Pages

Wednesday 31 January 2018

Page 33 of SOYAYYARMU

SOYAYYARMU 👫
     By Ganarious
Page3⃣3⃣

Gaisuwa ta mussaman ga mutan KENYA,(NAIROBI)..ALLAH shi bar kauna.

Fatan alkhairi ga makaranta..👍🏼💖

A koda yaushe sabbin updates na nan a 👉🏼 ganarious.blogspot.com/

     **      **        **
Mamee ta juya ta dubi ilham,cikin natsuwa da kwantar da murya tace "ba wai na fadamaki labarin zamana da mahaifinki da danginsa bane don ki tsane su, ko dun ki rama min abinda sukayi min..ah'ah
Bani son  na karajin wai kince zaki rama abinda sukayi min ko makamancin haka...sa'anan kar ki manta laifin wani baya shafin wani,..shi Hisham miye nasa a ciki?
Shiru ilham tayi,ta risunar da kanta kasa.
Mamee ta cigaba da fadin,baki gaji wulakanci ba,don haka rashi daukan wayar sa kamar kina wulakantashi ne don haka ki daina, kinji ko?.
Ta da'ga kai tare da fadin naji mamee..
Nan mamee ta mike tayiwa su Hisham da abokan sa sallama ta shige dakinta.

Shiru shiru ba wanda yayi magana tun tashin mamee.
Hisham ya cije,ya tattaro karfi😆,ya natsar da zuciyarsa zai yi magana.
Yana gyaran murya tare da bude baki,ilham ta dakatar dashi ta hanyar daga masa hannu...kamar daman jiran sa take.

Ta kara murtuke fuskanan tata😠...tace "yau ya zamar maka farko,da kuma karshe da zaka fadawa mamata wani abu game dani...bani son alaka da kai ko dole ne😡,na fada maka na fasa auren,don haka ka fita hanyata.😏
Tana kaiwa nan ta mike zata tafi,sai kuma tayo ribas ta dawo baya.
Mind u zan fada maka in advance,ku kasance cikin shiri,kamar yanda na fada maka ina nan akan bakata...sa'anan daya daga cikin family nan zai je kurkutu(prison),nan da sati biyu,bayan ya tafi wani zai bi bayansa,wanda shi idan yaje,ya tafi kenan nan zaiyi sauran rayuwarsa...don haka kana iya fada masu,su kasan ce cikin shiri..who knows watakila ma kana daya daga cikinsu🤔
Nan ta barsu zaune,tayi tafiyarta.
Cikin jin takaici da haushin abin da tayi masa a gaban abokansa,ya mike tsaye rai bacce yace "ku tashi mu tafi,wannan ma katoton wulakanci ne.😏...Mikewa suka yi jiki a sanyaye suka tafi,a hanyarsu ta koma wa kuma ba me magana,tsit kake ji a motan sai dai jefi jefi kaji tsukin Hisham., gashi idanunsa sunyi jajir.
Kamar kullum yau ma Hisham bai rintsa ba,cike yake da haushin abinda  ilham tayi masa a gaban abokansa!...abinda ya fi damuwar kuwa shine furucinta na karshe..
Tashi yayi ya zauna, a ransa yana fadin dole na nemi mafita kafin nan da sati biyu.

      **        **            **
A yayinda dakin ya dauki sanyi,kamshin dadi me sanya ni'ima da nishadi ke tashi.
Lallausar kafet ne shimfide a kasar dakin,wanda kana takawa kafarka na shige wa ciki...daga gefe teburi ne aka zagaya ka kujerun alfarma don zaman baki.
Daga can gefen kuma,teburi gilashi ne da kujerar taya a bayansa.
    *ALHAJI MUSTAPHA B.* shine sunar da ke ke're a wata doguwar kwalba wanda aka dagwarashi saman teburin.
Teburin na dauke da ababe kamar su laptop,takardu dasu files,sai daga gefe aka ajiye wata karamar frame  me kyan gaske dauke da hotonsa da uwar gidan sa Hajiya zubaidah.
A hankali aka budo kofan tare da sallama .
Ya amsa sallama yana me fara'a ganin me shigowan.
Alhaji Abdulmuminu ne,mahaifin hajiya zubaidah...ya shigo ya zauna a daya daga cikin wadannan kujerun.
Alhaji mustapha b.  Wanda jama'a ke kira da Alhaji Buba, ya karaso gun Alhaji Abdulmuminu suka gaisa.
Ya mike ya nufi inda firij ya ke a ajiye ya dauko masa ruwa roba.
Ya sha ya ajiye roban ruwan sannan suka fara tattaunawa akan abinda ya kawo sa.
Alhaji abdulmuminu yayi gyaran murya yace "watau batun kanfanin nan ne na kasar jafan da ake son saidawa.
Alhaji Buba ya daga masa kai,tare da fadin na'am ina jinka alhaji.
Munyi mitin da sauran wadanda muke son hada kai da kudi don sayan wannan kanfanin.....muna sa ran zuwa jibi takardun kanfanin zai iso hannunmu daga can kasar,kuma a ranar ina da mitin a kasar kuwait,don haka nake son ka wakilce  ni,domin kuwa a hannuna takardun  zasu fado,tunda bani nan a ranar sai su fado a hannunka din.
Idan sun iso za ayi mitin a abuja,inda kowa zai zo ganin takardan da idonsa.
nan dai alhaji buba da surikansa alhaji Abdul mumin suka tattauna,daga baya yayimasa sallama sa'anan ya tafi.
Tsaye yake a jikin windon falonsa,daga nan yana hangen mai fita da shiga ta gate din gidan.
Hannayensa na saman kugunsa..
Mai gadi ya wangale gate ,motan kaseem ne ya kunno kai cikin gidan..
Ganin su ba sa ya tashi ko motsawa daga jikin windon ba,sai da suka kai kimamin mintin bakwai da shigowa sannan ya tako ya zauna saman kujeran shim.
Cikin yanayin tausayi kareem yace 'ya daiiiiiiiii...ba mafita ne har yanzun? Gashi saura kwana hudu sati biyu ya cika.
Kai ya girgiza masu kawai.
Kaseem ya nisa yace kun ki bin shawarata,da zaku dauki magana ta ne da sai nace mu tafi gurin mamanta mu fada mata abinda Ilham ke shirin yi...yana rufe baki ,wayar Hisham ya shiga ruri,ganin me kiran yasa shi daure fuska kamar yana gurin.
ya kafa wayar a kunnensa tareda gaishe gaishe.
Daga can bangaren baba lamido ne (Lamido karami)
baya gaisuwa yace wa hisham yazo,yana nemansa yanzun.
Ya ajiye wayar tare yin tsuki.
YA tashi ya shiga dakinsa,ya sauya kaya sannan ya fito.
"Ku tashi kuyimin rakiya zuwa gidan baba lamido..
a gidan baba lamido ya tarar da baba yusuf,yana ganinsu gabansa yace ras!...sabida duk lokacin da zai hadu da wadannan mutanen,toh fa ba wata labari me dadi da zasu fada maka.

BAYan sun sake gaisaw Baba lamido ke fadin ya ya zancen ka da ilham?.
Shiru yayi na dan lokaci sannan yace  mamarta ta amince,amman ilham din ta ki amincewa....

ya tabe baki yace "shi yasa nace ka fita harko kinsu...ga hindo nan .
Ni da sauron yan uwana mun gama magana nan da wata uku za'a daura aurenku.
Cikin shakewar murya,ya shiga basu hankuri..da su hakura da batun aurensa da hindo.
Ai kuwa baba yusuf ya shiga balbala masa masifa.
Kai kasa hisham ke rayawa a zuci cewan mutanen nan basu san abinda ke shirin faruwa da su ba.🤔...a sanyaye yace don Allah baba,ku saurareni.
Su kuwa yi shiru suna jinsa.
don Allah ku bar zancen auren nan sabida abinda ke shirin faruwa a familin nan...kuma kokarina ganin abin be faru ba.
Shashasha......kaji shi da zancen banza! Me ke shirin faruwa? Wani zai mutu ne kokuwa?, ko kuwa idan mun hada ku aure zaka kasheta?..baba lamido ke wannan furucin
Nan dai shiga zazzaga masa maifar irin nasu,daga baya suka tunashhe cewan nan da wata uku aure ba fashi.

Rai bace ya koma cikin mota.
Ganin bacin ransa yasa kaseem da kareem basu tanka masa ba.
kaseem ya ja mota suka tafi.
A gidan hisham ko sai tsuki yake, tun suna daurewa har suka kai ga tan bayarsa abinda ya faru.
Kamar zaiyi kuka yace "mutanen basu isashen hankali😏....da sun san abinda ke shirin faruwa da tunanin hadani aure da hindo ba zai zo masu ba.
natsuwa sukayi suna sauraronsa.
wai fa so suke su dani aure da hindo

Ka fada masu ba ra'ayi mana🤷🏻‍♂...kaseem ke fadin haka.
Na fada masu wallahi....so suke suyi min auren dole.
Toh wallahi idan kayi shiru kai kaso,kuma kai zaka cutu...kareem ya tofa nasa shima.
Da haka dai sukayita banbaminsu har lokacin sallah ya gabato,sukayiwa juna su sallama.

Washe garin ranar da takardun kanfani suka iso hannun alhaji Buba,ya sanar wa sauran mutane..sun kuma shaida masa isowar takardan suke jira,don haka ya gaggauta barin office ya nufi gida don sallamar uwargidansa  zashi tafi abuja.
rakiya tayi masa har zuwa wajen gate inda ya ajiye mota,ganin baza shi dauki lokaci ba yasanya shi barin motan a waje.
ya bude motan don ciro takardun ya nunawa matarsa,sai ya gan ba alaman takardun,ya duba bayan seat din motan,ba alamansa ya koma ya bude bot nan ma babu.😲😧...salati ya shigayi tare da daura hannuwan sa bisa kansa🙆🏻‍♂,Kafin ka sani kayansa sun jike sharkaf.
Read More »

Tuesday 30 January 2018

SOYAYYARMU 32

*SOYAYYAR MU👫*
         By Ganarious.
Page3⃣2⃣

Wannan page din naku ne,mutanen KENYA (NAIROBI)...ALLAH shi barmani ku.🤝🏼

        **      **       **
GAnin bata da niyar tashi,yasa na mike tsaye .
Na mika mata hannu,itama ta miko hannu na daga ta.
Tana tsaye nace muje ki kwanta!.
Ta girgiza kai..
A fusace na kara fadin muje ki kwanta ko!
..."ni gaskiya bazan  iya takawa zuwa dakin ba.
😳Ido waje nace sa "ya ya kenan tau?🤷🏻‍♂
Humm...🤔,sai dai ka goya ni,ko ka dauke ni.
"Raya wa nake a zuciyata ko na shake ta ne sabida takaicin ta nakeji?.
Murya kasa kasa,tace "kar kayi tunanin shakenin ko yimin wani abu fa,! Sabida mutane na kallonmu.
🙄mamaki ya cikani,yanda tasan abinda nake rayawa a raina.
Na matso gab da ita na bata bayana tare da risinawa..amman kuma ban cemata komai ba.
Ta hau bayan na kaita har saman gado.
Na sa lallausar bargon da ke saman gadon na rufe mata jiki sabida dakin ya garwaye da sanyi.
Na zari pilo,na koma saman kujera don kwantawa,sai na ji tana fadin "ka dawo nan mu kwanta
Hasbunallahu wani'imal wakil kawai nake fadi,ba tare da na amsa ta ba.
Ka dawo nan ka kwanta, ko kuma wani abu ya faru yanzun nan ...ta fadi hakan rai a bace.
Nan da nan na mike domin tsoron abin nan da tace zai faru,wata kila ta taramin jama'a gani ba ni da kowa a kasar.

