai dai me!...maganar da take yi a wayan bashi da ha'di da maganar su Hisham.
BAyan ta tabbatar da cewan ilham ta ga'ma wayar tayi sallama ta shiga dakin...gefen gado ta zauna,jiki a sanyaye ta dubi ilham,itama din mamee take kallo.
"Naji labarin mahaifinki yana tsare gidan kurkutu ko?"
Kallon mameen take,ba tare da ta amsa ba.
GANin bata da niyar yin magana ya sa mameen fadin "zani so ki je ki duba shi"
Tsubul ta mike kamar wace maciji ko kunama ta sara..gaban mamee ta dawo ta durkusa,gwiwowinta duka biyu a kasa..."ban ta'ba kin bin umurninki,ko sa'bq maki ba,haka zalika baki ta'ba sanya ni yin abu na ki ba,ba na kuma fatan Allah shi nunamin ranar da zani sa'ba umurninki......please and please mamee ina neman alfarma,don Allah kar ki tilasta ni yin hakan,wallahil azeem,har ga Allah bani son ganin mutumin nan....ta rike hannun mamee tare da cigaba da fadin "please mamee kar ki tursasa ni.

Ajiyan mamee tayi.."shikenan,ba zani saki dole ba.amman fa karki manta uba,ubane koman lalacin sa ubanki ne...sa'anan hannun mutun baya rubewa ya cire ya yadda.
Lokaci na nan zuwa da zaki fahimci haka,don haka bazani saki ala dole sai kin dubo shi ba...sai dai abu daya nake so dake.
fiddo ido tayi tana me sauraro me memee ke shirin fadi kuma.
"Idan har kinsa kina da hannu ko kume ke ce ki ka sa aka tsareshi,ina me umurtan ki dakiyi gaggawan sanya wa a sake shi ,kuma duk wani plans da kikayi ko kike shirin yi akan su,tau ki wargaje su.
Shiru tayi,sai idon da ta sawa mamee.

...." kina jin abinda nake fa'da maki kuwa?
Eh....naji mamee,amman....
Da hannu mamee ta dakatar da ita, "bani son jin wani abu,rashin dakatar da wadannan plans dinki zai sa nayi fushi dake,fushi kuma na hakika..don haka zabi ya rage naki.'kar ki manta rashin jin maganar mahaifiyata abinda ya janyo min'..
Tana kaiwa nan ta mike,har ta kai bakin kofa sai kuma ta juyi tana duban ilham,tate da fadin"ina fatan zuwa gobe zani ji fitowarsa ko?

Ta ja kofan bayan ta fito da'ga dakin,labewa tayi tana jiyo ilham din tan bugun kasar dakin ta tana fadin "oh my Gid,oh my god mamee why..ta mike ta shiga shurin gadon ta da kafafunta.
Mamee dake labe ta fashe da dariya,sa'anan ta nufi Dakinta.

Anyi transfering alhaji buba,da surukinsa.watau mahaifin hajiya zubaida zuwa abuja sabida shirin shigar da case dinsu babban kotu.....
A ranar da kotu ta umurci da a zo dasu,ake sanarwa da babban lauya cewan an ba'da umurni da'ga embassy cewan a kyalesu,domin kuwa me karan ya gan takardunsa.
Nan ta ke kotu ta ba'da umurni da a sake su,sai de masu tsoron nasu sunce sai akan beli za'a sake so,don haka kowa ya kawo lambar wanda zai zo belinsa.
Mahaifin hajiya zubaida ya bayarda lambar abokinsa, ayayinda shi alhaji buba ya bayr da lambar Baba yusuf.
Ana sanarwa alhaji yusuf yayi kiran yan uwansa ya sanar da su ba'a ba'ta lokaci ba kowa ya harhado abinda ke gare sa,don haka ya dauki hanyar kaduna tare da baba lamido da kuma Hisham.
Sun jima zaune ba'a bi ta kansu ba har sai da abokin mahaifin haj. Zubaida ya iso,sa'anan yan sanda suka saurare su...bayan yan rubuce rubucen da suka yi,da'ga karshe su bada izinin cewan kowa ya tafi da nasa..

Murna gun yan uwa da abokan arziki.
A gidan goggoji yan uwa suka hadu tarban Alhaji Buba.

Gidansu kareem hisham ya nufa cike da farin ciki..a nan din ya tarar da kaseem,ya sanar masu da labarin abinda ke tafe dashi, ya kuma nemi alfarma da suyi masa rakiya zuwa gidan mamee domin yi mata godiya.

Yau din ma a falo suka tarar da ita.
Zaune take kan lallausar kujeranta ta alfarma, a yayinda abba ke kwance tare da daura kansa bisa kafarta yana me karanta mata fairly tales,tana sauraro,a yayinda take shafar kansa.

Abba yanajin muryam hishma yayi sallama,ya mike,a guje ya karasa gun hisham din ya rungume shi..
Hisham ya rike hannunsa suka karasa cikin falon inda mamee ke zaune.
A tsanake suka gaida ta,sa'anan suka zauna.

Cikin farin ciki Hisham ya shiga yi mata godiya bayan gaisuwat...na yake sanar da ita an saki baba buba da surukinsa.
tayi mada barka tare da fadin yanzun dai kam za'a dunga cin abinci ko?
keya ya shiga sosawa yana me yin murmushi.
Da haka har lokacin sallah ya gabato,mikewa sukayi sukayiwa mamee sallama.
abba na makale da hisham,suna fita waje ,hisham ya duka dai dai kunnesa yana meyi masa rada.."wai ina ilham ne"
ta'be baki yayi yace tana dakinta.
Ido waje😳...Ashe tana cikin gidan nan ,duk dadewar da mukayi shine bata fito ba..
SAKE Dukowa yayi "nuna min windon dakinta a nan.
Juyawa abba yayi, a yayinda yake nunin sama,inda dakinta yake "gaaa......",ganin be karasa maganar ba yasa hisham da'ga kansa yana duban inda abba ke nuni.

πŸ‘ΈπŸ»gimbiyar ce tsaye rungume da hannayenta,ta zagaye kirjinta da su...duk abinda sukeyi akan idon ta ne.
Murmushi yayi mata,ya aika  mataπŸ’‹ kiss da'ga inda ya,ganin bata motsa ba yasa shi nuna kansaπŸ–•πŸΌπŸ™…πŸ»‍♂πŸ‘‰πŸΌ,ma'ana *I love you*...
Ta fahimci abinda yake nufi sabida yasa ba da hakan tun suna makaranta...barin jikin windon tayi ganin kareem da kaseem ma ita suke kallo.

Mahaifiyar hajiya zubaida tana sane da dawo wan mijin ta don haka take shirya masa bala'in da zai tarar,....banda hakuri da ban baki ba abinda haj. Zubaida kiyi.
Ganin mahaifiyarta ba'ta da niyar sakko wa yasa ta ji haushi. Fiiszqn jakkarat tayi,tayi hanyar fita don zuwa gida tarbon mijin ta.
tana fitowo tayi karo da mahaifinta tare da abokansa ,ta karasa gunsu cikin farin ciki tana yiwa mahaifinta barka.
sallamarsu yayi daidai da fitowar mahaiyar haj. Zubaida rike da karamar bokiti.
Ganinta yasa shiyi mata murmushi yana me murnan ganin matansa.
A tsakiyar falo suka ga'me a yayinda abokansa ke shirin zama.
shi kuwa tsaye yayi yana wage hakoransa,bokitin ta da'ga ta kwara masa daga saman kansa zuwa kasa...ALLAH ya taimake shi ya dukar da kansa.
MIYa ce a cikin bokiti.
"Azzalumi,munafikin,macuci kawai....mazinaci me ya'yan banza".
Haj. zubaida ta karaso gaban mahaifiyarta,hannun ta sa tana me toshe mata baki.
KOKAri takeyi domin ganin ta cire hannun haj. zubaidan,ita kuma ta ki cirewa a yayinda take fadin "haba mama"
Cikin sa'a ta samu ta cire hannun haj. zubaidan,tare da ture ta da karfin ta,kafin ka sani haj. Zubaidsn ta zube a kasa.
'Shege me shaggu...ta shiga tafa hannunwata a yayinda take cin mutunci cikin da'ga murya.
...."mazinaci me shaggu,hu hu hu kaji kunya azzalumi kawai,da yardan Allah sai ka tozarta a nan duniyar har lahira..sai kayi da ka sanin dawowanka wannan gidan don da zaman ka kayi a kurkutu zaya fi maka.
Ganin zagin cin muyunci ba sassauci ya sanya hajiya zubaids mikewa,ta rike mahaifiyatya tana janta da karfi...da kyar da kokawa ta samu ta shigar da ita cikin dakinta.
sololo...yayi,a yayinda abokanss suka yi mutuwar tsaye sabida abin al'ajabin da suka gani a yau......sun dau lokaci ba wanda yayi magana ko motsi cikinsu,sai da'ga baya daya daga cikinsu ya karasa gun mahaifin haj. Zubaida ya dafa shi.
"Ka daure ka shiga ciki don tsaftace jikin ka.
Hakan ya sa sauran sanya baiki,suna kuma bashi baki akan kada ya biye wa mahaifiyar hajiya zubaida....suna tsaka da bashi shawarwar da nasiha haj. Zubaida ta fito,..nan suka shiga bata baki da kuma gardadinta akan cewan tayi iya kokarinta dun ganin cewan wani mumunan abu bai faru a tsakaninsu ba.
godiya tayi masu, sa'anan suka sallami mahaifinta zasu tafi...ba su kai ga fita da'ga falon ba mahaifiyar haj. Zubaaida ta fito a guje rike da tabarya.
Yana hango ta ya ruga a guje,haka abokansa ma..da gudu suka fita daga falon a tunaninsu ta fara hauka ne.
Hajiya zubaida ta biyo ta cikin da'ga murya tayi ihun fadin "mamaaahh..."
Kiran da tayi mata ya razanar da ita,tsak.! Ta tsaya don ganinta yi kamar ta hau iska ne.

Mahaifinta da abokansa ma tsayawa sukayi chakk!..yanzun kallo ya koma kan hajiya zubaidan....
Ganin haka yasa fasheda kuka tana meyiwa mamar ta fa'da...
Ita ma din ta fashe da kuka,tana fadin duk abinda zani yi wa mahaifinki,ban rama kwatan abinda yayi min ba,toh menene na ganin laifina?.
Ganin tana cikin hankalinta yasanya abokan matsowa,suna bata hakuri duk da basu sanda abinda ke faruwa ba.
Nan ta shiga yi masu bayani...hakuri suka shiga bata suna bata baki da nasiha,daga karshe sukayi mata alkawarin zai yi mata bayani,su fahimci juna.
     "Bana son bayanin sa,idan har yaran nasa ne toh wallahi idan ya tunkare ni da zance bayani zan kashe shi".

Da kyar suka shawo kanta da lallashi ta shiga cikin gida,tare da yi masu alkawarin baza tayi masa komai ba.

Hajiya zubaida na son zuwa ganin rabin ranta,watau alhaji Buba amman ba bu da'ma,sabida gudun kar ta tafi ta barsu suyiwa junasu illa.

