Pages

Sunday 24 September 2017

SOYAYYARMU👫


             By Ganarious.
17
Ji nayi an zare littafin dake hannuna,haka yasa na da'go.mamatace tsaye a kaina muna ha'da ido na sauko kasa inayimata sannu da dawo wa.ta sami daya daga cikin kujeru ts zauna tana kallona.
  Ta dauki tsawon lokaci sa'anan ta tambaye ni tunanin me nake haka da take sallama ban amsa ba ko bansa da shigowarta ba ko!
    Shiru nayi ban amsa don bani da abin fadi... tayi ajiyar zuciya sa'anan ta cigaba fadin"ni da Babanki mun zauna don neman mafita akan matsalarki"
Nan na kalleta,watau kallon rashin fahimtar me take nufi da hakan.
Read More »

SOYAYYAR MU👫..

            By Ganarious.
16
Da yatsa nayi mata nunin   dakin fillo,sai saukan mari naji a kunci na.na dago kai muka hada ido da ita sai kuma ta hau duka tana shuri na..
Ranar ce ta farko da mamata ta kai hannunta jikina da sunar duka!.
Kaina na tsakanin gwiwowina ina kukan zuci,jin an daina bugun ne yasa na da'go.
fillo na gani duke a gaba na Babana kuwa yana rike da mamata ya janta zuwa cikin gida.na juyo muka hada ido da fillo,murmushi nayi masa   sai dai shi bai mayar min ba.sai ya tsiramin ido.muna cikin haka babana ya dawo cikin rudani da'gani yana fadin ina ke maki ciwo...sai a lokacin na sami damar yin kuka duk da daurewan dana so yi.
Read More »

SOYAYYARMU👫

         By Ganarious.
15
Haka mukayi ta rayuwa kullum safe sai na kaiea fillo abinci kafin na tafi makaranta,idan kuma na dawo sai na shiga gun sa munyi hira kafin na shiga ciki.idan kuma na shiga ciki Allah Allah nakeyi na idar da sallah na dibi abinci na a plate natafi dakin sa na zauna ina ci muna hira.duk da kashaidin da mahaifiyata tayimin.
Weekends kuma mu tafi yawon ganin gari da sayayya,a maimakon librabrin da muke zuwa da safiya.
Read More »

SOYAYYARMU👫

         By Ganarious
14
Alhamdulillah,maa Shaa Allah...Haj.Fateema A.Bayero(mrs Bash gwandu) ta sauka lafiya.mun sami babby girl me suna umaimah,Allah shirayamana ita kan addinin musulunci.ameen.
Jama'a makarantan soyayyarmu ina muku barka da sallah.Allah shi maimaita mana.
ina me baku hankuri akan rashin typing akan lokaci.kuyi hankuri.
Gaisuwa ta mussamman ga haj.Sa'adat Ahmad(a.k.a sa'adat mubi 4real,basu labari).
Read More »

SOYAYYAR MU👫.


          By Ganarious.
13
A sanyaye nake komai tun bayan tafiyarsu Malam Lamido.
Da zarar na zauna sai na fara tunanin dan fillo.wata sa'in na shiga dakin da suka sauka nayi zaune ina tunano fuskar sa da murmushinsa ni karan kaina na kasa gane me ke damuna.
Mahaifiyata kuwa har tambayata take wai ko lafiya.! Ko so kike ki koma rugga.
Yan gidanmu sun samin suna wai "yar rugga"
Read More »

SOYAYYAR MU👫

By Ganarious.
12
Falon Babana musake komawa tare dasu Malam Lamido,Nan nasake yimasu bayanin malam Lamido da fillo.
Babana da abokansa sunyi mashi godiya sosai.sai alokacin babana ke bayanin ai daman Gobe za'a yi shari'a ta karshe a kotu,amman tunda Allah yasa gaskiya ta bayyana,toh wadannan yaran da iyayensu kawai za a kamomin.
Read More »