Bargo ta sa tarufe mu ...tare da fadin kar kayi tunanin yi min wani abu".
Sannan ta juyamin baya,ni ma bayan na juya.
A daren ranar ban runtsa ba sai addu'oi nake...domin kuwa ilham ta daina bani mamaki,sai tsoro,sa ran nake tana tare da mutanen boye shiyasa take haka.
 Gab da kiran sallah bacci yayi awon gaba dani.
Ina farkawa muka hada 👀,ni kawai take kallo...zaune take saman kujera ta hade hannayenta tare da rungumarsu,ta daura kafarta bisa dayan..muna yi👀,gaba na yace ras!..a zuciyata ina fadin yo ko me wanna gimbiyar take kunsawa a ranta?
Na lalubo wayata domin duban lokaci,mikewa nayi a hanzarce ganin goma ta wuce,na shiga bathroom nayo alwala,sannan na gabatar da sallah,ranar ta farko kenan da na taba missing sallan asubahi tun tasowana.
Ganin bata motsa da'ga inda take zaune ba,yasa nima ban motsa ba tunda na idar da sallah sai rokon Allah nake da shi tsare ni a duk wani abu da take shiryawa a ranta...yanayinta kawai ya tsorota ni.

Jin motsin mikewarta yasa na saci kallonta,nan da nan ta juyo muka hada ido,nayi saurin dauke kai na.
Bata jima ba ta dawo rike da tire,ta ajiye a gaba na tace "inakwana"!.
Dar'dar na amsa mata da lafiya lau.
Zama tayi,ta dibo abinci ta kai baki na....haka na dunga cin abincin ina kallonta.
Ta gama bani abincin ta umurce ni da na shiga wanka..ban mussa ba nayi yanda tace😄.
Na fito wanka na tarar ta ajiyemin kayan sawa.
Bayan na saka kayan na zauna,ina tunanin yau kuma me take shirin yi.
Muna nan a haka,ba me ce da wani qalah,sai satan kallonta nake,ita kuwa tana gyaran farce.
A haka har lokacin sallah yayi,ta mike tace mu tafi masallaci..bayan mu dawo daga masallacin tayi ordering abinci anan hotel din,ba da jimawa ba suka kawo.
Bayan gama cin abincinmu,ta tashi zuwa inda kayanmu suke ta harhada jikin jakkuna..ta tako zuwa inda nake tace tashi mu tafi..
A raina nace "yo ina kuma zata kaini".
Airport muka nufa,ganin mun bi layin masu zuwa uk,na tsinci kaina cikin farinciki da godiya ma Allah.
Jirgin mu na sauka na ra'ba jiha da ilham..shatan mota nayi,duk da bani da kudi,amman nayi kira abokaina da su fito da kudi su jirani a bakin hostel dinmu.
Daga ranar da muka sauka,duk wani abu da zashi hadani da ilham ina kaudashi,fushi nake da ita sosai,hakan yasa na yanke duk wani mua'ammala da ita....hakan yana bakanta mata rai.
Ta kai gayimin txt,Amman ban amsa mata ba,sabida cike nake da haushinta.🙄
SAti biyu ina avoiding din ta...wataran zaune nake cikin abokaina sai ga ta ta zo gun.ta zo dai dai inda nake tace ashe kudi zai shiga tsakani na da kai...tayi ta surutan ta ba tare da na amsa mata ba..
Tana barin gurin da kamar minti goma,naji text a wayana,a zato na itace...sai da aka dauki lokaci sa'anan na duba wayar..'Bank alert ne' sunyi min refunding kudade na,an maida min da komai yanda yake a baya.
Mamaki ya cikani,na rasa abin ce wa,ina cikin haka text ya sake shigiwa kuma...wannan karon itace.
You've fail'.🙅🏻‍♀.shine abinda ta rubuto.
NAN take hankalina ya tashi,na shiga neman ta a waya amman ba ta dauka..na shiga tunane tunane yanda ilham ta sami kudin da ta maida min a account.
Haka ilham ta cigaba da gara ni kafin,sai da na garu sannan ta hakura muka maida *SOYAYYARMU*

Hisham ya dubi kaseem da kareem yace kunji dalilinda yasa na dage da cewan zata aikata duk abinda tayi niya.
       😄😅😂🤣dariya suka shiga yi masa sosai,tun can da yake basu labarin dariya suke masa.
Ya daure fuska yace idan baku da abin cewa,ku tashi ku tafi,ku barni nayi tunani abinda zan ce mata kafin gobe.
Yauwa!...kaseem ya fada,a yayin da yake nuna hisham,..idan zaka je gidan gobe,ka kira mu mu tafi tare.
Idan ta gan idanunmu dolenta ta saduda,ko kuwa ya dubi kareem.
Haka ne abokina,kasan sarkin yawa ya fi sarkin karfi....

Washe gari bayan sallan la'asar kareem iso daukan Hisham da motansa,daga nan suka nufi gidan su kaseem.
   Sunyi sa'a kuwa domin mamee na gida...ssi da hisham yayi tope-tope😃,sannan suka matsa bell..kareem da kaseem kuwa sai dariya suke masa..
Basu jima a gurin ba blessing ta zo ta bude masu kofa.
Da sallamarsu suka shiga falon,nan suka tarar da mamee zaune.
Tayi masu marhaba da zuwa,cikin fara'a..ta kuma umurci blessing da ta kawo masu abin sha🍷🥂🍸🍹🍾
Wayarta ta dauka tayi kiran ilham wai ta sauko kasa,ba tare da ta sanar da ita su Hisham ne suka zo ba.
A hanzarce ta fito daga dakin ta,sai dai kafin ta sauko sai da ta duba kasan falon tukun sa'anan ta fara taku daddaya,ganin Hisham ya sata ta hada rai.
Sannu a hankali take takowa kuma cikin takama da kasaita...daya bayan daya take sauke kafarya daga steps din,fuskar nan kamar ka gudu,sabida yanda ta hada rai.
Yanayi ya baiwa Hisham tsoro,su kareem da kaseem kuwa a ransu sai cewa suke wannan 'dodo ce'.
A yayinda idon mamee ke kan wayarta,bata san wainar da ake toyaa ba.
Kamshin turaren ta kawai ya sanar da isowar,mamee da dago ta dube ta.
"Sannu da hutawa mamee"..ilham ta fada,tana me shirin zama.
Yauwa sannunki..fadin mamee.
ta juya garesu,suka hada ido da hisham yayi saurin dauke kai.
"Sannunku da zuwa" ta fada cikin sanyin murya.
Read More »

Sunday 28 January 2018

KAZAMACE MATATA Page2

💖💖💖💖
*KAZAMACE MATATA*
        💖💖💖💖
      By Ganarious
Page2

√gaisuwa ga jama'an kontagora.

√kuna rai na Hajiya Fatima A.Bayero, Nazhee yareema😄👍🏼, Amina muhammad(jago) jagoness dita😘

                *****
       *BAYAN SHEKARU*
Tun bayan tafiyar munir kasar Paris, bai tako nijeriya ba sai da ya kammala karatunsa.

Ya tarar da wasu canji  a mutanensa,don kuwa mahaifinsa tsufa ya fara ja,kanwarsa kuwa khadija ta haifarwa alhaji suleiman mijinta ya'ya uku,..kuma ta dauke farida daga gidansu inno zuwa nata gidan,a yayinda shi kuma alhaji suleiman ya sanya Abdulwahab a makarantan kwana....sai dai inno kam tana nan da halinta sai abinda ya karu...
Munir yayi farin ciki tarar da wadan nan canji daman kuma adduansa kenan komai ya zamto daidai.

Ko huta gajiyar tafiya munir baiyi ba...domin kuwa washegari ya kwashi kwalifications dinsa ya nufi government house da su don neman aiki.
Ganin kwalifications dinsa yasa basu bata lokaci ba,suka bashi aiki dakuma babban matsayi lokaci guda....sunyi hakan ne sabida sun jima suna neman me irin fasahnsa a fagen naurorin komfuta,don haka basu son ya kubuce masau.

Allah ne me bayarwa! Allah ne ke nufan ka da Arziki,Allah ke daukaka bawan sa..ya kuma yi wa  engr.munir wadannan ababen da na lissafo.
Lokaci kadan ya budewa munir hanyoyin arziki,ya kuma daukaka shi..
Ta ko'ina kamfunoni masu zaman kansu sukan so ace dasu munir yake aiki,amman haka bata yiyuwa,sai dai idan suna da matsala fanin saita masu komfuta,ya kan taimaka a biya shi.

Engr.munir ya gyara gidan iyayensa, ya sa kannensa a makarantu ta kudi sa'anan ya baiwa matar ubansa inno jari.
Haka engr.munir bai bar yan uwan mamansa da suke kauyen dakin gari ba..yakan je masu ziyara ya kuma kai masu abin arziki.

Bayan ya gama da iyayensa,duk da ba'a gama hidiman iyaye..ya ginawa kansa gida.
Gidan engr.munir gida ne  da sai ka zagaye fa'din birnin kebbi baka gan irinta ba ko ma shigensa ba.
🏡 engr.munir ya zama *Topic*a gari,ya zama abin magana  da kwatance, yan👱🏼‍♀🧕🏻🧝🏻‍♀👩🏻‍💼 kuwa sai mafarkin shiga gidan suke..uwa'uba,idan sun gan shi kansa me gidan..subhanalillah,sai kiji suna fadin dama ni zai aura ya saka ni a wannan gidan nasa,wata kuma tace ita tafi dacewa dashi da gidan sa..da dai sauransu

Haka yan matan birnin kebbi suka rinka ciwon kai sabida son kasancewa da engr. Munir,...ba yan matan kebbi kadai ba,duk garin da yaje sai yan mata sunyi rubibi a kansa..
Munir ya zama celebrity ga kwarjini,duk inda ya taka jama'a maza da mata na son kusanci ko abota da shi..yan matan social media kuwa sukan baro garinsu su zo birnin kebbi ko Allah zai sa suyi dacen ganinsa.

Ganin ya ajiye komai na rayuwa amma ba mata yasa yan uwan marigayiya mahaifiyarsa sunyi kiransa suka yi masa zancen aure,yayi masu godiya da alkawarin zai yi auren nan ba da dadewa ba.

Munir ya kasance yana neman mace mai tsafta,mai ladabi da biyayya,me kuma tsoron Allah wace zata tallafawa rayuwarsa, ta kuma bawa ya'yansa da zata haifa mashi tarbiya.
Tsai da mace yayi masa wuya,sai yake ganin kamar samun macen kirki a zamanin nan zaiyi wuya...ransa na bashi duk wace zata so shi don wani abu nasa zata so shi ba don Allah ba.
Yan mata kuwa da yake tunkara,nan da nan su sadaukar da komai nasu gareshi,ga rawan kai da rawan jiki,ba ko dan aji,hakan ko baya birgeshi.

Haka munir ya cigaba da neman mace tagari,a ransa kuwa cewa yake mata masu aji sun kare ne!...

          **   **     **.
Duk ranar jumma'a  idan an sauko daga masallaci gidan babansa yake wucewa.
Yau ma hakan ta faru,can ya nufa bayan an sakko sallar jumma'a.
a waje ya hadu ba mahaifinsa,suka gaisa.ya karasa cikin gidan nan ya tarar da inno tana fadi in fadi da diyarta habibatu,sai masifa take yi muryar ta na tashi.

Habiba na ganin munir tayi shiru,domin kuwa duk fadin duniyar nan ba wanda take shakka ko girmamawa kamar munir...shima kuma yasan da haka.
Ya baiwa inno hakuri yayiwa habiba nasiha da ta daina hakan.....
Yayi mata sallam zai tafi sai kuma ta tsai dashi,ya koma ya zauna yana ssuraron ta,a daidai lokacin mahaifinsa ya kunno kai ya shigo dakin da sallamansa.