     Zaune take duk lissafinta a da'gule take,tsuki tayi tace" kai mamee...naso na ganar da mutanen nan kuskurensu,na so su zo gaban ki su durkusa suna masu baki hakuri,sabida cutamaki da sukayi ammamn kuma ki tsinkemin lisafi....karan kararruwan falon ya tsinke mata zancen zucin da takeyi.
A hankali ta maida dubanta ga kofa,da shike ba'a rufe ta ciki ba.
Hisham ne ya turo kofan...ya kunso kai cikin falon da sallamarsa,yana me yi mata murmushi.
Kallonsa takeyi ba tare da ta dauke idon ta ba, ba ta kuma amsa masa sallamar da yayi ba...
Har ya karaso gunta bata dauke idon ta gareshi ba,hakan yasa shi xuwa gabanta,yatsar sa ya kawo gun idonta,bata kifta ba,ba kuma ta daina kallonsa ba.
Ya duko gab da fuskarta,fuskar sa  na fuskantar nata,yana kallonta cikin ido,ita ma din kwayar idonsa take kallo...sun dade a haka,sai kuma ya kai idonsa kan lebenta yana me kallonsu,da'ga baya ya shiga matsowa da nasa leben.
TAna jin le'bensa akan nata,ta kauda kai.
Murmushi yayi ya kuma dawo gefenta ya zauna gab da ita....ya kai bakinsa dai dai gun kunnenta ya rada mata "i missed those memories we had in school"...Nan ma bata amsa amsa ba,ya kwantar da kansa bisa kafadarta..yayi hakan ne don tayi magana,amman ta kiyi.ya mike ya dawo gabanta ,ya durkusa tare da daura hannayensa bisa kafarta.."come on ilham,ni ne fa Hisham,mutumin da kike si,can you please talk to me?.
ya juma a hakan yana me rokonta akan tayi masa magana,ta ki....yana a durkushen mamee budo kofa.
rikicewa yayi,ya rasa gun zama,ga kunya.
ganin yanda ya rude,ilham ta shiga yimasa dariya ba tareda ya ganta ba.
Mamee ta karaso cikin falon,da sauri Hisham ya durkusa yana gaisheta. Ta amsa masa cikin farin  ciki.
bayan sun gama gaisuwarsu da Hisham,sa'anan ilham tayi mata barka da isowa .
mamee ta dubi ilHam a yayinda take kokarin mikewa "Babana yace na fadamaki wasu mutane sun kira shi da'ga u.k,wai zasuyi magana dake.
Ya fada masu baki kusa,amman su kira karfen tara,gobe da safe.don haka gobe da safe idan ALLAH yasa muna raye sai ki tafi.
tau .....ta fada tana me mamakin wanda ya kirata a tsohon line-line telephone na gidan kakanta,wanda shike bata san lambar ba balle ta baiwa wani.
har mamee tayi nisa,sai kuma ta juyo,ta dubi Hisham tareda tanbayarsa ko anbashi abin shaa me sanyi.
dukar da kansa yayi cikin kunya ba tare da ya amsa mata ba.
ta kai duban ta ga ilham..."sai ki tashi ki kawo masa lemu ko?.

Washe gari da sassafe ilham ta shirya,ta nufi dakin mamee zuwa yi mata sallama.
Tana baro gun mamee ta yi karo da Hisham a bakin kofan falonsu,da'ga alama ya jima da zuwa,tsaye tayi tana dubansa.
πŸ˜‰gira ya da'ga mata.
Ta dauke kai tare bin ta gefensa,ya biyota yana fadin na zo yi maki rakiya ne...
cigabawa tayi da tafiyarta,ba tareda ta amsa shi ba...
YA Rike hannunta,na ta tsaya tana duban hannunta dake cikin nasa...
Ta da'go ta dube  shi"wai dole ne sai nayi maka magana?
Ya da'ga mata kai.
Ta sake duban hannuwansu tareda fadin sake min hannu.
KIN sakewa yayi.
"Ka sake min hannu nace ko?ta fadi hakan a fusace .
ya Saki hannun,ya kuma rike kafadarta.

Uhmmmm....kawai tayi,tana me dubansa.

πŸ˜‰gira yasake da'ga mata.
"Wallahi abu zai faru yanzun nan,idan har baka dauke hannunka da'ga jiki na ba".
Da sauri ya cire hannunsa,ta cigaba da tafiyarta.
Me gadi dake tsaye yana kallonsu ya girgiza kai,yana me yin murmushi tare da bude mata gate,yana yi mata fatan adawo lafiya.
Tana fita gate,hisham ya shiga motarsa ya biyo ta a baya.
Taku take a hankali,wanda dayawan mutane sun dauka kirkiranshi tayi,alhalin kuwa hakan Allah yayi abinsa..
nisa da ita yayi parking ya fito daga motan,ya tako ya sha gaban ta.
"Ki bani dama na zama drivern ki a yau,please ilham"..
Ta dube shi ta watsar tare da bin gefensa,ta cigaba da tafiyarta.
Ya sake binta ya sha gabanta,wannan karon harda durkusawa yayi yana me rokonta akan bukatarsa,..
waigawa tayi,ganin su jama'an gurin da masu wucewa duk su suke kallo...
Batayi masa magana ba ta juya ta nufin inda motansa yake a ajiye,sanin nacin HISHAM,gashi ba'a turai suke ba.
Tsale yayi ya mike yana fadin YES..!πŸ’ͺ🏻,cikin jin dadi.
Tunda suka fara tafiyar take suburbuda masa masifa,da alkawarin idan yasake yi mata abinda yayi a yau tau wani abu zai faruπŸ˜πŸ˜„.
Shiko banda dariya ba abinda yake yi.
Gidan kakan ilham,watau mahaifin mamee suka nufa..
A waje suka tarar dashi yana sauraron labarai a redio,ilham ta rungume shi a yayinda take gaida shi...ya amsa yana mai yi mata wasan kaka da jikansa..
Ya kai dubansa ga hisham, ya nuna shi da yatsa yace "wannan shine HISHAM.
Ta da'ga kai....eh shine.
Ya bude hannuwansa,da nufin hisham yazo,ya zo ya rungumeshi.
"Idon ka kenan hisham?.
Kallon kaka yayi yace kayi hakuri kaka...
Ya daga kai tareda fadin nasan ba kaifin ka bane ai.....yaya kake?.
Lafiya lau alhamdulillah,hisham ya maida masa.
Madallah....
bayan sun gama gaisawa da shi,suka karasa cikin gida..
hajiya cikin farin ciki ta tarbe su,tareda umurtan me aikinta da ta kawo masu abin breakfast.
Kayan tea aka kawo masu da soyayyan kwai da ayaba soyeyye.
Ganin abinda aka kawo masu,kuma hisham baya shan tea,yasa ta mike ta shiga kitchen.
Jim kadan taa fito rike da plate,a gaban sa ta ajiye ba tare da tacemasa wani abu ba.
Sayeyyean indomie ce ta ajiye masa,ya dube ta ya dubi indomie din yayi murmushi,yasan sarai ilham ya dauke da soyayyarsa.
9:00am dai dai wayar line-line telephone dake falon mahaifin mamee ya fara ruri,duban ilham yayi yace na tabbatar mutumin jiya ne don haka matsa ki dauka.
Cikin faduwar gaba ta kafa wayar a kunne tare da fadin "hello".
Read More »

Monday 19 February 2018

SURE..!! U CAN GET A SOFT AND SMOOTH FEET.

Skin is exposed to harsh elements on a daily basis, from sun and wind to harsh chemicals and drying soaps. Hands and feet are particularly prone to suffering from dryness and cracking, especially in the winter months when your skin can become stressed and hardened from dry, cold air. Smooth and soften your hands and feet with a weekly routine that uses all-natural, healthy ingredients you can find at your local drugstore and around the house.
STEP1

Soak your feet and hands in warm water . Either take a bath or fill a small basin with soothing warm water . Avoid hot water , which can dry out your skin . Add a few drops of lavender or rose essential oil to the water to create a soothing sensory experience. Soak your hands and feet for about 10 minutes.
Dry off your hands and feet using a soft , clean towel.
STEP2

Slice a lemon in half and dip one- half of the lemon into a small amount of regular sugar. Use the sugared lemon half to scrub any rough areas on your hands and feet. Go over your fingers and toes as well using gentle circular motions. If you have particularly rough areas on your feet or hands, use a pumicestone or foot file to smooth out these areas.
Rinse off your hands and feet using warm water and towel dry them.
Pour a small amount of natural oil , such as coconut, almond or olive oil , onto a small cotton ball .
Apply the oil to your feet, making sure to sweep the cotton ball around and between all your toes. Reapply oil to the cotton ball as neededuntil your skin is lightly coated.
Pull on a pair of clean cotton socks or plush socks to keep your feet clean while the oil does its job.
Repeat the process of applying oil to your hands and pull on a pair of clean cotton gloves.
Keep the socks and gloves on for at least two hours and, ideally, around eight hours. Time this process for around bedtime so that the oils can soak into your skin while you sleep.
Repeat the exfoliation process about once a week. You can apply natural oil to your skin as often as every day.
Lavender or rose essential oil , optional
Sugar
1 whole lemon
Pumicestone
Cotton balls
Coconut, almond or olive oil
Plush socks
Cotton gloves
Be aware of any allergies or sensitivities your skin may have before applying lotion or oil . Purchase a deep moisturizing lotion for everyday use between oil treatments to keep your skin happy throughout the day. Reapply after washing your hands or doing the dishes.
Read More »

Make ur palm(hand) soft.

The skin on our hands take brunt of every chore—from taking care of the kids to washing dishes to weeding the garden. To make things worse, these tasks mean that you have to wash your hands frequently. All of this daily wear inevitably leads to your hands looking as though they belong to someone older than you really are.
The soaps and other cleaning products we use today can cause your hands to look discoloured, wrinkly, and rough. Luckily, there’s no need to worry. Use these three extremely easy home remedies to get back the soft hands you once had!
1. One-Minute-to-Soft-Palms Scrub
Q: What is the easiest DIY remedy for soft hands? A: Why, olive oil and sugar, of course! |
Source
Is it possible to soften your hands in less than a minute? Oh, yes it is! After a long day of work, why not give your hands instant pampering and refreshment. This wonderfully simple scrub will leave your hands feeling 10 times smoother in just a minute.
Ingredients:
1 tbsp olive oil
1 tablespoon sugar
Benefits of the Ingredients:
Ingredient Purpose
Olive oil Moisturizes and hydrates skin cells.
Sugar
Exfoliates and sloughs off rough old, dead cells.
Directions:
1. Simply put the sugar in the palm of one hand and slowly pour the olive oil into it. Using your other palm start rubbing the scrub into your palms and hands.
2. Massage your fingers and hands with gentle squeezing and circular motions for about 30 seconds.
3. Then relax your palms and let the scrub sink in for another 30 seconds.
4. Now you’re done! Simply wash out your hands with warm water and pat dry with a clean towel. So smooth, you can’t stop touching your hands, can you?
Tips:
Glove love. Detergents and dishwashing liquids contain harsh chemicals that can damage the thin skin on your hands, making them look dry, discoloured, and old. Make sure you use gloves while cleaning whenever possible!
Oh, my glove! When working out in the gym, especially with dumbbells and other weights, it helps to wear workout gloves to protect your palms from getting hard and callused over time.
Good night, sweet palms! During the night, we actually have six to eight hours of great opportunity to show some extra love to our hands. Invest in a gentle hand cream, and apply it before going to bed! Your hands will thank you in the morning.
2. Overnight Treatment: Vaseline and Socks
The ultimate deep-action overnight treatment for dull tired hands! Wake up to beautiful soft palms the next day.
Want to give your hands some extra special love? Why not try an overnight intense softening treatment using only two items:
1. Vaseline
2. A pair of socks
Vaseline is known for its ability to lock in moisture and soften even the most callous palms. Many women mention Vaseline as their number one beauty secret.
After finishing all your activities for the day, wrap up by washing your hands with a gentle soap and drying them off. Then get a dollop of Vaseline and rub it into your hands. Go ahead and take an extra 30 seconds to massage your hands gently. Then simply slip the socks over your hands and go to bed. Wake up the next day to supple, soft hands.
Instead of using socks, you could using fabric gloves, but a clean pair of old socks you don’t use anymore work just fine—and don't require a trip to the store.
Tips:
From the inside out. Ever heard of the saying, "You are what you eat"? It’s true that what you eat will show in your skin. Eat foods for glowing skin like avocados and nuts, and the vitamins and nutrients will give your skin a natural glow.
Drink up. Not drinking enough water can cause your skin to get dry, rough, and patchy. Our bodies are made up of 70 percent water so if you’re not hydrated, it will show up on your skin. If you drink water only after your lips crack, you’re already dehydrated.
Massage. When applying these natural DIY soft palm scrubs, you can also massage your hands together in a gentle relaxing manner. Gently massage your fingers, palms, and top of your hands. This will help the ingredients sink in and improve blood circulation.
3. Citrus Power! Lighten & Soften your Hands
Tired, dull and discoloured hands? This is the perfect homemade remedy for you.
Are your hands dark, discoloured, and aged-looking? Use citrus to lighten them while softening your palms.
Ingredients:
1. 2 teaspoons lemon juice
2. 2 teaspoons honey
3. 2 teaspoons baking soda
Benefits of the Ingredients:
Directions:
1. Wash your hands with warm water and a mild soap.
2. In a small container, mix together all the ingredients evenly.
3. Now apply this mixture onto your hands, rubbing it through and massaging your hands for a minute. Allow the mixture to sit on your hands for five to 10 minutes.
4. Finally wash your hands in warm water. Do not use soap directly afterwards. Repeat this process at least twice a week to remove discolouration and promote soft healthy-looking hands.
Ingredient Purpose
Lemon
Contains citric acid, which gently lightens dark spots and discoloration on skin.
Honey
Contains numerous antioxidants, which slow down aging.
Baking soda
Exfoliates skin and sloughs off dead cells, revealing new clear skin cells.
Tips:
Slather on the sunscreen! You’d be surprised how many people apply sunscreen on their faces but fail to adequately protect the skin on their hands. Before you head out, generously apply sunscreen to your hands. And yes, you need to reapply when you wash your hands!
Too hot for your own good. Beauty experts will tell you how bad hot water is for your skin. Hot water causes the pores on the skin to open wide, and exposing it to such conditions may damage your skin. Washing frequently in hot water can dry out the skin and create wrinkles.
Brrr! Not so cold! On the other end of the scale, extremely cold water isn’t good for your skin either. It can break the tiny capillaries under your skin, making it look discoloured, pale, or unhealthy. It also dries out skin, and failure to moisturize can cause premature aging.
Read More »