SOYAYYAR MU

         By Ganarious.
11
A rugga kuwa bani da wata damuwa da ta wuce nagan iyaye na,Idan da sabo toh na saba dasu.na koya masu ayyuka dayawa,na kuma koyi wasu ababen a gunsu.haka nayi rayuwa a cikinsu har Allah ya kawo wani da zai je birni.
  Ana gobe zamu tafi,mukayita hiran bankwana dasu na kuma yi masu alkawarin sake dawowa.a hiranmu nake cewa Bintu idan ta haihu zan raini dan,na kuma kai shi birni.taji dadi sosai don a rayuwarta ba abinda ke mata dadi kamar ayi zancen birni,ko a cemata yar birni.
Read More »
SOYAYYAR MU👫
    By Ganarious.
8⃣
Bayan na bude takardan sai na gan rubutu kamar haka.'hahah..idan har kin tashi kin gan wannan takardar toh ki godewa Allah..ba mu sonki,bamu kuma kaunar ganinki.shiyasa mukayi maki hakan.sai mun hadu a can.
  Sai a wannan lokacin na tuna abinda su hafsat sukayi min.kuka na shiga yi sosai ina fadin menayi suka tsaneni haka!
Fillo kuwa ba abinda ya kai sai kallo na...sai da nayi me isata sa'anan nayi shiru domin kuwa kaina ya fara saramin,kamar jira yake nayi shiru sai yace min na tashi mu tafi tare da yimin addu'a da fulfude wai Allah reene,Allah seyne!.
   Tafiya mukayi sosai sa'anan muka isa ruggan su.yan uwansa sunyi mamakin ganin fillo tare da dani,sai na zama masu abin kallo.
Da fillatanci yayiwa iyayenshi bayani.
Na dade tsaye don kuwa dan fillo da yan uwanshi gabaki daya suka shige wani daki sai wasu kananan yara da suka firfitoo suna kallona kamar sun gan wata halitta.har na fara jin haushin biyoshi danayi.ina a tsayen,sai gasu sun fito amman kuma basu cemin komai ba,ko ga guri zauna ma ban samu ba...shima din fillo haka yazo ya wuce ni bai ce komai ba...hankalina duk yatashi ina tunanin me mutanen nan ke shirin yi dani.
 Guri na samu na dan tsuguna,ba abinda nake tunani sai sallolin da Ke kaina..ina cikin wannan tunani na hangi wata budurwa zatayi sa'ata a girman jiki,amman a shekaru mu ba tsara bane.itama din dai kallona takeyi har tana tuntube,da hannu nayi mata alama da tazo."don Allah ina zanyi fitsari?"nace da ita.
Bata amsa ba sai kallona takeyi na sake yi mata magana nan ma bata amsa ba ta juya ta wuce abinta,..gashi fitsari ya matseni sosai.
Nabkoma na tsuguna ina tunanin wannan wata rin rayuwa ce...sai kawai kuka ya zo min...amman kuma mutanen kamar dabbobi sai kallona sukai daga ne'sa.
   Kuka fa nake sosai,sai ga dan filli ya dawo shi da wani mutum.suna isowa na mike sauri nace fitsari nake ji wannan mutumin yace a kaini bayan ruggansu nayi fitsari   sa'anan na dawo.
Wannan mutumin dogone me kyan gaske gashi fari tas dashi,sai kuma Allah ya bashi abinda mata ke kira dimple...ya tambayeni duk wani abu da yake son sani game da haduwata da dan fillo kuma da dalilin da yasa aka bar ni a daji..na kuwa fada mashi komai da komai daga kan abinda su hafsat sukayi min har yanda muka hadu da dan fillo.na kuma rokeshi da ya taimaka min na koma gun iyayen A kaduna.
'toh naji zamu taimaka maki mu maida ki gun iyayenki sai dai ba wanda zai je birni cikin yan ruggan nan.amma idan ansamu za'a mai dake gida.
Shiru nayi ina me rokon Allah a zuciyata da yakawo min mafita.