"Yauwa malam,gwara da Allah ya kawo min kai,"
Cikin anashuwa yace tau tau tau...ta samu ne.?
Daman  wannan dan ,ta nuna munir da yatsa,   na samowa mata!...na gan alamar bashi da niyar bamu jikoki mu mora!
SHiyasa a matsayi na na uwarsa  nagan dacewan da na samo mashi mata..ko yaya ka gani?
Cikin jin dadi tare da wage baki yace " hakan yayi dai dai,kin kyauta.Allah shi saka maki da alkhairi...ya dubi munir da kansa ke kasa tunda ta fara magana yace kana jin abin alkhairi da inno tayi maka kuwa?.
Murmushin dole ya kago domin kuwa maganarta ta sanyai shi zazzabi.
Ya dago kai..yayi mata godiya.

Yauwa Allah shi yi maka albarka, ta fada sannan tace masa "idan ka tashi sai kazo isah ya yi maka rakiya zuwa gidan su yarinya,sunanta SUWAIBAH..ni da mahaifiyarta mun gama magana,saur su malam.

Daga gidansu,gidan su alhaji suleiman ya nufa.
Zaune ya tarar da su,a yayin da khadija take gyara masa farcenta.
Suna gama gaisuwa kahadijah ta dubi shi tace yaa munir lafiyar ka lau kuwa?
Me kika gani?..shima ya tambayeta
Ni ce fa khadija,na san yanayin ka idan kana cikin ko wani hali...kallo daya zanyi maka nasani.
Dariya alhaji suleiman yayi yace tau kalleshi ki fadaman yanayin da yake ciki

Ahhaaabb.....yaa munir cikin damuwa yake wallah..tana fadin haka tamike ta shiga kitcen
Ta fito rike da tire,ta jawo stool ta ajiye a gaban yayan nata tace masa bisimillah yaya.
Read More »

Saturday 27 January 2018

SOYAYYARMU 31

*SOYAYYARMU👫*
   Written by Ganarious.

👉🏼Annabi(s.a.w) ya kasance yana bude addu'arsa da *SUBHANA RABBIYAL ALIYIL A'ALAL WAHHAB*...Ahmad da hakim ne suka ruwaito shi daga maslamata dan akwa'i(r.a)

ganarious.blogspot.com/ ki shiga nan din ki duba yanda zaki gyara gashi da yin maiyukan gashi da kanki...nagode🤝🏼

3⃣1⃣
Ihu nakeyi,ina fadin noooo...no,nooo please don't do this to me.

Yana kaiwa inda nake daya daga cikin su ya zo a guje tare da dakatar dashi.
Yare suke ta yiwa junansu,ni dai ban fahimci abinda suke nufi ba,sai kawai binsa nake da ido.
Suna gama maganarsu suka fashe da dariya har shi me rike da takobin.
Nayi ajiyar zuciya a yayinda nake hamdalah a zuci.

Shi wanda ya dakatar da me takobin,ya karaso gaba na ya kama min hannu wai muje,da shike shi yana jin turanci...mu tafe yana min hira tare da fadamin sunansa...nan na tambayeshi yanda akayi na tsinci kaina anan.
Dariya yayi sosai yace "idan ka koma inda ka fito za'a sanar da kai.".

Tafiya muke ba kaukkautawa,munyi tafiyar da ta dauke mu kamar minti arba'in da takwas,ba mu hadu da mashin ko mota ba.
sai da muka bulo babban hanya sa'anan catapila ya zo wuce wa don haka macheal ya tsai da shi muka hau...yare yayi masa shima,da alama ya fadama sa inda zamu saukane.
Ganin mun shiga wani kauye ya sa na fara jin sanyi sanyi...
 Muna sauka meacheal ya nufi filin jirgin kasa dani muka shiga harda shi.
Awan mu shidda a hanya ga yunwa a tare da ni,ga salloli a kaina...muna cikin tafiya na tambayi mecheal wani gari ne nan?..yace min nan kasan Philippine ne.
Ido waje nace philipphine?
Yace eh...
Sai a sannan na tuna "bet" dina da ilham.

Mamaki ya cikani yanda akayi ilham ta kawoni kasar philippine..yaya akayi haka ta faru bani sani ba🤔!.. sai dai idan maganin bacci ta bani🙄

Babban birnin Manila muka sauka,watau capital din philipphine din kenan..muna sauka mecheal yayi kiran waya bayan ya gama magana a wayan ya jani zuwa wani gefe yace mu jira kadan.
Muna nan wata mota ta zo,don haka yace mu tashi mu shiga motan  a kaini masallaci nayi sallah..nayi masa godiya nace kamar kasan abinda nake tunani kenan.
masallaci suka nufa dani,sun kuma jira har na idar da salloli na, sannan suka nufi wani gida dai,ni dai sai bin su kawai nake amman a tsorarce nake.

Gidan kamar guest inn ne,muna shika nunamin toilet wai na shiga na hanzarta yin wanka sabida jirgin da zani shiga zai tashi nan da awa daya.
Ba nemi sanin inda kuma  za su kaini ba na shige toilet don yi wankan...sai a lokacin nake tunawa da wayata hakan yasa na sanya hannuna a aljuhun wando don ciro wayar ,ba waya a ciki sai wata yar gutun takarda me dauke da rubutun ilham tana cewa "da fatan kana jin dadin yawon?

Na fito wanka na tarar da su ajiye min abinci,sai dai abincin ba irin wanda zani iya ci bane,don haka na tsattakula na bar sauran a gurin.
Daga nan manila airport muka nufa.
Cikin dare jirginmu ya tashi ba tare da nasan inda muka dosa ba,addu'ata dai Allah shi sa london zani koma.

Ganin ba airpot din da na saba sauka bane ya sa na kariya..araina kuwa nace "ilham kin cuceni".

A hankali nake taku zuwa inda aka tanadar don tarbon matafiya..gaba na sai dukan uku-uku yakeyi sabida ban san inda zani dosa ba kuma idan securities ko polisawa suka lura da hakan,zasuyi zaton wani abu su kama ni,gashi bani da wata shaida ta shiga kasar,ba i.d card ba komai..Allah yasa jirgin ta yan kasuwa ce da masu bincike sun tsai dani.
Mutane sai tarban yan uwa da abokan arziki sukai ni ko ba alaman wanda na sani a guri,haka na cigaba da tafiya kamar hawayniya..wata yar budurwa ce ta taba ni,tace lafiyar ka kuwa?..maimakon na amsa ta sai nake tambayarta wani gari ne nan.
Huhh...ta fada ayayin da ta fiddo😳 idanunta waje  tana me mamanki tanbayata..
Kana nufin kacemin,baka san kana a dubai bane?..

oohps🤦🏻‍♂....sorry ba tanbayar da nake son yi maki bane kenan..
Tayi shiru tana jiran na tanbaye ta,rasa abin tanbaya nayi don haka nayi mata sallama kawai.
Sololo...tayi tana me kallona,nidai nan na barta,kafin ta tara min jama'a.

Ina barin gurin na hango kamar sunana,da sauri na tafi gun tabatarwa,..hakan dinne sunan ne rubuce barou  barau a katuwa takarda an daga shi sama,sai dai takardan ta rufe rabin jikin wanda ke rike da shi don haka ban gan ko fuskar ba...a rai na nace toh ko wa zani hadu dashi kuma?
Ina isa gurin nace "hi"
A hankali aka sauke takardan.

Ilham ce tsaye..tayi wurgi da takardan ,ta daka tsalle sai saman jikina...ta shiga sumbatata..,niko sololo nayi,ina dubanta.
Dariya takeyi sosai tare da rikemin hannu muka fito wajen airport inda ake ajiye motoci.

A zatona zatayi shatan motane,sai ganin nayi ta bude min gaban mota ta umurce ni da na shiga ita kuma ta zagaya gefen direba ta shiga...mamaki ya cika ni,yaushe ilham ta san dubai da zatayi tuki a gari...kai wannan tana tare da yan boye.
Kallona tayi ta fashe da dariya,tana fadin lots of talks ko?
Ban amsa mata ba sai kallonta kawai da nake.

Wata katuwar hotek ta nufa,wanda idan nace zan kwatanta maku kyau da tsarinsa tau fa sai gobe ko jibi zani gama baku labarin,muna shiga haraban hotel din tayi parking ta fito tareda zagayo ta gefe na ta bude min kofa,ta rikemin hannu na fito muka shiga ciki.

Cikin hotel din ma abin kallo ne,dakin da ta shigar dani kuwa ba'a cewa koamai...tsaye nayi ina waige waige,ta karaso inda nake ta rungume ni gammm..kamar ance mata za'a raba mu ko za'a sace ni.
Kan ta na saman kirji na,sai fadin take "i missed u,i missed u alot.....mun kai kamar minti shidda a haka,hannu na sa na cire ta daga jiki na ina me kallonta cikin ido..

TA fashe da dariya irin ta cin nasaran nan .banda kallonta ba abinda nake cos i was speechless..
ta sa yatsarta saman lebena tace "shiiiii🤫......I know  it all,u don't have to say it.
Sai lokacin na sami karfin yin magana.na ce da ita"ya'ya kikayi haka ilham"?

Ta sake yin dariyan..."kar ka ce komai".
Nop....ki fadamin yanda kika yi,na wayi gari a kasar philipphines,da kuma wadanda suka taimaka maki.
Dariya tayi tace, bazan ce maka komai ba yanzun,don haka dont ask..tana fadin haka ta mike. Sai ga ta ta dawo rike da wayana da kuma wallet dina,da sauri na karba wayat ...ta shiga dakin kuma ta fito.."tashi kayi wanka,ba tareda na amsa ta ba,na mike ina biye da ita har bathroom din,...zan ajiye maka kayan sawa asaman gado,idan ka fito ka sa..
.
Bayan na fito wanka na sa kayan,tsaye nake gaban madubi ina me kara kallon kaina,..budo kofa tayi ta shigo.
Wow..looking sweet ba laifi,ta karaso ta sumbace ni a kunci na,tareda rike min hannu muka fita.

Na cigaba da mamakin ilham,sabida sai da muka yawo ce kwatan garin nan,da farko Burj khalifa park muka fara zuwa,sannqn muka nufi down town da uptown, muka nufi desert safari,..anan take ce mani  ko ta sake batar dani ne nan...shiru nayi ina kallonta.
Ta sa hannu daga goshina zuwa kasan hanci na tace ko bazani iya ba?👱🏼‍♀....zaki iya wallahi🙄nace da ita..
Daga nan muka nufi fairy tale palace,hotuna kawaai mukayi anan sa'anan muka nufi masaukinmu,shima din sabida mangrib ya karaso ne.
Masallacin da ke cikin Burj khalifa hotel muka nufa,da shike akwai sashen mata...ba mu koma daki ba sai da mukayi sallan isha'i.
A falo na yadda zango,ita kuma ta shiga ciki tayi wanka ta fito.
Zaune nake ina operating wayana,sai gata..ta zauna saman kafafuna tare da kwantowa da jikinta saman nawa jikin.
Duk jiki na a mace yake,na kasa magana sai binta nake da ido.
.ta kawo bakinta setin kunnena ta radamin "idan na fada maka abu ka yarda kawai,don't doubt it"...abinda naso nayi maka ya fi haka,amman i dont want to miss....ta mike,ta taka inda rediyo yake a ajiye ta kuna wakar celinedion....duk dai idona na kanta,ta zo gurina ta rike min hannu tana fadin tashi muyi rawa..
Kallonta nake,ba tareda na tashi ba.
Ka tashi mana!!....ta sake fadi.
Nan ma ban tashi ba,ta bata rai tace wallahi zan sa a kullemin kai yanzun.
Da saurina na mike....sabida tuno maganar da ta gama rada min a kunne yanzun.😅
Dariya ta shiga yi tana fadin kace bani iyawa mana.
NA Girgiza kai nace kina iyawa ilham.

Muna tsakiyan rawa,tace daga yanzun sweet -moon din mu zai fara..ko ka manta na ce maka zamu zo sweet moon?.
A'a ...kawai na fada.