Friday 16 February 2018

KAZAMA CE MATA TA5

πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
*KAZAMA CE MATA TA*
           πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
Written by GANARIOUS.
Page5

√•Awwwww😘✌🏼,mutan *Kenya* one love keep us 2geda.

åina maku fatan alkhairi masoyana,na Gode sosai da addu'oin ku.

√•feedback,& suggestions din ku r higly welcome a  πŸ‘‰πŸΌ ganarious.blogspot.com/ ,thanks

åmarubuciya *A'ishah zahraadeen*,Allah shi Kara basira.

        **          **         **
   Washegari,bayan ya dawo da'ga masallaci ,dakinsa ya nufa tare da samun guri ya natsu.
Hisnul-muslim dinsa ya dauko ya shiga karantawa.....bayan ya ga'ma azkhar din ya dauki al'qur'ni me girma tareda budo suratu yasin,dukhan,rahman,waki'ah da suratu mulk..al'adar sace karanta wadannan surorin kullum safe.
Hannayensa ya da'ga yana me kwararo addu'oi,sannan ya shafa tare da mike wa.
    Ya isa gun wardrob dinsa ya fiddo riga marar hannu da waando 3quater.
Bayan ya sa kayan ya fito daga dakinsa..kitchen ya fara zuwa da niyar daukan tsintsiya.ya ci karo da kwalayen su kuloli,plates da dai sauran su..da suka zubda a nan bayan sunyi mata jere.
Ya tattara su ya kwashe su zuwa bola,ya dawo kitchen din ya share tare da goge inda ke da bukatan a goge.
Yana ga'mawa da kitchen din,ya nufi filin gudansa domin kuwa yan kawa amarya sunyi masa datti da gida,na ledar biskit nan ledan pure water da sauran su.
Gaba daya zagayen gidan sai da ya share shi.

Engr. Munir mutun ne me tsaftan gaske,ko wasa baya son datti, ba kuma yayi shiri da me kazanta,duk wanda ya sanshi ya sanshi da tsafta,hakan yasa abokansa dayayi karatu da su atare sukayi masa lakani da mr. Clean.

Bayan ya gama sharan filin gidan ya nufi falonsa,ya yi shara sa'anan ya shiga goge goge...da shike ra'bin falonsa duk gilashi ne,duk wani abun ado na falonsa gilashi ne,hakan yasa kullum safe kafin ya  tafi office sai yayi goge goge tukun.

Yana tsaka da goge gogensa yaji kamar motsin tafiya,da sauri ya waiga.
Suwaiba ce....kayan jiyan shine a jikinta har yanzun.,ga alama tashiwarta kenan da'ga bacci.

Kwan lahiyaa....tace dashi,a yayinda take murza ido.
Lafiya lau ya gajiya?
Gajiya kam ya bi jiki.......goge gogena kakai da sahiyan nan?....ta tanbaya da alaman mamakinsa.
     Shiru yayi na dan lokaci,sa'anan ya ce "al'ada ta ce kullum safe na goge gidan.!

Tabdi....ai kam an gaji...ta fadi haka a yayinda take shirin juyawa zata koma sashenta.."nikam nayi ciki zuwa yin sallah"
Subhanalillah...ido waje yace taho nan niyanga,shin wace sallan zaki na yi?
Sallan sahe mana..
Duban agogo yayi,10:09am...ya nuna agogonda yatsan sa "dubi"....karfe goma har da yan mintuna kike fadin zakiyi sallan asubahi?
Tau mi??....ta maida masa
Girgixa kai yayi tare da shan mur..."haka kukeyi a gidanku?
shiru tayi bata amsa ba ganin yanda ya murtuke fuska ya ba'ta tsoro

" toh wallahi ba zani daukan maki wannan a gida na ba...sam,ya fada yana yarfa hannu.
Karki manta kin dawo karkashina,don haka duk abinda na saki ya zaman maki dole kiyi shi.
Yin sallah a cikin lokAci yana daya daga cikin dokan da zani shinfida maki,sabida tarbiyan da nake son bawa gida na kenan...don haka da'ga yau kar ki sake
A sanyaye tace "tau,ba zani sake ba, kuma kayi hakuri".
Nayi...ya fada a dakile,da'ga idan zaki kwanta ki kwanta da niyar tashi yin salkan asubahi...infact ni da kaina zani dunga ta'da ke
Tau.....ta sake fadi.
Ma'za jeki kiyi sallan.

10:30am isa ya iso gidan engr. Munir da kula me dauke da wainar masa...inno ce ta aiko shi.
Engr.munir bayan ya gama aikinsa yayi wanka,tare da feshe jikinsa da ture me kamshin gaske.
     Lekawa yayi falin suwaiba,ba ta gurin don haka ya dakinta.
Sallamarsa ya sa ta da'go kai daga kwancen.
Kallonta yake cikin mamaki..."miyasa bakiyi wanka ba?"ya fada cikin da'ga murya
Kalonsa take yi bata amsa ba.
"Baki ji nane?....
Ta mike"yanzun da man nake da niyar yin wankan.
"Ina jiran ki a falo,idan kin fito wanka  ki xo mu ci abinci.

Baifi minti shida da zamansa ba sai ga'ta tafito.
kai ya daga ya na me duban ta cikin takaici,wai amarya kenan fa,fisabilillah,ki irin kamshi da amare keyi bata yi..siririn tsuki ya yi ba tare da taji ba.
abincinsa ya zuba ya turama mata kulan.
Har yayi nisa da ci,ba ta dibi abincin a plate dinta ba.
ya dube ta yace "ki zuba abincin mana,yanda zaki iya ci.
Plate ta dauka ta zuba abincin ta fara ci.
dubanta yake ....sam sam wannan ba ajina bace,yanda nake komai cikin class,ita ko wannan bata dashi ko kadan...wannan ba irin matar da nake son nake kasancewa da ita har tsawon rayuwa ta bane....a duk lokacin da zamu hadu sai rai na ya bacci..haka zamuyi rayuwar auren....duk a zuci ya ke wannan zancen....tsuki ya sake yi wanan karon kam a fili yayishi.
Kai ta dago tareda fadin lafiya dai?
daure fuska yayi ba tare da ya amsa ta ba.

Tana gama cin abincin ta mike zata kwashi plates zuwa cikin..
"Zauna muyi wata magana"....ya fada fuskan nan ba sassauci.
Tau...ta fada tareda koma wa ta zauna.

kina son aminci a zaman auren mu?
Eh...walle ina so.
Hakan zai samu ne idan har kin saureri ni kuma kinyi amfani da duk wani abu da zani fada maki.
akwai ababen da bana so,meyinsa ma bana sonsa balle na shirya da shi.
πŸ‘€kallonsa kawai take,tana me sauraronsa.
Abu na farko,shine me wasa da ibada kamar yanda kikayi da'zun,ina fatan baza ki sake ba,idan har hakan ya faru gaskiya bazaki kwashi me sauki ba.
Sa'anan abu na biyu,ni mutun ne me tsafta,duk me kazanta bana shiri da shi....da fatan zaki kiyaye hakan,
Kai kawai ta da'ga masa.
Shiru yayi na dan lokaci,ya dube ta yace ababenda nake ki' suna ds yawa amman idan kin kiyaye wadannan biyun sauran basu da matsa.
kin fahimce ni ko.?
Eh ....ta fada cikin sanyi murya.

ABIncin rana da ta dare duk inno ce ta aiko masu.
Bayan sallan isha'i engr. Munir ya nufi gidansu inno,yayi mata godiya tare da sanar da ita zancen tafiyar sa zuwa potakot gobe....addu a tayi masa.
Kudi ya ciro ya mika mata"gashi,koda suwaiba zata bukaci wani abu,duk da ba dadewa zaniyi ba.
cikin wage baki tace tau tau madalla....inno abinso ya samu.
Bayan ya dawo yake sanar wa suwaiba ,dubu goma ya bata yace ko da zata bukaci wani abu bayan tafiyarsa,sa'anan idan dubu goman be isheta ba,ta iske inno,idan ma wata matsala ce ta iske inno.
Washe gari yazo sashenta yi mata ssllama,yauma kwance ya tarar da ita,ya girgiza kai tare da kuntsa kansa cikin dakin.
"Kayan tea  na kitchen na sayo,ki hada tea ki sha,ni kam na tafi.
ta mike tare da yimasa a dawo lafiya..
Tir da wannan irin matar,ko irin rakiyan nan babu...ya fada a ransa.
Read More »

Thursday 15 February 2018

KAZAMA CE MATA TA 4

πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
*KAZAMA CE MATA TA*
             πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
  Written by Ganarious.
Page4

√ *NAZIHA YARIMA✌🏼*
√ *HIDAYAT ABIODUN*,.ONE love shall keep us together.

√jinjina ga yar'uwa *HADIZA GANA*

         **        **        **
Tun bayan da ya baro gurinta yake tunanin suwaiba ba irin macen ds ya ke so bane...qualitiez din da ke bashi sha'awa a mata ma, ta rasa su ko daya bata dashi.
   ...tsuki yayi"inna na neman ruguzamin farin cikin da nake hange a rayuwata.

Sai da engr.munir ya dauki tsawon lokaci, sa'anan ya sake zuwa gunta.....wannan karon shi kadai ya tafi.
Yau ma kamar ranar farko....shanya shi tayi,sabida ta dade bata fito ba,har ransa ya baci,yana tunanin ya tafi sai ga ta ta fito.
Gefen windon sa ta zo tare da kwankwasa masa gilashin,ya sauke gilashin yana me kallonya..."zagaya ta can,ki shiga gaban mota,
Allah ya taimake ta ta iya bude murfin,motan😜..tana zama ta buga kofan da karfi wai ita nan ta rufe murfin motan.
Ta dubeshi tare da gaida shi,shima din ya amsa yana me kallonta.

Gaba dayan motan ta dauki warin hayaki...sai rayawa yake a ransa wannan wata irin yarinyace haka me halin * "ko'in'kula...ko irin kwas kwariman da yan mata sukeyi idan zasu fita ta'di,ba tayi.