Wani daki suka kaini wai nan zan dinga kwana,da kamar nace masu bazan iya kwana anan ba amma ba yanda zanyi dole na na shiga ciki a takure na zauna.
A sannu sannu na fara sabawa dasu sai fai wasun su ba su jin hausa sai fulfude...Na rame sosai don kuwa tunda na shiga ruggan bana iyacin abincisu duk da kokarin danakeyi na turtusa kai na amman abin ya ki don kuwa idan na tursa kaina to amai ne zai biyo baya,hakan asa iyayen fillo cewa a dinga ta'cemin nono shanaye.
  Nafi shakuwa da dan fillo,idan za shi kiwo sai na bishi idan har ba zai dade bane.
Read More »
SOYAYYAR MU👫
      By Ganarious.
9⃣
Wataran muna gun kiwo ni da shi sai nace ni dai har yau bansan sunarka ba..ya kalle ni cikin murmushi sa'anan yace sunana Mustafa amma bakiji ana cemin buba ba?.
Na girgiza kai tare da fadin a'a ni ban ji ba,asalima ban taba ji ko lura da wani ya kira ka ba.
"toh kishee min buba"
Toh malam Buba,nace mashi ina murmushi...
Can kuma nace amma mamarku da yaranta sunyi daban kamar ita tana da surki da buzaye ko?
Eh...buzuwace.
Cikin mamaki nace....kai,!tabdi jam amman ya'ya akayi hakan ta faru?
  Ho...ni ma din ban sani ba.
Na dade ina mamakin yanda akayi bafulace ya auri buzuwa.amma kuma combination din yayi kyau sabida yaranta suna da kyau kamar larabawa ,ga gashi har gadon baya,mazan kuma gashin su yayi luf-luf yakwanta masu.
     **    **  **
Akwana a tashi har nayi sati biyu a wannar ruggan,ina cikin na uku amman ba wani labarin batun komawata...a lokacin ne yayan Buba fillo ya dawo daga kiwo ana kiransa Dahiru.shima yayi mamakin ganina nan aka bashi labarina,cikin kankanin lokaci muka fara shiri da shi...ina cika sati hudu akayi auren dahiru da diyar maigari(mai gari Laamido shine wannan mutumin da yayimin alkawarin maidani ranar d na zo ruggan da buba fillo).shine ya'yansu baban buba(dan fillo).diyar shi bintu da dahiru cousins ne kenan.
Amarya bintu da bata wuce shekara takwas ba sai mamakin abun nakai,ita ma mun shaku,duk da na girmeta nesa ba kusa ba idan muna hira sai nace mata wataran zan kaita birni,sai tayi ta murna.haka dai nayita zama da wayannan mutanen a sannu a hankali.
    ***   ***   ***
Su hafsat ne sukayita tafawa suna murna yau burinsu ya cika."kai ku zo mu tafi fa kar a tafi a barmu"fadin hafsat bayan sun gan cewan bana cikin hayyacina.da gudu suka bi bayan sauran daliban cikin sa'a kuwa suka iske ana shiga mota ne..
Sun isa masauki(hotel) ana fitowa don shiga cikin dakuna,shine Awwal ke tambayar su ina Aisha?
Sun dan dauki lokaci sanan Rabi'a tace ai ba motar mu take ba.ka dudduba motoccin mana,kana wani tanbayarmu.ta karashe maganar ne kamar Me fada.
Bai musa ba ya koma inda aka ajiye motor A daman kuma motan yake amma kowa ya sauko bai ganni ba.sai kuma yakoma gunsu yace aisha fa bata ciki.
Toh miye na mu a ciki.?inji Hafsat
Ban gane miye naku a ciki ba.tare na barku a dajin kunga ai dole ne na tambayeke kenan.
Tsaki sukayi gaba dayansu suka juya zasu tafi..sai ya sha gabansu..Awwal yaro ne da baya daukan renin hankali ko gun yan'uwansa maza.
"wa kukeyiwa tsaki? Ya tambayesu tare da nuna masu dan yatsan.
 Gefenshi suka sake bi batare da sunce mashi komai ba..
Read More »
Designed by Jide Ogunsanya.