SAI da ta gaji don kanta sannan ta ce mu zauna...
Kwantar da kanta tayi saman kafafuwana....ilham kamar 🐈 take,akwai son jiki.
Muryana can kasa kasa na ce da ita,ina bukatan kiyimin bayani daga likacin da kika bani sweet din nan zuwa yanzun.
Tayi murmushi trace bayanin me kuma?.
...hmmmm amman dai kin bani kunya!,basiran kenan batar dani ba cikin hankalina ba?
Mikewa tayi zaune tana kallona tace wa ye fada maka,ba cikin hankalinka kake ba.?.
Eh mana ,sai da kika bani wani abu tukun.
Hummmm...hisham kenan, ok,lets do it this way,tunda ka kasa tuna komai,ka duba wayatka zaka gani..kuma yanzun tunda kana cikin hankalinka mu sake wata "bet din".
A'a nace da ita,ina me girgiza mata kai.
Murmushi tayi tace ka ji tsoro kenan.

Naji...naji tsoro din.yanzun ki fada min inda kika sami kudin nan da kike watangale dashi.
Ina na samu?
na daga mata kai,eh ina kika samu.
Ba wani kudi bane face kudin da ka bani mana.

Cikin  rudewa nace nace yaushe na baki kudi?😳.
Kai fa kace na kwashe duk kudin da ke account dinka sabida deal din yayi alrmashi.

Ban tsaya sauraronta ba na hanzar ta bincike ta wayanaa.
tsullll namike tsaye ina salati,ganin babu ko sisi a account na,ta wawushee komai.

Zufa ke karyowa ta ko'ina  a jikina,cikin yanayi tashin hakali nace "yaya kikayi ilham"
ta tabe baki tace ,kai fa kace na kwashe kudin,kuma dashi nake komai na deal dinmu,jirgin da ya kaika philipphine jirgi ne ta yan kasuwa,mu kadai ya kwasa,ya kuma maidani a ranar,ka gan kenan dole na biyasu kudinsu,wayanda sukayi yi maka komai ma a can,sai da na biyasu.,zuwa dubai dinka,wannan hotel din da muke ciki duk a cikin kudinka ne.

Salati na shiga yi,na sulale zaune,kai na rike ina tuna nin yanda akayi tasan passcode da secret number dina,wanda shike ban fadawa kowa ba sai mahaifiyata.

Mun dade zaune ba wanda yace wa wani qa'lah.
zuciyata kuwa tam take da takaicin ilham.
Mikewa tayi tana fadin tashi muje mu kwanta dare yayi...wani irin kallo na jefe ta dashi me dauke da sakuna,a raina kuwa kamar na shaketa..
TA kara magana karo na biyu,
na girgiza kai ina fadin bazani iya kwana daki daya dake ba.
Sabida me,? Baka yarda da kanka ba kenan.
Shiru nayi ban amsa ta ba.
"Ka tashi mana muje"..ta kara faDi.
A hasale nace jeki ki kwanta,ni bazani kwanta daki daya dake ba.
Tayi fushi,ta koma ta zauna tana cewa ni ma bazani iya kwana a dakin ni kadai ba
Read More »

Friday 26 January 2018

KAZAMACE MATATA 1

💖💖💖💖
*KAZAMACE MATA TA*
       💖💖💖💖
Written by A'isha m.Gana
         (Ganarious)

√godiya ga Allah (s.w.a),da ya bani ikon rubuta wannan labarin.

√sadaukawar ga kanwata abin alfarinmu HADIZA MUHAMMAD GANA,karamar "yar sanda ta kasar najeriya..your inspiration shall reign.

√gaisuwa ta musamma ga makaranta har da marubutan.

√princess UMAYMAH BASHIR GWANDU,na mika gaisuwarta ga ma'karantan SOYAYYARMU.

√ina  marhaba da comments dinku,gyare-gyare,ra'ayinku,da dai sauransu a 👉🏼 ganarious.blogspot.com/ na gode🤝🏼

      **        **      **
Munir dogone,shi ba fari bane, ba kuma za'a ce masa ba'ki ba...yana da idanuwa masu girma,ga eyelashes dinsa cike kuma da tsayi.
Kana iya hangen daga inda karan hancinsa ta fara,lebensa kuwa ba'a maganarsu..sajensa ta faro da'ga gefen kunnensa ta zagayo ta kasar bakinsa, zuwa dayan gefen kunnen..
Yana magana gefen kumatun sa na lotsawa ciki.
Karya ne munir yayi magana baka sa masa ido ba,yana maganar yana lausaya idanunan nasa kamar me jin bacci...munir perfect example da yan mata suke mafarkin samu, suke kuma kira da *my dream partner*,ba wace zata kalli munir bata raya a zuci cewan da" ace itace the lucky lady ba..nima din me bada labarin sai da na kyasa😜.
Munir zai kai kimamin shekaru talatin da daya-xuwa da biyu da haihuwa.

  Mahaifiyarsa ta rasu tun yana shekara goma sha hudu, shi da kannensa uku ta bari a gun matar ubansu...munir da kannensa sun dandani kuncin rayuwa daga gun matar ubansu wace suke kira da inno..
Wulakanci,cin zarafi da mugunta ba irin wanda basu gani ba,inno bata kaunar ganin suna farinciki ko da na sekan ne,sai dai su kasance cikin bakin rai da bakin ciki,sai dai me,Allah yayi wa munir da kannensa hakuri.
Munir jarumine,duk da ababen da yake fuskan ta bai sa shi ya kariya ba,gwagwarmaya yakai,   dafi tashi don  ganin shi da kanensa sun sami ingantacen ilimi.
Munir bashi da daki a gidan ubansa,bashi da abinci a gidan ubansa bashi matsayi a gidan ubansa,amman wadannan ababen ba abinda suka dame shi ba ne,asalima idan ya tashi da safe,yayi wa inno share share sai ya fita gari neman inda zaiyi shara,ko wanki ko dai wani aiki a biyashi,idan ko ya dawo da kudin aikin sa gida,sai inno ta kwace..
Ganin haka yasa shi dabaran raba kudin gida biyu, rabi ya baiwa mahaifin abokinsa ajiya,rabin kuma ya kawo gida.

Munir na kammala makaranta ta sekandiri,ya sayi fom din makaranta ta gaba da kudin da yake tarawa...cikin sauki kuwa ya sami karbuwa a makaratar,amman mahaifinsa ya hana shi zuwa,wai bashi kudin bashi..munir ba kariya ba yace wa mahaifin sa shi zaya dinga nema wa yana biyawa kansa kudin makaranta..
NAn ma bai amince ba,wai inno tace idan shiga makarantar baza shi dinga kawo mata kudi ba..domin kuwa kudin da zaya dunga kawo mata shi zai kashe a makarantat...
YAYi kuka,yai bakin ciki da'ga baya ya roki Allah ya yayi masa alkhair.

Daga munir har mahaifinsa hadi da kannensa tsoron inno sukai, suna matukar shakkarta, sai dai ya'yanta da ta haifa basu shakkarta,masifarta ma baya basu tsoro, asalima fadi na fada takeyi da su,ba ta magana basu maida mata ba.

Haka munir ya cigaba da rayuwa a gidan,ya na fadi tashi don ganin ya nemawa kansa da kannensa.

  Alhaji suleiman shine mutumin da munir yake zuwa gidansa tun da sanyi safiya,ya share masa gida,ya zub da sharan gidan sa'anan ya wanke masa motarsa...ba gidan alhaji suleiman kawai munir ke aiki ba,akwai gidaje da dama da yake masu aiki,amman gidan alhaji suleiman yake fara zuwa.

Alhaji suleiman ya y gama karance munir..ya lura munir me tsoron Allah ne,komai tsakaninsa da Allah yakeyi,gashi da tsafta.
   Watarana bayan munir ya gama aikinsa,yayi sallama a falon alhaji suleiman,ya amsa tare da umurtansa da ya shigo.
Ya shiga ya sanar wa alhaji suleiman cewan ya kammala aikinsa na ranar.
Godiya alhaji suleiman yayi masa,sa'anan ya umurce shi da ya zauna suyi wata magana.

Alhaji suleima ya sake yi masa godiya sannan yace na fahimci kai mutumin kirki ne me tsoron Allah kuma..ko kasan da cewan kudaden da nake bari a mota da gan gan nake barinsu! Sabida na jarabta ka,kuma ka sha ka tsallake jarabawan..a gaskiya na yaba da halayyenka,domin abin koyi ne kuma da misaltawa...
Ga ka da tsafta,tunda ka fara yimin aiki gidan ya canza,ga ka baka shiga shirgin da da ba naka,infact halayyenka is perfectly ok wallahi
Munir ya ji dadi sosai,duk da ba yau ya saba jirin irin haka ba..don haka yayiwa alhaji suleiman godiya.
Alhaji suleiman ya cigaba da fadin zan so na sami mata me irin halayyarka.
Murmushi munir yayi bai ce uffan ba.
    Allah da gaske nake fa...idan kana da kanuwa me irin halayyanka,please ka hada ni da ita na aura..
Mata ta,ta rasu gurin haihuwa ta barmin yara uku..tun bayan rasuwarta nake neman koda me kwatankwacin halayyanta ne amman ina! Matan yanzun sai a hankali..ba wai ban sami macen me halin kirkin ba,no..no.no,kawai ina son wace zata bi dokata,ta kuma rikemin yara na tsakaninta da Allah.
Ina son mace me tsoron Allah,kuma me tsafta,wace kuma zata zauna a gida,nufi na anan shine bani amincewa mata ta ta dunga aikin gwamnati,..mata ta da ta rasu,digirin ta uku wanda shike ma bani dashi amman ta bi doka ta,ta zauna zaman baiwa ya'yana tarbiya..yanzun kam wace zata tara irin kwalifications nata ta amince da irin doka ta? Da wuya ko nace babu.
Don haka macen da zata zauna a gida nake so.
 Shiru shiru munir  baiyi magana ba,hakan yas alhaji suleiman ya sake yi masa magana.
Ajiyar zuciya yayi yace inada kanuwa wace na tabbata halayyenta sunfi nawa kyau da ban sha'awa...amman...nan yayi shiru
Ahaji suleiman cikin matsuwa yace,amman me? Zata aure wani ?

Ya ka'da kai yace a'a,..bata da isashen ilimin,matar uban mu bata barin ta zuwa makaranta,sai sa'a da sa'a..nan ya sanarwa alhaji suleiman irin rayuwar kunci da suke fuskanta.
Cikin tausayawa alhaji suleiman yace' wanan na daya daga cikin dalilin ya dayasa,na natsu ina neman mace ta gari,ba wace zata zo ta sa yarana cikin wani hali ba....mata abin tsoro,yanzun kiri-kiri ta hana ka zuwa makaranta sabida wata yofin dalilinta.
Munir ya da'ga,yana me jin abin a ransa.

Alhaji suleiman ya nisa ya ce shikenan,dama akwai wasu fom dake gurina wanda gwamnati ta bayar a bawa yara masu kokarin gaske,amman kuma wadanda iyayensu ba su iya dauka nauyisu..don haka gwamnati zata dauki nauyinsu zuwa kasar waje karatu..don haka ka kasance cikin,shiri sabida zakuyi jarabawa har sau uku,kunayi ana tace wasu daga cikin ku.

Munir yayi godiya sosai yana farincikin haka.ya mike yana yiwa alhaji suleiman sallama.
Ya tsaida shi ,yace masa ya jira shi su tafi tare,sabi da yau dinnan yake son ganin khadijah.
A kofan gidansu alhaji munir yayi parking,daga nisa munir ya hange ta,ya nunawa alhaji suleiman ita yana fadin ga ta can tafe ma..
a natse take tafiyar,ita ma din doguwa,kyakyawa da ita. Banbancin da munir shine  bakar fata ce da ita...
Alhaji suleima ya gama dubanta kaf! Kafin ta karaso.
kiranta munir yayi,ta waigo sai ta nufo su, da fara'anta ta gaida alhaji suleiman sa'anan tacewa munir "yaa munir gani.
Mekika sayo?
na sayo gari ne...ta amsa,
Tau shiga ciki,nima zani shigo yanxun.