Maganar tace ya dawo dashi da'ga duniyar tunanin da ya tsunduma.
"Mahaifina  yace na fa'da maka ka turo iyayenka sabida nan da wata biyu za'a yi bukin kanwata kuma yana son ya hada da nawa.
Sai da ga'ban sa yayi ras...jin maganarta,shiru yayi na dan lokaci sa'annan yace 'toh naji...ya sake yin shiru na dan lokaci sai kuma ya dube ta "miyesa baki sa turare ne?...
Juyowa tayi tana dubansa....tau kaka kake son nayi,tinda bani da shi?
Amman ai na baki kudi ki saya ko?
Eh....walla kudin nan abubuwa dayawa munkai dasu.,ta murmusa sanna  ta cigaba da fadin idan nace zani lissafa maka abinda munkai da kudi,duhu zai cimmana,ba tareda na gama fado su ba.
Yayi ajiyar zuciya yace "ni me son turare ne,idan kuma kina son mu shirya dake ki dunga sanya turare kuma ki zamto me jin magana.
Tau na ji'yah...zan duba ko zani samu ko da ta dari ce,ko ta dari da hamsin.
Jin takaicin ta yasa son barin gurin,don haka yayi mata sallama ba shiri.....dubu daya ya ciro ya mika mata "gashi ki sayi turaren"
Farin ciki ta shigayi,tare da yin godiya.
"A gaskiya idan na sake zuwa,ban ji kamshin turare ba raina zai baci..
"Innshaa'Allahu ka gama jin kamshin turaren....

Gidansu inno ya nufa bayan yabar gurin suwaiba..
Ya sanar da ita sakon mahaifin suwaiba,da ta fadamasa.
Inni cikin wage baki tace "toh toh madallah, ka gan kenan lokaci kadan ya rage, sai ka kasance cikin shiri..ka kuma bada abinda ya saukaka don a sayi kayan laifeh..
Tau inno, gobe inn'shaa'Allahu zani kawo kudin afara sayayya.
Yayi mata sallama sannan ya nufi gidan kanwarsa khadija.

Ya sanar mata komai game da zancen suwaiba,da kuma yanda sukayi da inno.

"Kenan ka amince da auren yarinyar nan?...cikin ba'ta fuska take maganar.
Kai ya girgiza...tau yaya kike son nayi?kin fi kowa sanin inno,rashin amincewa ta da hakan ma zai zama mani wani salon tashin hankali ne,gwara hakan dai.

Ya ta'be baki..."ni gaskiya da baka amince ba".
Sai a lokacin alhaji suleiman da ke zaune yana sauraronsu ya sanya baki.
"Shawaran da zani baka shike ka yawaita addu'oi,sallalo akan Allah shi zaban maka alkhairi,idan kuma babu alkhairi a tattare da aurennan,koda kuwa kwana daya ko sekan daya ya rage a daura,Allah shi ruguza shi ko ya kawo sanadi...
Shawarwari me karfafa gwiwa alhaji suleiman ya dunga bawa engr. Munir da'ga nan aka shiga hiran duniya.
Suna tsaka da hiran khadija da dauko zancen kayan le'fe..." gaskiya yaa  munir karka baiwa inno kudin kayan nan,ka bani kawai naje kasuwa na siyo,idan na saya sai na kaimata...na san inno sarai da shegen son kudin nan nata.
"Ah'ah kar kuyi haka,yin haka zai kawo maku abinda kuke gudan ma,idan har bata sayi abin kirki ba ko ta danne kudin kanta tayiwa...wataran ka sayiwa matan idan har ita din yar' kirki ce...fadin alhaji suleiman...da haka yayi masu sallama ya tafi gidansa.

Kudi masu yawan gaske ya baiwa inno.da na kayan le'fe, da kuma na kayan miya kamar su curry da thyme da za'a yi anfani da su lokacin buki.
Ya baiwa baban sa wasu kudaden da ya gyara inda ke bukatan gyara agidan,duk da sanin cewan babu.ya kuma bashi kudin abinci da za'a ci lokacin buki.

Shima din engr.ya kara gyaran gidan sa,duk da ba wani gyara gidan ke bukata ba,sai part din amaryansa da ya canzawa fenti.

Shiri ya kankama!...ranar daurin aure kawai ake jira,domin kuwa saura kwana uku kacal.
sai dai....gwamnatin jiha,ta umurni engr.munir da ya tafi jihar potakot domin setin wasu injinaye da aka shigo dasu.
engr munir ya nemi alfarma da su bashi kwana daya,bayan daurin aurensa....dalilinsa kuwa shine hangen abinda zai faru idan bai tsaya anyi daurin auren da shi ba,sanin inno da yayi da rashin fahimatr mutun.

Yau jumma'a,bayan sallar  jumma'a aka daura auren  engr. MUNIR & SUWAIBAH,...taro yayi taro domin kuwa makil gurin daurin auren yake da mutane....
engr. Munir me jama'a, abokan sa na social media wadanda bai taba gani ba sun zo,wadanda yayi karatu dasu, da wadanda sukayi yarantaka duk sun halarci daurin auren.
Yan mata ko, ba'a ce wa komai,sabida ko wace ta kasance cikin domin jiran  ko za'ayi dinning ko wani abu da zai sa matar engr. Munir ta zo,sabida suna son ganin wace ce wannan me farin kafan...sai kash, ba abinda aka shirya bayan daurin aure,amarya kuwa ko walima batayi ba..

Taro ya watse...amarya ta tafi gidanta, dangi da yan uwa gami da kawayenta da suka raka amarya gidanta sai santin gidan suke suna rayawa a ransu "da ma nice aka kawo nan, "da nicr na sami irin gidan nan" da dai sauransu...kowa sai tofa albarkacin bakinsa yakai,tare da yimata gargadin da kar tayi sakacin abinda zai sa wannan gidan ya sub'ce mata..
Da haka suka watse, suwaiba ta zama super star a cikin dangi,karkaf din danginsu,ta wajen baba da mama, babu me kwatankwacin irin gidan suwaiba...asalima ta kowani bangaren talakawane na hakika.
Amarya kadai aka bari,a yayinda ango ke waje da abokansa.
sai goma da rabi sukayiwa juna sallama,suka tafi shi kuma ya shigo cikin gida.
Ya rufe kofofi da winduna,sannan ya kashe fitilu...har ya kai dakinsa,sai kuma ya tuna fa yau bashi kadai ne a gidan ba fa.
ya karkada kai'a ransa yana fadin ko irin zullumin nan da angeaye suke yi shi baiyi ba,sabida sam sam yarinyan bata birge shi balle ta bashi sha'awa.

Hanyar sashenta ya nufa,ganin folonta empty ya bashi mamaki,ba kujeru balle t.v da sauran ababen ado,nan ma girgiza kai yayi, ya nufi dakinta..bude ya yarar da kofan a yayinda fitilun dakin ke a kune.
Kwance take bisa madaidaicin katifa,wanda ko zanin gado ba'a shimfida masa ba,sai ledan da katifan tazo dashi..da alama tayi nisa a barcin.
Da'ga bakin kofan yake kallonta, a ransa kuwa fadin yake wannan wace iri ce!...kayan jikinta ma bata cire ba,balle ta shimfidawa katifan bedsheet....wata kila ma wanka bata yi ba.
ya da'ga kafada yana fadin"anyway wannan ya rage gareta.
Ya kashe wutan,tare da jan kofan ya rufe.
Ya nufi dakinsa.
Read More »

Tuesday 13 February 2018

SOYAYYARMU 36

SOYAYYAR MUπŸ‘«
      By Ganarious.
Page 3⃣6⃣

        **       **         **
Mahaifin haj. Zubaida bashi da aiki sai tsinewa Alhaji Buba, ya na me da na sanin shigowarsa a rayuwar sa.
      Yan sanda ko na aikinsu na horansu,akan su fiddo takkardun.
Bincike ya nuna masu lallai takardun na hannunsu..
Mahaifin haj. Zubaida ya shaidawa Alhaji Buba da cewan da zarar sun fita daga nan kurkutun,tau za shi raba auren Alhaji Buba da na yar sa,ba shi ba,hatta abinda duk ya mallaka Alhaji Buba da yan uwansa,yana son a maida masa..

Mahaifiyar haj zubaida ce zaune tayi tagumi,abin duniyar duk ya sha mata kai, ya chikwikwiya mata..a yayin da ita kuma haj. Zubaida ke zaune gefen ta tana surutan ta.

Mama!...haj. zubaida tayi kiran uwar.
Ta juyo,ta dube ta ba tare da tace wani abu ba.

Gaskiya ki zo mu tafi gun bokan ki na nijar yayi mana aiki, duk wanda ya sace takardun nan ya maido su.
Mmmmmhhhh...haka ne fahhh,kinyi gaskiya.tunanin haka bai zo min ba,da ba'a tafi da mahaifin ki ba.

Me zai hana muje gobe?
Shikenan,muje gobe din...zuwa anjima zani je nayi mata shatan private jet.
Hajiya tayi murmushi "bazan kyale wannan barawon ba,wallahi sai na sanyawa ko wanene gu'ba ya sha"

Washegari sun shirya suna zaman jiran lokaci.karfe 12:00pm jirgin su zaya tashi wanda zai kai su har inda za su tafi,ya kuma dawo da su.
Hajiya zubaida ke fadawa mahaifin ta irin wulakanci da tozarci da zatayi wa duk wanda ya saci takardun nan....
....hayaniyar da suke jiyo wa daga wajen gate ya sa ta dakatar da maganarta,sun dan saurara "kamar muryan mace ki? Hajiya zubaida ta fada,a yayin da ita kuma mahaifiyarta ta kasa kunne ta ji da kyau..
Me gadi da ne fa nake tunanin yana sa'in sa da wata.
Mahaifiyar haj. ZUbaida tayi kiran me aikinta tare da umurtan ta da ta tafi bakin gate ta dubo abinda ke faruwa anan.

Jim kadan me aikin ta dawo" wata mata ce megadi ya hana ta shigowa shine suke sa'insa.
Ta mike ta fita zuwa bakin gate din....ta tadda matar tayi dammara,sai kokawa takeyi da me gadin...tsawa tayiwa me gadi ayayin da take kokarin raba su da hannunta...
..."bakubda hankali ne"..ko mahaukata ne ku??.
Matar da da'ga mata hannu,cikin tsiwa tace "bashi da hankali dai,mahaukacin megadin  da kuka ajiye..wallahi sai na koya masa darasin da bazai manta ba a rayuwa,tunda kaki ka sauri ko ni wacece,balle ka san matsayi ga me gidanka.
    Ganin fitsara da rashin kunyar matar ya sanya mahaifiyar haj. Zubaida yin shiru,sai bin ta take da ido,tana me mamakin dalilin zuwan mahaukaciyar nan gidanta.
Hajiya zubaida cevta iso cikin takama da isa.
"Kehh kehh kehh...ta fada a yayinda take dakatar da matar.
A wulakance ta dubeta da samanta zuwa kasa ta watsar...."mahaukaciyan ina ne ke,da zaki zo gidan mutane kina hauka?.

Kehh zubaida...matar ta fada cikin da'ga murya, ayayin da kuma take nunin haj.zubaida da yatsan ta.
   "Ni kike kira da mahaukaciya?!.toh ki sani watarana sai kinyi da kin sanin fadin haka don sai na tabbatar kinyi haukan nan da kika min kirari da shi.....wannan gidan da uban da kike takama dashi na baki aronshi ne na dan lokaci domin kuwa ni da yarana zamu kwaci incinmu nan ba da dadewa ba.
Ta cire dammara daga kugunvta,ta dubi mahaifiyar haj. Zubaida da take a daburce
"Na zo dubiyan uban ya'yana ne sabida kwana biyu naji sa shiru,da fatan ba mutuwa yayi ba....idan ko haka ne ,tozarci ta riske ku,domin kuwa sai na wulakanta ku yanda baku ta'ba zato ba.

Ta juya ta fara tafiyarta,a guje mahaifiyar haj. Zubaida ta bi bayanta tareda chakume ta,tana fadin "sai kin fada min hadin ki da me gida na".
Tureta ta yi da karfinta,domin kuwa saura kiris ta sha ka'sa..."kina son sanin hadi na da shi?...idan ma tafiya yayi,in ya dawo kin tambaye shi yaran sa faisal,farid da aminu da ya boye a garin Gombe...da'ga nan bata kara ba,tayi tafiyarta.
Mutuwar tsaye mahaifiyat haj. Zubaida tayi,da kyar haj. Zubaida ta shawo kanta sa'anan suka shiga cikin gida.
Tana zaunar da ita ta fashe da kuka tana me zagin me gidan ta hadi da tsine masa.