Munir ya juya ya kalli alhaji suleiman,yace ka ganta nan,itace khadijan.

Alhaji suleiman yayi ajiyar zuciya yace ,na ganta kuma tayi min dari bisa dari.....ka fadamata bukatata,idan ta amince sai nazo ganin mahaifinku.
daga nan sukayi sallama,alhaji suleiman ya mika masa kudin aikinsa na ranar,amman munir ya ki karba.
A daren ranar munir yayi kiran khadijah zuwa gefen gidansu,nan yake sanar da ita yanda sukayi da alhaji suleiman.
Tayi matukar farin ciki, addu'arta a kodayaushe Allah ya kawo mata karshen zaman ta a wannan gidan don haka tayi hamdala tare rokan Allah shi tabbatar da auren.
ganin alhaji suleiman mai maiko ne yasa mahaifinsu munir jin dadi don haka ya amince.
ba'a bata lokaci ba akayi komai da komai na auren.

An daura auren alhaji suleiman da khadijah, don haka amarya ta tare gidanta...ba abinda takeyi,sai yiwa Allah godiya da yarabata da gidan kunci,kannenta da ta baro can sune kawai damuwarta.

Munir ya dauke kafa daga gidan alhaji suleiman,aikima ya daina yimasa,sai dai ya shiga gari yana neman gidan da suke son ayi masu wanki su biyashi.
bayan haka,munir ya dage da karatu da kuma addu'a,yane me rokon Allah da ya bashi sa'a.

ALhamdulillah,anyi jarabawan gwaji har sau uku,kuma cikin ikon Allah,munir ya tsallakesu don haka yana daya daga cikin masu zuwa kasar paris.
sai da komai ya kammala na tafiyarSa,sa'anan ya sanarw mahaifinsa komai da komai,mahaifinsa yayi murna sosai tare da yiwa  alhaji suleiman godiya, ita kuwa uwar mulkin sai mita takeyi,wai wa zai dunga samo mata kudin chefanne... kaji min mata fa🤷🏻‍♀,ga ta da yara!

Da haka munir ya tafi kasar paris karatu.
Sai da yayi hawaye ranar  tafiyarsa sabida kannesa farida da Abdulwahab da zai bari,sai dai ya barwa khadijah amanarsu.
Read More »

Thursday 25 January 2018

29-30 of SOYAYYARMU

*SOYAYYARMU👫*
           By Ganarious
Page2⃣9⃣
👉🏼Annabi(s.a.w) yace "sunan Allah mafi girma wanda idan aka roke shi dashi yake bayarwa,yana cikin wannan ayar: *kulillahumma malikal mulk*" surah Al imran,26:...Dabarani ne ya ruwaito shi daga dan Abbas(r.a).

Gaisuwa ta mussaman ga masu karatun *SOYAYYARMU*,.ina me marhaba da COMMENTS, dinku ko opinions ko gyaregyare a Ganarious.blogspot.com/    Nagode🤝🏼🙌🏼

          **        **       **
Mama.!Mama!! Mama!!! Kawai nake kira,Babana kuwa jarumi ne,domi kuwa yayana yana parkin ya fito ya bude gefena zai dauke ta baba ya dakatar dashi sai ce mashi yayi shiga mota mu koma gida.
Cikin da'ga murya yace sabida me Baba!,mun iso asibiti sai kuma kace a komar da ita,alhalin ko bude ido batayi.
Shiru baba yayi,a lokacin shi kuma yayana yana kokarin fito da ita zai dauke ta zuwa cikin asibitin.
Babana ya sake umurta sa da ya shiga mota,a koma gida...sai a lokacin ya fahimci me baba ke nufi da hakan,don tabbatarwa ya kunso kai dai-dai gun fuskarta ya kiran Mama.! mama!!...mama don Allah ki karya tashi,bude ido ya gani..sai jijjiga ta yakeyi yana surutai tare da fashewa da kuka.nan nima na fahimci abinda ke faruwa...na shiga yin kuka sosai ina me nadama..
wata sabuwar kuncin rayuwa na sake shiga,mutuwar mamata ta tabani sosai...gashi yannena da kanina al'ameen sun tsaneni,wai ni na kashe mama,don haka ba abinda ke hadani dasu sai Allah shi isan masu...
..kowa ba cewa yake bakin cikina ne ya kashe mama,duk sun juyamin baya..ba su kaunar ganin na.hatta hajiya bata sake min fuska kamar da.
Babana sai yarana kawai suke harka dani

A kodayaushe ina kunshe a daki,banida aiki sai kuka da nadama,gashi baby Muhammad kullum cikin kuka yakai,sabida bai saba dani ba sai mama da baba.
Haka na ci gaba da zama  cikin kuncin da hantara.
Yan uwan mama da suka ji ciwon zuciya ne ya kashe ta,sukayita Allah shi waddai da halina na rashin jin magana.

Ako da yaushe bani da aiki sai kuka da kuma sa ran ko mamata zata dawo,domin na bata hakuri ta yafe min...hakan yasa na fara surutai kamar me tabon hankali,ganin ina neman zaucewa ya sa babana ya daukeni muka je ganin likita.
Ya sanar wa Babana ,lafiya lau nake amman fa idan har na cigaba da haka har zuwa wani lokaci tauuh fa sannu a hankali zan fara hauka,don haka yake bada shawaran ayi me yiyuwa.
A daren ranar Babana ya zaunar dani cikin kwantar da murya yake maganar..
"Haba Aisha..! Ki tausayamin mana! Ko so kike na bi mamarki?
Da sauri na girgiza kai ina fadin a'a Baba..kai kade ka ragemin,don Allah kar ka wuce ka barni.
yayi ajiyar zuciya "ki saki jiki,ki koma kamar yanda kike a baya,ki daina takura kanki da tunane tunane kinji ko.
Na daga masa kai.
Jin dadinsa ya bayyana a fili,ya kara fadin "kiyimin alkawarin cire fillo a rayuwarki,ki manta shi..nasan hakan zaiyi wuya amman ki kokarta kinji?
Na sake daga masa kai.
Yace yauwa me sunan mamata.
Daga wannan lokacin na fara kokarin sakin jiki tare da ganin na dawo dai-dai...
Yannena da kanina da suke nunamin tsana,Baba na ya zaunar dasu yayi masu fada,ya kuma tunashe su matsayi a gunsu sa'anan ya fadamasu lokacine yayi shiyasa mama ta tafi,don haka idan zun cigaba da nunamin tsangwama toh fa dan Allah suke shi da ya dauki abinsa.

Abin da wuya,amma alhamdulillah,...na fara komawa,mutun..matsala dayace baby muhammad da idan ya fara kuka baya jin lallashi,don haka kukan sa kan tuno min mamata,sai ni ma na kama kuka ina zancen zuci tare fadin "da mama na nan da za tayi ka za" da mama na raye da zatayi masa wannan da wancan" haka dai nake har na fara saba wa.

Bayan rasuwar mama da kamar shekara daya da rabi,..na fadawa Baba na cewan inason na nisanci gida,sabida wasu ababe da sukan dawo min sabo wata sa'ain.
Ina kike son zuwa? Ya nemi sani.
Da so samu ne na tafi American,can din ma ba wai zama zani je yi ba,karatu nake son naje na karayi fannin ilimi,ka gan da haka idan na dawo,sai na nemi aikin koyarwa..idan har ina zuwa gun aiki a koda yaushe bazani rasa abin yi ba hakan zai kawar min da zaman tunane tunane..
kwarai da gaske!..Babana ya fada cikin farin ciki..da alama maganar ta matukar sanyi farin ciki.
Ba'a bata lokaci gurin yimin abinda ya kama ta ba,don haka shirina ya kammala,na kwashi yara muka tafi kasar turawa sai mai aiki me suna Blessing da aka hadani da ita zuwa.
Allah da ikonsa da taimakonsa na gama karatuna na dawo gida,a zaton Babana a gida na na estate zani zauna don haka ya sa akayiwa gidan gyare gyare,aka sauya komai na gidan..nayi wa Babana godiya tare da fada masa yayi hankuri ba zani zauna a wannan gidan ba don haka ya bani daya daga cikin gidajensa,a yanzun haka cikinsa muke.

Mamee ta dago tare da dubansu,tace wa Hisham "ba wai naki kabane,ko wani abu,ba ni dai son ina harka da mutanen nan ne kawai"...tayi shiru na dan lokacin sa'anan tace "kuyi aurenku,Allah ya sanya albarka."..ta mike zata tafi daki,nan tayi karo da blessing ido jajir tasha kuka ma'ishi.
tayi  kalleta tare da yin murmushi ta shige.
Kuka takeyi sosai....
Hisham ya tashi ya koma  inda take zaune,ta dubeshi cikin ido tace "why...oh why..!..meyasa sukayi mata haka? Eyeeeh.meysa?
Tana fadin haka tana kuka me ban tausayi,
Hisham ya rungumeta ta yi lamo a kafadarsa,tana kuka, yana shafan gashin kanta.
sai da tayi ya isheta,sannan ta dago tare da daure fuskarta..tace "wallahi sai na dau fansa"...yanda ta dandani kuncin rayuwa sabida su,wallahi'azeem sai nasu ya ninka nata,mahaifina kuwa sai yayi da nasanin barin don wata.!ita kuwa hajiya zubaida! Soon,and soonest zata gwammaci lahira da duniya.
Da sauri hisham ya rike ta yace haba ilham! Abinda ya wuce ai ya wucen ne..please let it be.
Ta fizge hannunta da karfin gaske tare da kara murtuke fuska tace"kaiii....dont tell me that!,idan baza ka iya taimakamin da komai ba,tauh kayi shiru da bakinka.
Tana kaiwa nan ta mike ta shige,nan ta barshi....ya Santa fiye da kowa,idan tace zatayi abu, ba makawa sai tayi yi,don haka ya fara shiga rudani tun batayi ba.
Ya kai kimamin minti talati zaune a indata barshi sannan ya mike ya nufi gida.
A daren ranar,Hisham bai rintsa ba.tunane tunane kawai yake...domin kuwa duk wanda yasan ilham bayansa yake...idan tace zata yi abu tau ba fashi,ya zaunu kenan a zuciyarta!.tunani kawai yakai,yanda zai shawo kanta ta share zancen mutanen,don kuwa shi har ya fara tausaya masu,idan bata hakura ba...tsuki yayi,tare da gyara kwanciyarsa,..oh ooo Allah,ka taimake ni,ilham ce matsala ta kawai yanzun.da haka har bacci yayi awon gaba dashi.
Itama ilham ba ta rintsa,sai juyayin abinda mahaifinta fillo yayiwa mamee takai...ta kasa gane tsakanin mahaifinta da hajiya zubaida wa ya fi kuntatawa mahaifiyarta..tayi tsuki tace "gabaki dayanku zaku gane kuskurenku.


Kashe gari bayan ta idar da sallan asubahi,ta nufi  dakin mamee,zaune take kan abin sallah..da alama bata tashi ba tunda ta idar da sallah...,as usual,wayarta take daddanawa,ta durkusa ta gaishe ta,itama mameen ta amsa.
Shiru shiru...basu sake magana ba,mamee dai ta cigaba da abinda takeyi sai kuma ta dago ta dube ta tace lafiya dai ko?
Lafiya lau mamee...so nake nace maki mun gode,mun gode sosai akan tarbiyan da kika bamu,za kuma dawainiyanmu daga sa'anda babanmu ya gujeki...ba abinda zamu saka maki sai mafificin addu'a.
Mamee tayii murmushi...tace "come on babyname sake",kin manta ku amana ne daga Allah(S.w.a)? Da baza na iya ba,da bai bani ku ba..don haka godiya ga Allah.
Ok mamee,duk da hakan zani gode maki...
Shiru shiru bata tafi ba,kuma bata sake magana ba..
Mamee ta dago tace "anything more".
hmmm......yes! Ta daga yatsa...tare da saukowa daga kan gado ta rungume mameen.
"I love so much,so sorry for what u had gone tru because of us....ina kuma baki hakuri bisa ga ciwon kan da nasa ki akan Hisham,inn shaa Allah ba zani sake ba.
Mamee ta cire ta daga rungumar,suna fuskantar juna tace"Allah ne ya hadu ku,ba wanda kuma zai shiga tsakaninku.
Jikin girgiza kai ilham tace a a mamee,nifa na fasa auran Hisham.
Sabida me?😳...mamee ta nemi sani.
Sabida gabaki dayansu families din nan na tsane su...fadin ilham.
Har da ke kanki kenan?
Yes!...idan ta kama...,nu fa bazani boye maki ba,tun jiya nake da na sanin hada jini da su.
Mamee ta toshe mata baki,tana fadin dont be like this,ba wai na fada maki labarin bane don ki tsane ko wani abu....bata karasa maganar ba baby muhammad,watau dan autan ta,wanda take kira da abba ko Babana ko dady, ya fara motsi,tasa hannu a lebenta tana yiwa ilham alamar tayi shiru kar ya tashi.
Ilham ta bata fuska ta fice daga dakin..
Tun bayan rasuwar mahaifiyan mamee, mamee take tausayi baby muhammad,tausayinsa yasa ta shagwaba shi sosai..ga soyayya da kauna da take nuna masa,ga bauta masa da takeyi duk wai sunan so...hakan na matukar batawa ilham rai,taki jinin ta kalli abba yana shagwaba,da girmansa mamee na goyashi,ita ke yimasa komai,sabida ba ya son na kowa sai nata..duk ranar da ta barshi da ilham kuwa,dakansa take idan yayi mata wannan shagwaban don haka ke tsoronta idan mamee bata nan.

Dakinta ta koma bayan ta bar dakin mamee,cike take da takaicin abba sabida ya tsinke mata maganar da take sonyi da mamee.
Ta zauna tana nazari,can kuma ta mike tana fadin ya zama dole na fadawa mamee tun da wuri don haka ta nufi dakin mameen.
ta taras da mamee na mikar da abbab daga saman gadon shikuwa yana wani yauki yauki..cikin bacin rai ilham tace "mamee saukowan ma,sai kin taimaka mashi?
Idan baki iya kallo,ki koma dakin ki...fadin mamee.
Ta kara daure fuska,tace daman so nake na fadamaki zan je u.k
Mamee ta juyo ta dube tace ba lokacin hutu bane kenan?...me kike son kije kiyi a can,hutun ki bai kare ba.
Hmmmm.....akwai abinda nake son yi ne can.
Me kenan?..mamee ta nemi sani.
Ta shagwaba fuska,tace mamee don Allah ki bari naje,idan na dawo zan fada maki....nasan idan nayi maki karya zaki kama ni,shiyasa ban yi shi ba.
Tauww ai kuma baki fadamin dalili ba,don haka ban yarda ba.
Ta cije lebbanta,ta juya ta fita.a zuciyar ta na fadin mamee ta bata first steps of plans dina,amma zani san abinyi.
*SOYAYYARMU👫*
       Written by A'ishah
            (Ganarious)
Page 3⃣0⃣

Bayan rabuwan Hisham da ilham a gidan mamee,basu sake haduwa ba...ko kiranta yayi bata dauka,idan text yayi mata batayi masa reply.
Hakan yasa duk hankalinsa a tashe,ba  shi da sukuni.,don haka yau jumma'a ,yana dawo wa daga masallaci ya sake watsa ruwa ya canza kaya,tare da feshe jikinsa da kalolin turaruka.
Ya fizgi makulin motarsa ya fita..kai tsaye gidansu ilham ya nufa.
Sai dai me! Kunya ya hanashi shiga..gashi yana ta kiran wayarta ta ki dagawa..zaune yayi cikin motan,ya na tunanin mafita.
Yana tsakiyan tunanin,mai gadi ya wangale wa mamee gate  zata fito..
Da saurinsa ya fito daga motansa, ya nufo gun gate din, tana ganinsa kuwa ta tsaida mota
   Cikin fara'a ta amsa masa gaisuwa,bayan ya gaishe ta,sai ya kama sosa kai..
     Ta dubeshi,tace "ya ya dai Hisham?.
.....hmmm ba komai mamee.

Murmushi tayi tace feel free..idan da wani abu ka fada naji.
Har zuwa wannan lokacin ya soshe soshen kansa,sai kuma ya ce kawai dai....
..kawai dai me? Ta tambayeshi.
Ilham ce ta daina daukan  calls dina,tun bayan rabuwar mu a nan..ba ta kuma amsa min messages dina,abinda ya fi damuna shine "fansar da tace zata dauka.
Yanayin maganarsa ya baiwa mamee dariya, ta da'rah sannan tace fansan me kuma.

Wai zata rama duk wani abu da iyayena,da dangina sukayi maki..

Dariya ta koma yi,tace "kar ka damu,ba abinda ilham zata iyayi...tausayi da bakin ciki ne suka sanya ta yin furucin,na tabbata ilham ba zatayi komai ba...rashin daukan wayarka da batayi,kazo gobe..ga ka ga ta zanyi mata fadan haka.

Haka ya koma gida jiki a mace,kwarai da gaske ni kadai nasan ilham,hatta mamee da ta haife ta bata san ta kamar yanda na santa ba....
  kwance yake,amman kuma idonsa a rufe suke kamar mai bacci,yana ta zancen zucin shi kadai,daga shi sai singlet da boxer..cikin sa a kife yake kan lallausar kujeran sofa.
kaseem da kareem ne suka shigo da sallamarsu,daga kwancen ya amsa masu,ba tare da ya da'go ko ya bude ido ba..

Samun guri sukayi suka zauna,kareem ya mike ya nufi inda frij yake ajiye ya dauko masu drinks,..a yayin da kaseem yake cewa hisham"lafiya kuwa  abokina?..tunda ka dawo tafiyar nan muke ganin ka haka,me ke faruwa ne.

A sanyaye ya mike zaune,ya dauki pilo ya rungume.

Wai me ke faruwa ne??...ilham din ce k? Fadin kaseem.
   Ya daga masu kai daga  baya,yace itace wallahi.
   Sun fashe da dariya,sabida yanayin da yayi maganar..sai da suka gama dariyansu,sannan suka ce toh yaya?...mahaifiyar tata ce taki amincewa har zuwa yanzun?

Ya kada kai.."ta amince ai.
Cikin daga murya suka ce maa'shaa'Allah,ka isa barka.
 Hummm...kawai yayi
Kaseem yace yanzun dai me ye matsalan?
Ya nisa yace' abinda kenan,shine bayan na dawo saudiya na tafi gidansu,don daman tace idan na dawo na zo,toh shine fah take ba mu tarihi da labarin zaman da tayi da iyayena,da dangi na ga baki dayansu...
A gaskiya ba su yi mata adalci,shine yanzun ilham ta dauki alkawarin ramawa mamanta abinda sukayi mata.

Kareem yayi guntun tsaki,yace tau miye damuwarka???...ai wannan bai shafe ka ba,tunda mamarta ta amince,idan ta gama daukan fansarta ba sai kuyi aurenku ba..besides me wannan yar ilham din zata iya🤷🏻‍♂

Ido waje Hisham yace me zata iya fa kace??...Tabdi..,wallahi what ilham is capable of doing ya wuce tunanin wani dan adam,nasan ilham,nasa abinda zata aikata...infact nasan ta fiye da kowa a duniyar nan..duk abinda tace zata yi, tau fa sai tayi shi.

Kana wani magana can😏,auren ma tace ta fasa...duk da nasan ni kadai take so...don haka abinda fi damu na shine yanda zan shawo kanta ta yafewa iyayena da dangi na.

Kareem,yake sa baki yace"na fada maka ba abinda zata iya yimasu"

A hasale Hisham yace kaiii...wai kodai na baka labarin ilham ne kafin ka yarda?
Ilham mace ce da idan tace zatayi abu sai tayi shi.
Ba sau daya ba,ba sau biyu ba ta sha tace min zatayi abu,idan nace baza ki iya ba sai tace muyi "bet"...da ikon Allah kuwa sai tayishi.
Wani lecturern mu ya taba kashe kansa sakamakon,duk da bansan me ilham tayi masa ba,ta dai dau alwashin sai ya gwammaci lahiransa da duniyan,sakamakon fyade da yayiwa daya daga cikin kawayenta.

Ilham takan bani mamaki akan hakan,sai dai bani daukansa serious,kullum cewa nake baki iya wa,...na daina fadin hakan domin kuwa nima ya kawo kaina.

Watarana,nazo school,amman tunda nazo ban ganta ba,al'adarmu kuwa bamu shiga class sai mun hadu da juna,don haka na nufi hall din da nake sa ran ganinta..gaba daya dalibai suka juyo suna kallona,shiki lecturer ya tambayeni me nake nema?  Nace masa ba komai don haka na fita daga hall din,..ina cikin tafiya na ji an rike ni,juyowar da zani sa kawai na gan ilham ce rike da jakkarta.
Cikin bata fuska nace meya sa kika fito alhalin ba'a gama maku lectures ba.
Ta shagwabe tare da marairacewa tace "ko da na zauna ma bazani fahimci komai ba,tana maganar tana lallausa idanuwanta.
Ido waje nace sabida me?
Hannunta ta yi nuni kirjina dashi..ban nemi karin bayani ba,na rike mata hannu muka tafi.
Gurin da aka kebe ko donyi karatu,ko me son hutawa ko shakatawa, ko kebencewA,nan muka nufa,ina zama na janyota ,ina fadin zo ki zauna.
..ta make kafada tace ita baza ta zauna a nan ba,nace tau ina kike son zaman,?
Tace saman kafafuna..
ido waje nace kafafun basu da karfi,don Allah ki tausayamin....ganin bata da niyar zaman yasa na janyota ta zauna bisa cinyar nawa...na sa hannuwa na zagaye cikinta dasu tare da kwantar da kaina a gadon bayanta,murya kasa kasa nace kina ganin mutane mu suke kallo?
Toh ina ruwanka da su? Ta fada.
"Kinsa da ganinmu za su fahimci mu yan nijeriya ne,especially ke! Kuma ansan mu da kunya,don mun zo cikin su ba shi zai sa muyi koyi da al'adar su ba,su yakamata suyi koyi namu.
ba tare da tace min wani abu ba,ta cire min hannuwana,ta dawo gefe na ta zauna,tare da kwantar da kanta a kafada ta.
Magana irin ta masoya mukeyi,tana yai min zancen yanda zamuyi zamantakewar aurenmu...daganan ta dauko maganar ya'yan da zamu haifa, tana fadin  Allah shi sa yaranmu su biyo basirah da fasahan ta.
Dariya nayi mata nace ke har wata fasaha ne da ke? Kiyi fatan su biyoni dai..nan dai muka shiga musu,ita ala dole tana da fasaha.
Cikin dariya nace da fasahanki,da basiranki kike bacewa a gari?
Itama tayi dariya,tace wallahi wannan  bacewan da gangan nayi kuma sabida kai.
Ba wani nan...ke dai fadi gaskiya!.
Da gaske fa nakai,sabida kai na bacce...ko da gaba dayan duniyar nan zani shiga bani bacce ba.
Dariya ta bani sosai nace " ko a makarantarmu ina iya batar dake fa,kuma ki batu.
haba dai....sai dai ni na batar da kai.
ni din...? Ya fada
EH kai din fa.
Kaiiii....yarinya kinyi kadan da ki batar dani.
Haka kace?
Nace mata eh,kinyi kadan wallahi...bari ganin komai kikace zakayi Allah ba baki sa'a, this is me!...ina fadin haka ina bugun kirjina.
Tayi kuttah tare da mikomin hannu wai muyi "bet"..munyi bet akan zata batar dani,idan kuma baki batar dani kin zama tawa har abada tace eh ta yarda, tace idan kuma na batar da kai ba kai ba kallon wata mace a duniyar nan sai ni kadai...nima nace mata na yarda..da haka hiran yazo karshe..
Nayi mata rakiyah har izuwa baki gate din hostel din su,mukayiwa juna sallama,na juya nazi tafi tayi kira na don haka na taka zuwa inda take tsaye,tayi murmushi tace ka kasance cikin shiri don da zaran anyi hutu zaka bace.
Dariya nayi,na shafa kanta nace da sauranki yarinya.