11:34am haj. Zubaida ta umurci mahaifiyarta da ta tashi su tafi airpot,sabida tafiyarsu ta zuwa nijar din.

Hawaye ta share.."wa? Allah shi sauwwaka naje nijar sabida macucin nan,sun dade  basu rike shi a can din ba.
Haba mama...haj.zubaida ta fada a yayida ta maida fuskarta na tausayi.
Wallahi ba inda zani je....sayar da komai nasa zani yi kafin ya fito,don bazani tashi a tutan babu ba, sabida ya sami ma'ga da.

Haba mama...karyiwa babana haka mana...!da'ga jin maganar wannan matar ko nace mahaukaciya sai ki dauki zafi kina zargin mijin ki.

Ba wani nan...wallahi maganar ta akwai kamshin gaskiya.
Hajiya zubaida ta kara marairacewa tana me bawa mamarta hakuri sai kam tayi nisa domin kuwa baza taji kira ba,balle ta saurare ta.

         **         **      **
   A gidan baba yusuf akayi taro,domin yin shawarwari yanda zasu bulowa al'amarin da ke faruwa a wannan familin.
Gaba dayan su sun hallara,su kuma tattauna akan al'amarin Alhaji buba da ke tsare a kurkutu.
Mafitan dai guda daya ce shine kuma addu'a,abinda kawai suka yanke kenan,su dinga yi masa addu'a har Allah ya fidashi da'ga nan.
bayan sun gama shawarwarin Hisham ya fada masu da su bar masa komai, inn'shaa'Allah zaiyi kokari ya gan cewa komai ya dawo dai-dai...
wata zuciyar ta raya mas da ya fada masu su je su baiwa mamee hakuri watAkila hakkinta ne ya kama baba buba..da sauri yace wa zuciyarsa a'a.
a karshe ya shaida masu zaya je lagos cikin satin nan don dubo baba Buba.

kai da komawa yake yiyana me cizon yatsan sa.
kaseem da kareem kuwa sai binsa suke da ido,ganin bashi niyar natsuwa ya sanya kaseem riko shi ya zaunar.
"na fada maka yanda zaka kawo karshe wannan halin da kuke ciki?
Kai ya dago ya dubi kaseem din,ba tare da ya amsa ba ya mayar da kansa.
"Ka amsa ni ma'nah...shin kana son kawo karshen wannan kuncin da kai da yan uwanka kuke ciki.
Kai ya da'ga yana m kallon kaseem din.
..."toh ga shawara,amman fa duk abinda na fada zakayi ba gardama.
Ido kawai ya sawa kaseem.
"Zuwa zakayi gun mahaifiyar ilham din, ka bayyana mata komai,ka fada mata halin ilham..ka fadamata abinda ilham keyi da kuma wanda take shirin yi..ka fadamata ilham is behind the anxiety and difficulty ur families a facing...ka roke ta da Allah da annabi da ta hana ilham abinda take yi,hakan zai sa komai ya zo karshe,domin kuwa ita kadai nake ganin zata hana ilham daukan wannan act din.

Gaskiya na goyi bayan shawaranka...hakan kuwa ya kama kayi hisham,sabida ita kadai ce zata iya stopping ilham da aiwatar da kudirinta....fadin kareem
Hisham ya yi ajiyan zuciya..."thank all for your support, inn'shaa'Allah zanyi yanda kuka fada amman sai dawo da'ga lagos .
Karfe bakwai da yammacin ranar su kareem suka yi masa rakiya zuwa airpot,sun kuma shaida masa gobe zai iske su anan din don tarbonsa.
Hotel hisham ya kama,sabida bashi da dangi a lagos sai dai abokansa da suka yi karatu tare...don haka anan ya kwana.

Mintuna goma sha biyar suka bawa Hisham don ganawa da alhaji buba.
Yan sanda biyu suka fito da alhaji buba,sun rako shi har inda aka tanadar domin baki masu zuwa.
Hisham na hangen sa ya tsira masa ido har sai da suka kusankaraso wa gunsa,sanan ya tashi ya rungume alhaji buba cikin murna.
Suna zama ya hangi ta'bo a fuskarsa,ya duba da kyau.."baba karfe wuta suka na'na maka a fuska?
murmushi yay tare da kama hannun Hisham.."ya ya kake,ya ya mutanen gida?..da fatan ba abinda ya same su ko? Duk lafiyar su kalau ko?

Hawayene suka zubo bisa kuncin Hisham,ya sa hannuya share yace "kowa lafiya lau baba..! Suna kuma gaida ka...da fatan basu horonka ko?

Girgiza kai yayi,kar ka damu da wannan..ina muhammad kanin ilham?
Lafiyansa kalau baba..
Ina gaida  shi sosai sosai idan ka koma.
Shiru hisham yayi...daga bisani,yace "baba ko na wakilce ka,na baia mahaifiyar ilham hakuri?..watakila za'a samu sassauci ga wannan al'amarin.

Kai ya sake girgizawa,"kar ka damu ,idsn Allah yasa na fito,zamu tattauna akan wannan.
..suna baka abinci yanda ya kamata kuwa?....hisham ya nemi sani.
Murmushi yayi ya da'ga kai,zaiyi magana masu tsaronsa suka tada shi,lokaci yayi.
Rike hannunsa Hisham yayi yana me hawaye.."baba zanyi kokari na fidda ka da'ga nan.
Murmushi kawai yakeyi wa Hisham a yayinda ake turashi...ya juyo yacewa Hisham da ya fadawa yan uwa su daina sawa kansu damuwa akansa.

Hisham ya fito gidan kurkutu yana me hawaye...
Bai ta'ba jin a ransa yana jin haushi ko takaicin ilham ba kamar ta yau. Ji yake kamar ace tana kusa ya shaketa....wayarsa ya ciro tare da nemo lambarta.ya rubuta mata sako kamar haka *your iman is weak,i do wish you could see how terrible and horible your actions turns ur onw father*...ya tura sakon tare da maida wayarsa cikin aljihunsa.
Ya tari taxi,yayi shatanta zuwa airport.
Yana isa airport sako ya shigo wayarsa, ilham ce ta maida masa martani kamar haka *oh my Goodness,it's a pity u just got to know that.i also wish u could feel or imagine the situation my mum went truu years back,which result of her loosing a wonderful mother*...a sanyaye ya maida wayarsa cikin aljihun wandasa.ya karasa cikin airport din.

Kareem da kaseem ne suka zo tarban sa as usual.
Ganin yanayinsa yasa basu ce masa komai...
A hanyar su ta zuwa gidan mamee kareem ya hangeshi ta madubi yana sharan hawaye,ya tausaya masa kwarai da gaske.

Suna isa gidan mamee ana kiran mangariba.a waje sukayi parkin,ba tare da sun shiga cikin gida ba,domin kuwa me gadi ya shaida masu mamee bata dawo ba,amman yana da tabbacin duk inda take yanzun yana hanyar dawowa gida,sabida mangariba baya riskanta a waje.
Sun tambayi me gadi ko da masallaci kusa ,yayi masu nuni da masallacin suka tafi.
Bayan sun dawo sallan mangariba me gadi ya yayi masu izini da su shiga domin mamee ya dawo kuma ya sanar da ita zuwan nasu
Har sunyi nisa,sai kuma Hisham ya dawo baya gun me gadi
"Don Allah idan baza ka damu ba inason nayi maka wata tanbaya
Megadi yayi murmushi yace 'a'a badamuwa,Allah yasa na san amsar tanbayat'
" ilham na ciki?
ah'ah..tayi tafiya jiya.
ALHAMdulillah .....ya fada,yayiwa me gadi godiya sannan ya riske su kareem suka karasa falo.
 
Mamee ta dauki tsawon lokaci bata fito ba.
Sai dai me..!
Ta fito ne rike da tire a hannu,blessin na biye da ita a baya,itama din rike da tire a hannunta,a saman dining table suka ajiye sannan mamee ta umurce su da su taso suci abinci.
kin tashi sukayi,har sai da ta sake magana a karo na biyu.
A kunyance  suka mike zuwa gun dining table din.
ta zubawa kowa nasa a plate,tare da fadin bisimilan ku ko?
kareem da kaseem sunyi *bismillahir.....* suka fara ci,don daman suna tare da yunwa.
ganin shi Hisham din bashi da niyar cin abincin ya sanya tayimasa magana.
"Kiyi hakuri mamee,bani da appetite, bani iya cin abinci
😳 waje mamee tace  sabida me?

"Wallahi mamee ina cikin damuwa,dalilinkenan da ya kawoni nan ki taimaka min ,domin kuwa ke kadai ce zaki iya magance mani matsalata....
Kafin ta yi magana,ya mike,taku biyu yayi zuwa gefenta ya durkusa gwiwowinsa kasa.

"Pls and pls mamee ki yarda da duk abinda zani fada maki,kar ki dauka maganar shirme ce.
Kallonsa kawai take yi,batare da ta ce wani abu ba.
Kamar yanda kika fada *SOYAYYARMU*da ilham al'amarin  abu ne da Allah ya kirkira.Allah kuma yasa kinsan da hakan,a duniyar nan bayan ke,duk wanda ke son ilham a bayana yake,inason ilham wanda shike bazani iya kwatanta soyayyar da nake mata ba...haka kuma na santa kamar yanda nake sonta, i'm sorry to say this,mame yanda na san ilham baki santa haka ba...nasan abinda zata aikata da wanda baza ta aikata ba.
πŸ˜”Shiru yayi na dan lokaci sannan yaci gaba "nasan iyayena sun sa'ba maki,sun kuma cancanci ko wata irin hukunci,sai dai ganin wannan tsa-tsauran hukuncin da suke fuskanta ko nace suke shirin fuskanta ya ta'ba min zuciya...jini kenan.
Don Allah mamee ki yafe wa iyayena,hskan zai sa ilham ta yafe masuta kuma sassauta masu.

KALLOnsa kawai takeyi,tana me sauraronsa.
idanun sa sunyi jajir,sunyi taf da hawaye kiris ya rage su sakko.
"Daga lagos nake,naje dubiyan Baba Buba,wanda yau watansa daya da kwana hudu kenan a gidan kurkutu...ya share hawayen da suka sakko ya dubi mamee yace "Baba babu nacikin wani hali,tsorona kada ciwon zuciya ya kamashi, azaba iri iri suke horonsa da shi acan akan laifin da baiyi ba..
ya dakata da maganar sa.,ya ciro wayarsa.
ya budo sakonin ilham da tayi masa.
ya mika mata wayat tare da fadin don Allah mamee ki yarda dani.
ta maida masa da wayarsa bayan ta gama karantawa.
"Ilham tayi alkawarin duk wadanda suka sa'ba maki a baya sai ta tabbatar sun dan'dani kunci fiye da naki..
na kasa bacci sabida tace mutun biyu da zai tafi kurkutun,ba zai dawo ba iya tsawon rayuwarsa.

Shiru yayi na dan lokaci,itama shirun tayi..."don allah mamee ki taimaka min,ke kadai ce zaki hanata..iyayena da dangina suna cikin wani hali,sun rasa farin cikin su,na san nayi son kai da neman wannan alfarman,alhalin abinda ya dace da su kenan,amma na kasa jurewa na kau da kai akan halin da suke ciki.
don allah ki yarda dani,ilhamce a bayan duk abinda ke faruwa .