         **     **      **
Mun gama jarabawa da kamar kwana hudu,muna tare da ilham zancen mu bai wuci irin ta masoya ba,nan na kawo maganar "bet" din na..
Ta dube tace ban manta ba ai,kuma gobe ne ko jibi inn'shaa'Allah.
Nace tau allah shi kaimu,don na matsu ki batar dani na gani ki basiranki ba a baki bace kawai.
Murmushi tayi,tace bacewan taka ai ta yan gata ne sabida sweet-moon zaka tafi yi.
wanene sweet-moon kuma?..ko dai honey moon kike nufi?
eh..honey moon ai na ma'aurata ne,sweet moon kuma na masoyane masu shirin yin aure.

Washe gari jira nake,ilham ta zo mu fita ta batar dani shiru,don haka na dauki wayata nayi kiranta....daga bangarenta hayaniya nake ji,na nemi sanin inda take tace min tana kasuwa,ta umurceni da nazo na sameta a bus stop din kasuwa.
ban bata lokaci ba na shirya,na dauki wallet dina,da atm card sai wayata..ina isa gurin na hangeta tana zuwa inda na ke..rike take  da tsinkayen sweet,tana isowa ta mika min daya tana shan dayat.
na yi dariya nace a kasuwan nan zaki batar dani?
ba tare da ta amsa ba,ta girgiza kai.ta zauna nima na zauna kusa da ita.
bayan kamar minti goma da zamar mu a nan bus ta zo,ta rikemin hannu muka shige bus din...da shigar mu na fara ganin kamar bus din juyawa take dani,na rufe ido na ina me fadamata yanda nake ji...ta kama kaina ta kwantar a cinyarta.

Bude ido nayi,na gan ni kwance a gadon kara,na  mike da sauri na leka windon dakin ciyayi na gani,na koma dayan gefen na lekan windon,shima kamar dayan gefen ne,na dawo tsakiyan dakin na kara yiwa dakin kallon kyau duk komai na dakin da ka'ra akayi shi,kofa na  gani,shi ba'a bude ba shi ba'a rufe ba,na taka sannun a hankali zuwa gun kofan na bude...
a tsorarce nake ganin ba abu mai rai a gurin ,daji ne sosai,da alama wannan dakince kawai a gurin na waiga hagu da dama ba abinda nake ganin sai ciyayi...a raina ko addua nake,nayi taku hudu zuwa biyar zuwa gefen dakin,nan na gan hanya,sai dai wannan hanyat,mutane sukayi shi da sahun kafarsu,ba ta mota bace ko mashi,ko keke.
Na bi hanyar,tafiya me nisa nayi ban hadu da abu me rai ba,sai tsuntsaye da ke yawo a sararin samaniya...ina cikin tafiyan nagan alaman na shiga gona don ganin alkama a shuke,hamdala nayi ina sa ran ganin mai rai..cikin ikon Allah na bulo a wata gona,mutane na gani sun fi goma maza da mata,suna noma,suna gani na suka mike tsattaye,wasun su na nunani suna yare,kafin na ankara wani ya zaro takobi yayo kaina.
Read More »

Saturday 20 January 2018

27-28 of SOYAYYARMU.

: *SOYAYYARMU*👫
      By Ganarious
Page 2⃣7⃣.
Sai bayan sallar isha'i Babana tare da hajiya suka shigo,a lokacin kukan ya lafa...sai dana sanin abinda nayi wa fillo nakeyi.
Tunaninsa nakeyi,ina kuma jin haushin kaina bisa ga abinda nayi masa.
Ina ganinsu na risina ina me gaida su.
Babana ya danyi shiru na dan lokaci,sannnan ya nemi da yasan me ke faruwa.
Ba komai na ce dashi..
Ba yanda basuyi da ni ba da na fadi abinda ya faruwa,sai ce masu nake ba komai,hakan ya batawa mamata rai tace "tashi ki bar mana gida tunda haka kawai kika zo don ki tada mana da hankali.
Hakuri na shiga bata...,Babana kuwa shiru yayi bai ce komai ba.

Washegari da safe ya sake shigowa ya matsamin da na fadamasa nace ba komai baba.
Ranar da na cika kwana hudu a gidan mu,Babana ya aika a kira masa fillo don ya neme shi a waya bai samu ba.
Ashe wai fillon ba ya gari.

Zaune nake ina yankewa mujaheed farcen sa..ba abinda nake tunani sai fillo..
Binta ce ta shigo da  sallamarta .
Cikin fara'a na amsa mata,yara kuma suka nufeta aguje sunai mata oyoyo..
maman ilham kin barni da ke'wa.! Fadin Binta.
Na basar da maganar ta,na dauko wata zance.
Na tambayi lafiyan mutan estate tace min suna nan kalsu.

Shiru-shiru..ba wace ta kara magana...can ta nisa tace maman ilham wani abu ya faru  tsakaninki da Baban ilham ne?
na da'go  ina kallonta tare da tambayarta "me kika gani?'
Hmmm...kananan maganganu da tseguma ne suke yawo a Estate,na kuma shaida maganar nan ba da'ga bakin ki suka fito ba.....kawai shairin mutanen na.
Da sauri nace wace irin magana ce?
"Cewa sukeyi wai kin ce a tashi maki a gida,ma'ana mutan estate din su kwanshi kayansu su bar nan din...shine fa salisu da yusuf suka matsawa mutane wai a kwashe cikin satin nan...wallahi Goggoji tun shekaran jiya take koke-koke wai ita ba inda zata tafi,su kuma sun matsa mata ,domin mahaifi hajiya zubaida ya riga ya bada gidan da zata zauna.
....shiru nayi,zancen ya daure min kaina,"Allah ya sauwwake"kawai na fada.

Shiru shiru har na shiga sati na uku fillo bai zo ba,Babana ya sake aikawa a nemo shi,wannan karon anyi sa'a.
Karfe hudu ya iso gudan mu.a falon Babana aka yi zaman.
Babana ne yake bayani akan zuwa na gida,kuma sun nemi su san dalilin haka nace ba komai,..ya kara da fadin "kai kuma muna ta sa ran ganinka shiru,shiyasa na sake aikawa a nemo min kai
Bai boyewa Babana komai ba ya sanar masu abinda ya faru a tsakaninmu....ya kuma sanar masu gida ne mahaifin hajiys zubaida ya bashi,don haka yake son ya kwashemu ya maida can din.
Babana ya girgiza kai yace "amman dai kuwa bakayi min adalci ba,ai kafin ya baka gida ni na baka...jeka ka sake shawara da iyayenka,duk abinda kuka yanke sai ka dawo ka dauki matarka.

Mikewa nayi na bi bayansa sa'anda zashi tafi,sai da ya kai gun motansa ya tsaya...ya juyo ya dubeni ba tareda ya ce wani abu ba.,ganin haka yasa nace masa amman fa baka kyautawa babana ba wallahi..
Eh...Na sani,ya maida min
Ido waje nace "ka sani fa kace?
eh,ya da'ga kai.
Toh wallahi tunda a sane kake bakanta min rai bazani bika zuwa wannan gidan ba,sai dai kuwa mu rabu.
🤷🏻‍♂ya da'ga hannuwansa biyu tare da make kafada,yace "anyway,shawara ta rage gareki,ni dai na baki nan da sati biyu ki harhada kayanki da na yara,idan kuwa bakiji ba duk abinda ya biyo baya kiyi kuka da kanki.
...a hasale nace 'ma cuci...butulu kawai,idan har sai na koma gidan wannan shegiyar,tau gwara mu raba hanya...ko kana tunanin bazani iya rayuwa ba da kai ba!
Ya shige motarsa ,ya tafi..ya bar a nan inata surutai na.
Na juya zani shiga cikin gida,na gan babana tsafe bakin kofar falonsa ya rungume hannayensa yana kalo na.

       **       ***     ****
A haka na kara yin sati uku a gidanmu.fillo ki wani daga cikin yan uwansa basu zo ba.

Zaune nake ina gyaran farce,sai naji sallama,na amsa tareda ba da izinin shigowa.
Me wankin Babana ne ya shigo rike da wata katuwar envelope... bayan ya gaisheni ya mika min envelop din wai wani ne ya kawo yace a bani..na sa hannu daya don karban envelop din sai ya kubcemin sabida nauyi,na sa hannu na jayo envelop din kusa dani domin kuwa ya fara yagewa..ba tareda nayi tunanin wani abu ba.
A inda na na gama gyaran farce,a nan bacci yayi awon gaba dani...ban farka ba sai da naji yars nayiwa mamata oyoyo..
A hankali na bude ido,ina me yimata barka da dawowa.
Ta amsa tare da fadin kin kuwa yi sallan azahar kuwa?
:ido waje nace laaah..ashe lokacin sallah,yayi.
Tana me kallona tace yayi ko ya wuce?.."kina bacci baki ma san da dawowan yara  ba.
Na mike na shige dakina don sauke farali.
Ban fito daga daki ba har sai da na tabatar na gabatar da sallan la'asar.
    Zaune na tarar da mamata tana shan kayan itace...yara kuwa sun baibayeta,tana basu a baki.
..idon ta ya kai kan envelop din,tace "me ke cikin envelop din can,tayi nuni da hannunta.
Hmmmmm...ni ban ma san me ke ciki ba,dazun nan malam Abdullahi ya shigo dashi wai wani yace a kawomin.
Tauu...bude mana ki gan abinda ciki!.
Toh mama!.
A hankali na yage shi,sabida daman can ya fara yagewa.
makullai ne suka zubo kasq,cikin mamaki na daga su sama ina kallo,na juya na kalli mamata,itama ni take kallo....na ajiye makullan na duba envelop din,takkadu ne a ciki da wata karamar envelop din kuma.
Na ajiye takkadun gefe na bude karamar envelop din,dan takkardace a ciki me dauke da rubutu layi biyu...ganin abinda ke rubuce ya sanya nayi ihun fadin "WHAT"...!!!
mamata ta taso ta karbi takardan,tana dubawa.
Innalillahi wainna ilaihiirsjiun kawai take fadi.
JIki a mace ta zauna kan kujera rike da takkardan.
Daga ni har ita din ba wace ta sake magana,sai dai surutun yara.
Kafin mangrib Babana ya dawo...a zazzaune ya tarar da mu yace 'ince dai lafiya ko?
Mamata bata tsaya wata wata ba ta mika masa takkardan.
SHIma din sakatsi ya shiga yi,ya dube ni ya ce "Haka Allah ya nufa!
Shima din guri ya samu ya zauna...kiran sallah ya ta dashi,ya mike zai tafi masallacin,ya gifta ta gefe na sai kuma ya dawo ya risina ya dauki sauran takkadun dake gefe na.
..murmushi yakeyi yana duba takkadun..can kuma yace "Dan Adam kenan".
Sai bayan da na idar da sallah wata irin kuka mai tattare da tausayi ya xomin.
NAyi kuk,nayi kuka kamar idona sasu fito.
washe gari kuwa mamata da babana basu je gun aiki ba,asalima ko abinci ya gagare su ci.
Yara ma ba wanda ya bita kansu har sai da hajiya tashigo..
Tace yau yan makaranta basu zo sallama ba,ashe basu je makaratan ba,injin dai lafiya?
mamata ta sauke numfashi tace lafiya kau kawai dai na tashi  jikin ba karfi ne,mamarsu kuma yanzun haka na san ba'a hayyacinta ta ke ba balle ta shiryasu.
cikin mamaki hajiya tace "lafiya?
tauuu lafiyan kenan...mijin ta ne ya aiko mata takkadar saki jiya.
Saki fa kikace?
Eh fa...
Ah'ah'ah....
Amman dai wannan yaron bashi da mutunci, fadin hajiya
mutuncin kenan ai...har fa takkardun Estate ya maido.
Nan hajiya ta shiga yin salati..tace yaushe hakan ta faru?
Da yammacin jiya
..ina daki,ina jin duk wani abu da suke fadi..
Suna gama magana hajiya ta karaso cikin dakina ta zauna....tana zama na fashe mata ds kuka,nan ta shiga lallashi...
washegari mama ta shirya yara suka tafi makaranta,amman ita bata tafi aiki ba.