Gyaran murya tayi,ta umurci hisham da ya koma saman kujera.
BAYAN ya zauna ta yi nuni da plate din dake gaban sa tareda fadin 'ci abincinka,kafin yayi sanyi.
Kiyi hakuri mamee wallahi duk yanda naso cin abincin bana iyawa.
Mikewa tayi ta dawo kusa dashi ta shuga bashi abincin a baki....tana tsaka da bashi abincin abba ya shigo a guje.
runguman Hisham yayi ta bayansa.
Hisham yasa hannu ya riko shi,tare da dawowa dashi gabansa suna fuskantar juna.."kayi fushi dani ko?
Eh nayi,amman ganinka yanzun yasa na hakura na daina fushin.
☺thanks...hisham ya fada

Yauwa uncle hisham yau zamuje gidan nan ko?...sabida nayi mafarki da mutumin nan wai ya kone a fuska.
hisham cikin mamaki ya ta'ba masa kuci.."ai mutumin nan yayi tafiya,amman kafin ya tafi,yabar sakon gaisuwa zuwa gareka.
Cikin bata fuska abba ya koma gefen mamee ya zauna.
Mamee ta cigaba da baiwa hisham abincin,
...."laaahh ,ka gode anty bata nan da tace kato da kai ake bawa abinci a baki.
Kaseem da kareem dsi yan kallo ne,domin kuwa sun gama cin abincin su tu da dadewa.
sai da abinci ya kare a plate din sannan mamee ta sarara masa...tayi masa alkawari komai zai dawo masu dai-dai inn'shaa'Allah,don haka ya daina damun kansa.

Daga gidan mamee gidan kakansa baba lamido ya nufa,ya shaida masu komai ya kusan zuwa karshe da yardan Allah.
Read More »

Friday 9 February 2018

Page 35 of Soyayyarmu

SOYAYYARMU πŸ‘«
     By Ganarious.
Page3⃣5⃣

πŸ’žso da kauna ga mutan *Kenya nairobi*πŸ’ž
.         **         **        **
Mahaifin haj. Zubaida zaune,yana yi wa bokansa bayani rai a bace..sai huci yake.
Yayi masu bayani cewan ya tarar da surukinsa ya ba'tar da takkardun kanfanin da aka aiko.
Bayan sun gama sauraronsa,daya daga cikin su yayi mass jajen kudinsa da ya aika,ya kuma bada shawaran da ya ajiye surutaka a gefe,ya matsawa Alhaji buba ya fito da takardun.
sauran mutanen sun goyi bayan shawaransa.
Alhaji Buba da ke zaune cikinsu yayi gyaran murya yace "wallahi sace takardun akayi'
Tsawa mahaifin haj. Zubaida yayi masa..ya shiga zaginsa yana fadin "macuci kawai,na dade da samun labarin cutar dani da kakeyi sabida kana son ka mallaki dukiyoyi na ta wata hanya ko!..yan uwan duk ka sayan su hanyar sace min dukiya,ko kana tunanin banda masaniyar haka ne....toh wallahi wannan karo kam,ba zaka tsira ba matsayaci kawai.
Talakan banza...idan ta kama zani raba aurenka da diyata.
Kuma na baka yau zuwa jibi ka fito da takardun nan,idan ba haka ba  ko!..duk abin da ya biyo baya kai ka saya..don sai na sa an rufemin karkakaf din matsiyatan dangin nan naka,hatta jariri bazani sarara masa ba.

Alhaji Buba ya koma gida yana me jin zafin cin mutuncin da surukin sa yayi masa..
Ko kadan baya san abinda za 'a ciwa dangun sa zarafi balantana akai ga wulakantasu.
  Hajiya zubaida ne ta zo kusa dashi ta zauna,tana me bashi baki akan ya kwantar da hankalinsa za'a gan takardun.

      **       **       **
Hisham zaune tare da su kareem.
Kaseem ya dube shi yace "daga jiya zuwa yau ka faa'da.
Hmmmm...ba dole ba! Idan ma akace ina dauke da ciwon zuciya,ba zani mu'sa ba,wallahi na shiga damuwa sosai,yau fa saura kwana biyu sati biyun da ilham ta kudirta ya cika.
Kamanta mamarta ta tabbatar mana ba abin dai faru?

Hmmm...zuciya ta,ta ki amincewa da haka...ilham sai ya aikata.
Kareem yayi ajiyar zuciya yace ka kwantar da hankalinka guy! Mu bari zuwa jibi tukun
Gaskiya ka kwantar da hankalinka..ka gan yanda ka koma kuwa.
Ya taba kuncinsa yace "ai dole na rame ko don auren dole da suke sonyi min.
Dariya sukayimasa....suna fadin wasa daiiii.
Wasa???.....idan baku sani ba,yanzun ku sani har sun sa ranar auren nan da wata biyu.
Idanuwa waje suke ce yaushe  akayi haka?
Ranar da kuka kai ni gidan,daman kiran da sukeyi min kenan.

Tabdijam....da basuyi maka adalci ba gaskiya.
Lokaci ya kai da mahaifin haj. Zubaida ya diban ma Alhaji Buba,kuma ba alamun ganin takardun.

TUnda bayan dawowansa daga masallaci ya kasa samun natsuwa,sai addu'a yake Allah shi fisshe shi daga wannan tozarcin dake shirin afkuwa masa.
Karfe takwas dai dai,me gadi ya buga masu kofa.
Hajiya zubaida ce ta tafi bude kofsn...a yanda ta gan fuskan me gadi ta fahimci ba lafiya.
CIKin tashin hankali yace hajiya ga yan sanda can kofan gida fa.
Batayi mamaki ba, domin kuwa mahaifin ta ya sanar ma ta abunda zai biyo baya idan har Alhaji buba be kawo takardun ba.
Tana tsaye gurin ya karaso,shima din baiyi mamaki ba,domin kuwa da shirin sa yake.
Ya shiga daki ya chanzo kaya,ya dawo gun hajiya zubaids yana me neman alfarma da ta rokan masa mahaifinta kar ya ta'ba masa yan'uwa.
Ta rike shi gam...ba inda zaka tafi,yana jan hannunsa tana ja itama..
Suna cikin haka yansanda suka shigo..tureta suka yi sa'anan sukatafi dashi.

Mahaifin haj. Zubaids ya bada umurni da su horeshi har sai ya fadi inda takardun suke...kudi masu yawa ya bawa yan sanda,sun ji dadin haka sabida haka suka shiga gallaza masa azaba iri-iri.
Ssi da yayi kwana uku a hannun yan sanda sa'anan hajiya zubaida ta sanarwa yan uwansa.

Nan da nan labari ya kai kunnensu gabaki daya,ciki harda Hisham.
sun shiga tashin hankali marar misaltuwa sabida sakon da mahaifin hajiya zubaida ya aiko masu da su kasance cikin shiri,mudin Alhaji buba bai fidda takardun ba,toh ko jariri ba zaya ragawa ba.

Hisham ya shiga tashin hankali,ya rikice,ya rude...ba abinda ke fito wa abakinsa sai"ilham y..ilham why..
WAyar sa ya dauka yayi kiran kaseem da kareem.
Cikin dishewan murya yace kudirin ilham ya tabbata..haka kawai ya fada masu ya ajiye wayar.
Ba'a dauki tsawon lokaci ba suka iso.
Nan ya shaida masu abinda ke faruwa.
Mamaki suke...abinda ya daure masu kai, shine mahaifinta da ta fara dashi.

🀦🏻‍♂dafe goshi hisham yayi.."washh washhh..
a hanzarce suka matso gab dashi,suna tambayar lafiya?
Ya rike hannun kareem,ya ce jiri nake gani,gashi kaina na barazanar fashewa.

Ba su tsaya tunanin wani abuba,sun kamashi zuwa gun mota,daga nan suka nufi asibiti da shi.
Likita ya gama gwaje gwajensa ya dawo gare su.
YA shaida masu jinin sa ne ke son hawa...kuma ina me baku shawara da ku fadamasa ya rage tunane tunane.,ya kuma dunga samun isasshen baci
a ranar likita ya sallame su,ya kuma basu maganin da hisham zai dunga hadiya.

A hanyar su ta komawa yace wa kaseem su kaishi gidan baba Lamidi(kakansa)..domin sanin halinda suke ciki.

YA tarar da iyayensa da yan'uwa anyi chirko chirko, kamar an aiko masu mutuwa..nan ya shiga tausaya masu..
Hisham mutumine da Allah ya hallici ce shi da wani abu wai tausayi...
Ya nemi sanin police station din da aka tsare Alhaji Buba,
Ko ka tafi baza su bari ka ganshi ba fadin baba lamido.

TAFe suke akan hanyarsu ta maida hisham gida..kaseem ya nisa "yanzun menene abinyi?
A fusa ce kareem yace kawai a sanar wa mahaifin hajiya zubaida cewan su tuhumi ilham domin kuwa itace sanadin komai.
Kana ganin haka zai yi?...fadin kaseem
Me zai hana.
Tau ai ba wata kwararriya shaidan da zai nuna cewan itace ta aikata haka.
mu dai gwada yi haka don ceto bawan Allah,don da Alam wannan ilham din bata da imani.
har cikin ransa yaji furucin kareem,amman ya daure.

KASeem ya nisa yace mudai bita a hankali,domin kuwa wace zata iya aikata wannan abun komai ma tana iya wa kenan..

Suna kaiwa gidan hisham sakon text message ya shigo wayarsa.ganin ilham ce yasa shi saurin budewa jiki na rawa.
"Next person" shine kawai abinda ta rubuto masa.
Ya da'fe kirjinsa tare da jingina jikinsa a motan.
ganin haka yasa kaseem karasowa da sauri ya rike shi.
YA AMshi wayar ya karanta abunda ke a rubuce.
Da taimakon su hisham ya karasa falonsa.
 Zama sukayi,bayan sun zaunar dashi.
Gaskiya ya kamata ka sanarwa iyaye da yan uwanka abinda ke faruwa.
Ya fahimci qbinda kaseem ke nufi da haka,ya girgiza kai yace " soyayyar da nake yiwa ilham ya wuci haka...babban kuskurene sanar da su abinda ilham ke yi akansu..

So kake a kyaleta ta cigaba da saku cikin kunci?.
Kuyi hakuri,inn shaa'Allah zuwa gobe i will come up with a plan,yanda zamu dakatar da ita.
A ranar da alhaji buba ya cika sati,mahaifi haj. Zubaida ya baiwa yansanda cin hanci da su kamo baba yusuf su tsare shu,wata kila ba zai  rasa sanin inda takardun yake ba.
Hankula sun kara tashi,sai jeren giyan zuwa gidan mahaifin haj. ZUBAida suke,domin bashi hakuri da neman afuwa.
yayiwa megadi kashedi akan kar ya sake barin su shiganmasa gida,sai dai idan da takardu suka zo.

WASA wasa har Alhaji buba yayi satibiyu a gidan kurkutu.
Mahaifin haj. Zubaida zaune yana banbami wai alhaji buba ya ki fitowa da takardun,matarsa kuwa sai lallaminsa takeyi...suna tsaka da haka yan sanda tareda airforce suka faso cikin falon.
Ganin ka'ten maza yasa su jin tsoro.
Takarda suka ciro,suka bude tareda nunawa mahaifin haj. Zubaida.
Wannan warrant ne da ya bamu daman kama ka,akan laifin  amsan takardan kanfani ba tare da sa hannun me shi ba..
Embassy na japan dake wakiltansu a nan najeria,da kuma shugaban airfoce suka sa hannu domin a tafi da kai.
Babban police headikwata na birnin tarayya aka tafi da shi.
sun sanar dashi laifinsa shine amincewa tayi da kuma karban takardun da aka sato alhalin me kanfanin bashi da masaniyar haka.

Mamaki sosai yayi jin cewan me kanfanin na raye...yayi Allah shi waddai da rashin binciken da baiyi ba.
ya sanar da yansanda daga farko har izuwa halin da suke ciki na bacewan takardun...nan babban ogan yan sanda ya sa aka taho masa da Alhaji buba
Tambayoyi yayi masa daga nan yasa aka tafi da su kurkutun garin lagos kafin su gama bincike a shigar da kara kotu.
Hajiya zubaida ta shiga rudani, gashi da alama karamar hauka ta kamata.surutai kawai take,..sai fadin take mutane biyun da ta fiso a duniya ake shirin rabata dasu.
Nan da nan gari ya dau gulmace gulmace da labarai akan zance mahaifin haj. Zubaida da mijinta.
Read More »

Thursday 8 February 2018

SOYAYYARMU 34

*SOYAYYAR MUπŸ‘«*
         By Ganarious.
Page 3⃣4⃣

DOMIN KI *Nazhee yareema*πŸ˜ƒ...Babban abokiyar ilham.

Labarin *KAZAMACE MATATA* na nan a ganarious.blogspot.com/
Kar ku bari a baku labari.

Gaisuwa ga masu karatun *SOYAYYARMU*,Kuyi hakuri da kurakuren da typing errors da labarin ya kunsa.🀞🏼

         **       **         **
Ya jingina jikinsa da motan.
Hajiya zubaidah ta karaso gunsa tana taba shi ya sulale kasa.
   Ta shiga cikin gida a guje tayi kiran me gadi.
Da taimakon mai gadin,suka shigar da alhaji Buba wanda yake a sume.

Yana farfadowa ya fara surutai.
Hajiya cikin damuwa take fadin 'ka kwantar da hankalinka,da yardan Allah za'a gan takardun..
Ya dube ta cikin ido,yace me kike fadi?.
Nan ta sake maimaita masa abinda ta fada.
Ajuyar zuciya yayi,ba tareda yace mata komai ba.

Karee da kaseem ne a mota.
Kaseem ne matukin,kareem ya nisa yace ya kamata mu dubo Hisham,mu san halinda yake ciki,domin kuwa saura kwana hudu kacal ilham ta aiwatar da alkawarin ta..
Hummmm....wallahi,nima abin ya dame ni.gashi duk mun kasa samun mafita...fadin kaseem.

Sun danyi shiru na lokaci,sa'anan kareem ya dubi kaseem yace 'guy kasan me?
Kaseem ya girgiza kai yace sai ka fada.

Juya motan mu je gidan Hisham.
Ba gardama kuwa ya yi rivas suka kama hanyar gidan Hisham.
Yau ma a kwance suka tarar da shi.
Yayi masu barka da zuwa.
Bayan sun zazzauna kareem ke fadi"ya ya ake ciki ne aboki?..ko ka sami mafita? Don lokaci na gabatowa.

🀦🏻‍♂da'fe kai yayi "wallahi har yanzun ban sami mafita ba....kwakwalwata ta daina aikin ma.
Dariya suka yi masa.

A gani na kuma idan za'a dauki shawarata,muje gurin mamarta kawai...muyi mata bayani daya bayan daya akan abinda ilham din take shirin aikatawa.
Itace kawai zata iya hana ta.
Duk sun amince da shawaran kaseem,amman Hisham na me kwankwonto akan mamee baza ta amince da maganarsu ba.

Gidansu ilham suka nufa,me gadi ya sanar da su mamee tana gurun aiki, basu fidda rai ba suka nufi guri aikin ta.
Sunyi dace domin kuwa ta fito lectures kenan,tayi masu izini da su shiga offishinta ita ma din tana biye da su.
Baby Muhammad,(Abba) ne zaune yana buga games a laptop dinta,yana jin motsin shigowarta ya nufe ta yana fadin "wani lokaci ne zamu je sanyan ice cream din,a shagwabe yake maganar kamar zaya yi kuka.
Rungumeshi tayi,ta sumbaci goshinsa'yanzun nan,baba na...amman sai  ba'ki sun tafi tukun.
Sai a lokacin ya dubi su hisham tare da risinar da kai yana gaida su.
Bayan an natsu mamee take tambayarsu abinda ke tafe dasu.
   Kaseem ne ya wakilce sa da yin bayanai akan abinda ke ta'fe dasu game da ilham.

     Dariya sosai mamee tayi sa'anan tace "kuma ku dauki maganar ta muhimmaci?...toh ku kwantar da hankalinku sabida ba abinda ilham zata iya yi...besides akan wani laifi zata sa akamasu?🀷🏻‍♀..babu! Don haka ku kwantar da hankalinku,ku daina tunani irin nata.
    Nan mamee ta shiga jadada masu akan ilham bazatayi komai ba,bacin rai ne yake sanyata fadin haka.

Sunyi godiya tare da mike wa don kimawa inda suka fito.
Hisham ya mikawa Abba hannu yana fadin 'ka bini mana,na saya maka ice-cream din tunda mamee na aiki yanzun.
Cikin jin dadi yace'toh'...ya juya ya dubu mamee "mamee na bi wannan uncle din?
    Ofcos! Ai yayanka ne shi.
Ya mike yana tsale tsale..cikin jin dadi yayiwa mamee sai ya dawo.

Suna fita da'ga offishin mamee wayat hisham ya shiga ruri......ganin me kiran ya sanya shi yin tsuki,tare da maida wayan cikin aljuhunsa.
Wayan tayi ringing kamar sau biyar,ganin ba'a hakura yasan zuciyarsa na raya masa watakila wani abu na faruwa ne.
ya dauki wayan,baba lamido ne.
Sun gaisa..can bangare baba lamido ya umurce shi da ya zo yanzun nan suna nemansa.
Bayan ya gama wayat yacewa kaseem 'muje gidan baba lamido,suna nema na acan....ya kai kallonsa ga Abba 'zamu dan biya wani gida,kayi hakuri..idan mun fito sai muje gun sayan ice-cream din.
Abba yayi murmushi "ba komai uncle.'

A waje sukayi parking mota...suka karasa cikin gidan da kafa.sai dai Hisham ne kadai ya shiga ciki-cikin gidan.
Kaseem da kareem harda Abban samun guri sukayi  a gurin da aka ke'be don hutawa,don haka suka zazzauna suna jiran fitowan Hisham.
Suna zaune gurin,me gadi ya wangale gate...Alhaji buba ne ya shigo,yayi parking ya fito dagacikin motan.
Gefen su ya biyo za ya shiga cikin gida,nan kareem da kaseem suka gaishe shi,ganin haka yasa Abba ya gaida shi,shima.
Har ya juya zai wuce,sai kuma yayi kiran Abba da hannu...ya mike ya nufi gun da Alhaji buba yake tsaye..
"Kai dan wani gida ne?
shiru abban yayi na dan lokaci,sa'anan yace nima ban san sunan gidan mu ba.
Alhaji buba ya murmusa,ya kai hannunsa kafadan Abba tareda risunowa 'ko zaka iya fadamin sunan babanka?
Mustapha sunan babana..ya bashi amsa a takaice.
Kai fa?..alhaji buba ya sake tambaya wa.
Ni?😳...a makaranta muhammad mustapha ake kirana,mama na kuma tana kirana Abba.
Hisham ne ya karaso gurin a lokacin da Alhaji Buba ke shirin sakeyiwa Abba tambaya.
Ya gaida shi, shima ya amsa cikin fara'a yana  me tambayan Hisham 'wannan yaron dan wani gida ne?.
Shiru hisham yayi ya rasa amsar da zai bashi....sai da alhaji Buba ya sake tambayarsa sa'anan yace  kanin ilham ne..
Da shike yasan da zacen ilham da hisham din,ya kuma san hargitson da ake ciki.
Ya dubi Abba,ya kara risuniwa ya sumbaci goshin sa.
Ya sa hannu ya shafi kuncinsa tare da fadin ya'ya kake?
lafiya lau ya maida masa.
Ya'ya yayanka mujaheed?
Lafiya lau,ya sake fadi.
toh madallah..

Yana tafiya yana waigowa,shima Abban alhaji buba yake kallo.
Hisham ya taba shi yace muje ko?
A hanyarsu ta komawa,abba ke tanbayar Hisham waye shi wanan mutumin da ya sumbace shi a goshi?
Kanin mahaifi na ne.
Murmushi yayi tare da fadin uncle Hisham zaka sake kawoni wannan gidan na gan sa?
kai ya da'ga masa 'inn shaa Allah.
Cikin jin dadi yace yes!!πŸ’ͺ🏻,na gode uncle Hisham.
bakery din da ke unguwar sarki,suka nufa.
Ya umurci Abba da ya fadi abinda yake so,
ice-cream kawai nake so,fadin Abba.
Hisham ya saya masa ice-cream din ya kuma hada masa da cakes masu yawa...daga nan gidan hisham suka nufa.

Sai bayan ssllan magrib,ya tafi maida Abba gida.
HAR cikin gida ya shiga.
Blessing na bude masa kofa,idonsa ya kai kan gimbiyarsa tana saukowa daga sama...
mamee kuwa,na zaune a kujerun alfarma da suka kayata falon,tana me dane danen wayarta.

A GUje Abba ya isa gurinta,ya ajiye ledojin da ke hannunsa bisa teburin ya rungume mameensa yana sumbatatan.
Ya bude ledan ya ciro daya daga cikin robobin ice-cream din,ya bude ya shiga bata a baki.
Ya is a haka babana,..na gode..fadin mamee.
YA Girgiza kai 'a'a,sai kin shanye duka na cikin roban nan.
SAI da ta kakalo aman karya,sa'anan ya daina bata.
Ta dubi Hisham da ke zaune yana kallonsu tayi masa godiya.
Gimbiya kuwa ta daura kafarta daya bisa dayan...bata gaida Husham ba,balantana tayi masa magana.

"Baka yiwa anty tayin ice-cream din ba"
Cikin turo baki yace"itama bata bani nata."
toh ai na fada maka,ka barta da halinta,duk abinda tayi maka ka daina ramawa,kaji babana!.
Ilham dai sai kallonsu take,tana me takaicin abba.

Yaawaaa....kinsan me mamee!.
A'a babana,ban sani ba ssi ka fada.
da muka fita da uncle Hisham,munje wani gida na gan wani mutum me matukar kama da Anty.
idan da kana zaune kusa da hisham,zakaji hargitson da ya'yan cikinsa suke yi,sabida maganar abba ya razana su.
Cikin mamaki mamee ta kalleshi tace kohh?
eh wallahi mamee..kin ma san me?
Kai ta sake girgizawa,tana me duban fuskarsa.
Banda kamanin da suke dashi da anty,harda wannan abinda take dashi a gefen bakinta,shima yana dashi...kuma ya san ya'ya mujaheed.

Shi kadai kawai suke kallo,yana zuba masu surutu..
YA mike cikin farin ciki da anashuwa yace ..kuma kinsan me?
Kai ta girgiza.
wallahi inason mutumin nan,sabida ya sumbace ni yanda kike yimin.
Shiru mamee tayi,banda kallon Abban, ba abinda takeyi.
Dallah yiwa mutane shiru...da'ga yau na sake jin kayi maganar wannan mutumin sai na yi maka dukan tsiya..
TA DUbi Hisham a fusace tace "kai kumaa...
mamee ce ta tsinke mata maganarta.

MAMEE ta dubi Hisham tace'na gode kwarai da gaske,akan dawainiyar da kayiwa abba..sai dai kuma idan bazaka damu ba,abinda ya faru,yau bazani so ya sake faruwa ba.
hisham yayi gyaran murya,ya baiwa mamee hakuri tareda yin alkawarin hakan bta sake faruwa..
........fuuuuu ta mike,tare da barin gurin.
Mamee da dubi Hisham,tace kar ka damu da duk wani abu da zata ce maka,nima kuma zan fahimtar da ita.
A sanyaye ya bar gidan,har gun motan ss abba yayi masa rakiyah,yane me tambayarsa yaushe zai sake zuwa suje gidan.?

Ka'sa zama tayi tun da ta koma daki...sai kai da komawa take,tana me jin haushin abinda Hisham yayi a yau....tayi kuttah,tana raya wa aranta sai ta hukuntashi.

Mamee ce ta turo kofa,tana ganinta ta bata rai.
Gefen gadonta mamee ta zauna,ta riko hannunta tare da jawota ta zaunar.
"Me kike kinsawa a ranki yanzun kuma?...cikin ido mamee ke dubanta ayayin da tayi mata wannan tanbayant.
Shiru tayi bata amsa ba.
wannan bacin ran dai na san sabida abba ya hadu da mahaifinku ne ko?
Kai ta da'ga,batare da ta dubi mameen ba.

Ki sa a ranki haka Allah ya rubuto zai faru,ko ba da sanadin hisham ba,idan ma dake ne zai hadu da mahaifinsa...kuma kar ki manta jini na da matukar karfi.
Don haka bana son ki baiwa Hisham laifi akan faruwan haka....da haka mamee ta shawo kan ilham da nasihohi.

Mahaifin hajiya zubaida ne zaune da abokansa wa'anda suke shirin hada hannu da karfinsu domin sanyan kafani da aka kawo masu talla daga japan.

*FAHAD INDUSTRIES*,kamfani ne  na ke'ra motoci,mashuna,kekuna da duk wani abu da ya shafi karfe..me wannan kamfanin ABDULRAHMAN IBN FAHAD balarabe ne daga kasar saudiyah.shine mutumi na uku a jerin masu arzikin a kasashen larabawa..a jerin masu kudin duniya kuwa shine na goma shabiyu.
 Dan wannan balaraben me suna Fahad shine ya kawo wa mahaifin hajiya zubaida tallan kamfanin.
ya sanar mashi cewan mahaifinsa ya rasu ne kason sa kean wannan kanfanin shiyasa yake son ya saidashi.
ganin wannan garabasan ba tareda wani tunani ko nazari ba, ya sanya mahaifin haj.zubaida kiran abokansa,domin kuwa bashi da kudin da zai iya saya masa kamfanin...asalima duk fadin africa,ba wanda zai iya sayan sa shi kadai,komai kudin sa kuwa.

  Abokan mahaifin haj.zubaida sunyi mamakin jin rasuwan Abdulrahman ibn Fahad da'ga sama sabida basu ji rahotani a news ba ko a social media.
Suma din basuyi bincike ba suka aminta da tayin mahaifin hajiya zubaida don haka suka fara dabaru da kuma kudin da ko waninsu zaya bada..
sun nemi da akawo masu samples da hotunan kanfanin,yaron yace masu su turo daya daga cikin su ya zama masu ido,ma'ana ya dudduba masu kanfanin.

a cikin sati daya akayi komai da komai,umurnin yaron kenan.sabida ya shaida masu idan suka wuci sati dayan zai fasa saida masu.
hakan yasa mahaifin haj. Zubaida ya tattara makudan kudade har biliyan hudu,ya turawa fahad,dalili kenan da aka kawo takardu,suka fada a hannun Alhaji Buba.
Read More »

Monday 5 February 2018

Page3 OF KAZAMACE MATA TA.

πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
*KAZAMACE MATATA*
          πŸ’–πŸ’–πŸ’–πŸ’–
  By Ganarious.
Page3

√Mutan Kenya godiya dubu,dubu...πŸ˜˜πŸ€πŸΌπŸ‘πŸΌ

√Ku bi novels Dina a πŸ‘‰πŸΌ ganarious.blogspot.com/
              Ko
πŸ‘‰πŸΌgroup din Facebook, *Ganarious book series*.
Thank u.

√ *SANARWA!!!*
KAZAMACE MATATA,kirkiraren labari ne har sunaye,da garurukan ke cikin labarin,idan labarin tayi shige da rayuwanki/ka,ne neman afuwaπŸ‘πŸΌ....ba don naci zarafin kowa ba.

       **          **          **
   Sai da ya gama cin abincin,sa'anan Alhaji suleiman ya dubeshi yace 'kanwarka tace kana cikin damuwa,ina kuma sa ran a duniyar nan ta fi kowa sanninka....don haka zamu so jin abinda ke damun.

Nan ya kwashe yanda sukayi da inno ya sanar masu.
Ya kara da fadin "banyi gaggawan yin aure ba,sabida bana son nayi da na sani a rayuwar aurena, a gaskiya hankalina bai kwanta da maganar inno ba,tana fadin hakan, na tsinci kaina cikin wani yanayi,sabida ina tunani zata ruguza min rayuwa.

Rai bace khadijah tace 'gaskiya hakan ba zai yiyu ba....duk wacce inno zata nema maka,ina da tabbacin ba ta gari bace...kar ka manta mahaifiyar yarinyarce abokiyarta, anan abokin barayo,barayonne..sannan fa me halin kirki baya taba birge inno!..tunda ko yarinyar ta birgeta har take neman hada ku aure...! Tooh fa abin shinshinawa ne.
gaskiya yaa munir kar ka amince da haka....wannan karon kam,kayi kunnen kurame,kayi idon makahi da wannan zancen sabida rayuwa ce da idan ansami akasi toh fa sai da tamakon Allah.

Alhaji suleima ya nisa yace "gaskiyar khadijat,idan kagan zata danne maka hakkinka toh kayi magana tunda wuri...
Da haka suka tattauna yanda zasu magance zancen inno.

Engr.munir ya dau tsawon sati biyu,watau jumma'a biyu kenan bai je gidansu ba.
Sai a cikin sati na ukku,sa'anan ta tafi bayan sallan jumma'a kamar kullum

Inno na ganinsa ta hau masifa,tana fadin daman ta ji a jikinta bai yi marhaba ds maganarta ba...daga nan ta shiga kwalan munafurci wai ba don itace ta haife shi ba shiyasa yayi mata haka da makamancinsu.
  Suna tsaka da haka malam Abdullahi ya shigo....ya tarar da tana kwala,cikin rudewa yake tambayarta me ke faruwa.

Wannan danπŸ‘‰πŸΌ...ta nuna munir da yatsa. Sabida ba nice na haife shi ba shi yasa ba zai bi umurni da maganata ba..
...malam Abdullahi cikin matssuwa yace fada min abinda yayi maki na hukuntashi yanzun nan.

Ta share hawaye tace "maganar yarinyar nan ne da na sama masa,tun ranar da na tunkare shi da maganar ya dauke kafa daga gidan nan watau baya so kenan.

Ahaaf...nan da nan malam Abdullahi yashiga balbalin masifa,ta inda yake shiga ba ta nan yake fita ba....aure kam kamar anyi an gama,sai dai idan yarinyar ce tace bata son ka.

Ya gama zage munir tas, sa'anan ya fice abinsa.
munir ya bi bayansa,ya je ya bashi hakuri...da kyar ya hakura sannan ya umurci munir da ya tafi ya baiwa inno hakuri.
Ya nufi cikin gida cikin sanyin jiki,ya tarar inno na sa'insa da Habiba akan zancen sa da suwaiba.
Habiba na ganinsa tayi shiru.
Guri ya samu gefen inno ya tsuguna yana me bata hakuri.
Ta ji dadin haka sosai...don haka tace masa ta hakura,kuma tana son zuwa yamma ya zo isa ya yi masa rakiya zuwa gidan su suwaiban don su ga'na da ita.
Ya amsa mata da "toh inni"...sannan yayi godiya ya mike.

Gaskiya inno kin shiga hakkin yaaa munir...fadin habiba dake zaune a gurin tana jifan inno da harara.
Inno ta harareta ba tare da tace mata wani abu ba.
Tunda munir ya koma gida yarasa me keyimasa dadi,ya kasa samun nastuwa sai kai da komowa yake yi tsakanin dakunan gidansa.
Dalilinsa na zuwa gudansu inno shine din ya bata hakuri akan ta hakura da zancen aurensa da suwaiba,..sai kuma ya tarar da makircinta.

Wayar Alhaji suleiman ne ya shigo,ya amsa wayar jiki a mace.
da jin muryansa alhaji suleiman yasan ba'ayi nasara ba, don daman tare suka yanke shawaran da yaje ya sami inno yace ta hakura.

Ya ya kayi da innon,muna jiran kiran ka tun dazun baka kira ba..shiyasa na kiraka yanzun don khadijat ta matsu...fadin alhaji suleiman.

Engr. Munir ya nisa sa'anan ya fadawa alhaji suleiman duk abin da suka faru tsakaninsa da innon.
Hakuri ya bashi,tare da bashi shawaran da ya da'ge da addu'a,Allah shi kawo mafita.

Bayan sallahn magrib munir yayi wanka,ya sanya kananan kaya tare da feshe jikinsa da turaruka masu kamshin gasket,don daman shi ma'abocin son kamshi ne.
Gidan su inno ya nufa...da sallaman sa ya shiga cikin gidan,ya tsakar gidan ya gansu zazzaune suna shan iska...yayi gaisuwa sannan yace wa inno yana son zai je gidan su suwaiba.

HAkura waje sabida jin dadin abinda ya fada....
"TOh toh toh madallah,haka yana da kyau.
TA dubi inda isa ke zaune tace masa "tashi ka raka shi bayan kassuwa".
Ido waje yace 'bayan kassuwa kuma,wane gida zamu na hala!.

Gidan inna ige zaka na raka shi,daga nan za'a nuna maku gidan su suwaiban.
Kin tashi yayi sai da ta dunkula masa zagi sannan ya mike yana tura baki.
har cikin gidan su inna igen engr. Munir ya shiga,ya gaishe su tare da yi masu kyautan kudi masu yawa..
Inna ige ta hada su da jikanta don ya nuna masu gidan su suwaiban.
Ashe ma makwabta ne,gida dayane a tsakaninsu,ganin haka yasa engr.munir ya koma cikin motansa ya gyara parking dai dai gidansu suwaiba...
Jikan inna ige ya shiga cikin gidan don yi masu sallama da suwaiban.

SUn kai kimamin minti arba'in bata fito.
RAnsa ya baci,a ransa kuwa yana fadin za'a fara haka tun yanzun?!!
tsuki yayi...watakila ma wanka ta ke yi,watakila irin matannan ne da basu tsabtace jikin su sai idan za a fita ko idan samarinsu sun zo gun su..haka yake ta sake sake a ransa..
YA sake tsuki yana me duban agogon hannunsa.
ISA ya juyo ya dubeshi yace 'yaa munir da ka fita harkan yarinyar nan mukoma gida ka fadawa inno ba mutuniyar kirki bace,ji fa yanda ta shanya mu anan.
Yana rufe baki suka hango wata na fito wa daga gidan....
Ganin ta nufo su ya basu tabbacin ita ce suwaiban.
Daga isan har engr munir suwaiba suke kallo.
daga yanayin tafiyarta ya raya ransa wannan ba natsattsa bace...tafiyarta kamar zata tashi sama.
Gefen isa ta zo tare da kwan kwasa gilashin.
Engr.munir ya sauke gilashin a hankali yana me dubanta.
Barkan ku da zuwa ta fada.
...wata zuciyar tace ka I...!wannan akwai zakin murya....barkanki kema,engr.ya maida mata.
Maganarta ta yan'sakkwatawaπŸ˜„..tace wane nah ah muneeru ku?.
Isa ya nuna munir da yatsa..bata bata lokaci ba ta zagayo ta gefensa.
Dukowa tayi dai dai windon sa.
SUbhanalillah..!!!.numfashinsake barazanar daukewa,sabida wata irin do'yi da warin hayaki dake tashi daga jikin nata..
Sai ji yayi tana fadin "shii na ka tahi cikin duhu..bara na koma na amso tocilan inna.
Ta juya zata tafi yayi kiranta domin kuwa ya fahimci abinda take nufi.

Yasa hannun sa ya kuna fitilan cikin mota,haske ya bayyana,ya juyo ya dube ta....nan ta'ke zuciyarsa ta shiga raya masa ababe masu yawa.
Itama ido ta sa masa tana me kallonsa...sun kai minti uku a haka sannan tace masa "toh na ganka yanzun.

YA Numfasa domin a takure yake,a matse yake da ya bar gurin.
.....gashi na zo ne da niyar  mu fahimci juna amman kuma baki fito da wuri ba har lokaci ya wuce,dare yayi,sai dai wani lokaci idan na sake zuwa ko?.
Ohoooo...walle wata abikiyata naka sawa man famin,shinassa ban fito da wuri ba.

YAYI ajiyar zuciya yace' toh shikenan,mu zamu koma gida,sai na sake zuwa.
Tayima sa sai da safe..ta juya zata tafi yayi kiranta.
hannu ya sa a aljuhun wandonsa ya ciro kudi batare da ya kirga ba ya mika mata yace gashi a sayi turare ko!!

cikin murna tace a sayi turaren mi!..mi akai da turare abin banza!..tabdi ai wannan kudin ababe da dama za'ayi da su.
Mamakinta yake,sai kallonta yake..shi fa ya bata kudin ne sabida riga kafi....kar ya sake zuwa,ta fito masa da wannan do'yin.
GODIYar ta ya farkar dashi,ba tareda ya amsa ba tayi cikin gida da saurinta.
Read More »
Designed by Jide Ogunsanya.