 Hajiya tareda Babana suka shigo dakina ..na risina na gaishe su.
Babana yace subhanalillah!!! Kuka kikayi haka?..kin gan idanuwanki yanda suka koma kuwa?...haba mamata!
Kukan dai nakeyi masu,ba yanda basuyi ba na daina kukan,  amma kukan ya ki dainuwa.gashi idanuwan sun kumbure sun rufe,da kyar nake bude su sabida nauyi.
Ilham da mujaheed sun shigo gida a guje,sun zo suka rungume babana,yayi masu barka da dawowa,sun gaida hajiyaq da mama daga nan sukayo kaina....da shike mujaheed na da son jiki,zuwa yayi ya haye cinyata ya kali fuskata yace"mamee idonki na ciwo ne?...ya fadi hakan yana taba min idon.
Eh na da'ga masa kai,ya marairace fuska kamar me shirin yin kuka.
Ilham dake tsaye gefe tana kallona tace " sorry mamee"..
Ita ma kai kawai na da'ga mata..
Hajiya ta umurce su da su tafi su sauya kayansu..mujaheed ya mike yana cewa mamata "wa zaiyi mama na wanka toh"..shiru tayi bata amsa shi ba,ya kara fadin ko mu sa kaya hakanan!
Mama ta amsa eh,ai yau bakayi datti ba,jeka kasa kayan haka nan.har sau fita daga dakin mama tayi kiran ilham tana tambayarta ina Hisham.
Ta bata fuska tace uncle salisu ya daukeshi sun tafi.
Kuma...! Fadin hajiya.
Babana ya nisa yace ku kyalesu kawai,zan nimesu anjima.
[1/20, 8:22 PM] Aisha Gana: *SOYAYYARMU👫*
       By Ganarious.
Page2⃣8⃣
👉🏼Annabi (s.a.w)yace hakika addu'ar dan uwana Annabi Yunus(a.s) tana da ban sha'awa da mamaki,farkonta Hailala(kalman shahada),tsakiyar ta tasbihi,..karshen ta kuma tabbatar da laifi(ikrari)..wannan addu'an itace *La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimina*..wani ma'abocin bakin-ciki,ko ma'abocin bacin rai,ko ma'abocin damuwa,ko wani mai bashi,ba zaiyi addu'a da ita ba face sai an amsa masa..!dailami ne ya ruwaito shi daga Abdurrahman dan aufin(r.a)
           **        **       **
Babana da kansa ya tafi "my precious Estate".
A gate din shiga estate din masu gadi suka sanar dashi ba kowa a a cikin estate din....sai dai gidan malamai.
Tsaye yayi yana mamaki,ya zuciyasa yace miye abin mamaki,tunda sun aiko makullai!..ya tambayi masu gadi ko sun san sabon gurin da suka koma?
Suka ce a'a,basu da masaniya,amma wata kila malaman zasu sani...don haka babana ya karasa cikin estate din.
Malaman sunyi farin cikin ganinsa,nan yake tamabayarsu ko sun san inda masu gidan suka koma?
Suma din sunce basu sani ba,nan sukayiwa babana fatan alkhairi ta tafi.
Lambobin wayansu duk ba sa zuwa,amman baba bai fidda rai ba..kullum trying yake ko Allah zai bashi sa'a.

Mamee tayi shiru na dan lokaci,ta dubi Hisham da ilham,ita suke kallo. Gaba dayansu idanunsu yayi jajir,ba kamar ilham da hawaye  ya kusan sauka bisa kuncinta.
...mamee ta cigaba da fadin "na fita hayyaci na,na lallace,kamanni na ya sauya,na zama zautata abin tausayi.
Bana ci bana sha,ibada ma na neman gagarata,sai da kyar.
Bani da aiki sai kuka da tunane-tunane,kullum ina daki ko falo,bana fita cikin gida ballantana cikin gari..
Iyaye da abokan arziki sunyi ban hakuri,sunyi lallashi,sunyi nasiha,sunyi ban baki,sunkawo ayoyi da hadisai akan na dauki al'amarin a matsayin kaddara,amma abu ya ki yiyuwa domin kuwa a koda yaushe wata irin sabon son fillo nake tashi dashi..soyayyarsa sai huruwa take.
Babana ya daina fita,zama yakeyi dani a daki,gudun kar na yi wa kaina wani abu.
Mamata kuwa ta dade da fita harkata,duk da abin yana damun ta..fushi take da ni wata sa'in.
Nan ma mamee ta sakeyin shiru ta share hawayen da suke zubowa..ilham kam tuni ta fara kuka itama.Hisham kam namiji ne,hawaye na makele a idon sa ya daure yace mamee munajinki.
Ta share hawayen ta cigaba da fadin "na kasance makauniya, domin kuwa bana ganin halin da mamata ta shiga sabida ni.
Wasu daga cikin yan uwa da suka sami labarin abinda ya faru dani,sunyi murna har sukan kira mamata suce 'darasin rayuwa ce'..wasu suce  idan da ya'nazeeru na aura,sun tabbata hakan ba zai faru ba....kowa da abinda yake tofa wa lamarin..
Masuyi mata yi mata fata nagari,kadan ne....akwai wace don rashin imani ma tace Allah shi maimaita,duk fa mamata suke fadawa wannan sabida naki auaran ya'Nazeeru..ire-iren wadannan maganganu sun sanyata tunani,ta fara fita hayyacinta itama gata  da rike magana.

Ya'Nazeru kuwa tunda ya rasani ya kiyin aure,yan uwa sunyi sunyi ,sunyi korafi,sunyi fada gami da nasiha ya ki sauraronsu,asalima yason anayi masa zance aure.
Yana jin ance mijina ya sake ni,ya zo gidanmu don ganewa idonsa,ya na koma kuwa yace shi fa da so samu ne da zarar na haihu a daura masa aure dani...iyayen sa sunyi allah shi waddai,ba kuma zasu amince ya aureni ba...shi kuma ya dage sai ni,sannu a hankali suka amince badon suna so ba.

Watarana bayan na ci kukana,na mike zan shiga toilet,sai nakejin jiri,maimakon na koma na zauna sai na ci gaba da tafiyat,ban ankara ba sai ganina nayi zube a kasa,duk da ban san wata duniyar hankalina yake ba,zani iyacewa inajin abu kamar ruwa ruwa yana bin cinyoyina.
Na dade a haka,ba wanda ya sani domin kuwa babana dake zama dani ya tafi massalaci.
Wata irin azaba nake ji,tun ina ji har na daina ji.
Farkawa nayi na ganni a gadon asibiti.
hajiya da babana ne zaune gefe na,ina bude ido suka mike.
Baba na cikin rudewa yace yaya kike ji yanzun?
Binsa kawai nake da ido,ganin haka yasa shi barin gurin don kiran likita.

Kwana hudu nayi a asibiti suka sallame ni...likita da kansa yayimin nasihohi,ya kuma shaidawa Babana  da na dinga cin abinci,sabida yaron cikina yana tattare da yunwa...ya ce ba fata yakeyi ba amman yanada masani casa'in da tara akan yaron nan na dauke da ciwon yunwa.
ya kuma shaidawa baba na da zarar na shiga watan haihuwa ma'ana nan da sati biyu kean su kawo ni a cire yaron,sabida halinda nake ciki bazani iya haihuwa ba,asalima "tana iya rasa ranta da zarar tayi nakuda na dan  lokaci.
Godiya sukayi,muka nufi gida...
Daga wanna lokacin Babana yake kokartawa don ganin na ci abinci,sa'anan da yammaci ya rikemin hannu mu shiga cikin gida muna zagayawa,sabida shawaran da likita ya bada akan na dinga yi excersice.
Babana bai taba minti talati batare da ya shigo duba ni ba,har cikin dare yana kan zo dubiyata sabida haka ne baya samu isashe bacci.

Ina shiga watan haihuwa da kwana goma Babana ya umruci su hajiya da su shirya ni a tafi dani asibiti.
A ranar da suka kaini,a ranar akayimin tiyata aka fiddo yaro.
Da' namiji Allah ya bani,tunda muka koma gida Babana ke kokarin neman daya daga cikin yan uwan fillo,bai samu ba,don haka ya hakura ya aikawa fillo gun aikinsa cewan matar sa ta haihu....shiru shiru ba alamansa.
Ni kuwa tunda na haihu nake sa ran ganin fillo,nasan ko ba komai zai zo duba dan sa.
Har ana gobe suna ba fillo,kuka ya dawomin sabo...kewar fillo kawai ke damuna.
Babana ya tambayeni ko da sunar da nake ra'ayin a sawa yaron!.
Nace masa "muhammad"sunar baban nawa kenan.
Don haka ranar suna yaro ya ci sunarsa muhammad.
Bayan an watse taro,wasu daga cikin yan uwan mamata,su kawo zance na da na ya'nazeeru....mamata bata son maganar amma ba yanda ta iya da su....ce masu tayi zatayi shawara da babana.

      **          **           **
Yaron nan tunda na haifeshi bazani iya tunawa ko sau nawa ya sha nono na ba...bani da lokacin abinci balantana ya sami kulawata,kulawarsa ta koma gun mamata.
   Tun bayan da aaka gama suna, na dauki wata hali na kyaluwa...ba wanda nakeyi magana,a ko dayaushe ina kunshe a daki...
mamata wata sa'in idan zatayi aiki ta kan kawo jaririn guri na ta kwantar dashi,amma fa ko da jaririn nan zai shekara yana kuka ba zani daga shi ba har sai ta zo ta daukeshi..tayi fada ta gaji don haka ta daina ajiyeshi guri na..wani lokaci ma sai na kwana biyu ban sa shi ido ba,sai idan babana ne ya shigo rike dashi.
Ganin na ki koma wa dai-dai kuma abin nawa kara ci yake,ya sa mamata ta baiwa Babana shawara da akaini asibiti,wata kila kwakwalwata ba lafiya..bai ki shawaranta ba,don haka suka dauke ni zuwa kasar waje.
Gabaki dayan mu muka tafi can don dama yara na hutu.

Sun tabbatar masu da cewan lafiyata kalau ba abinda ya sami kwakwalwat,sai dai damuwa..suna kuma bada shawaran da na daina damuwa,idan ba haka ba zai kawo min ciwon xuciya ko mutuwa gefen jiki.
Sati uku mukayi a can,sannan muka dawo gida..mun dawo ba da dadewa ba mamata ta fara rashin lafiya.
Ta nemi nemi izini gun Bab na cewan zata koma kasar london inda muka baro don ganin likita.
Day su ilham ta tafi,har da jaririn,a lokacin kanina ya dawo gida domin kuwa ya gama karatunsa,don haka ni dashi da su hajiya ke gida.
Watan mamata daya a can ta dawo,ta bar ilham gun yayana dake da zama a can.
Sauki kam alhamdulillah ta samu.
Bata wani dade da dawowa ba ta sake komawa,wannan karon ma da yaran ta tafi,Ba yanda babana bai yi ba akan ta tafi ta bar yaran,tace Allah ya sauwake ta barmin yara.
Karon nan ma ta dade kafin ta dawo,sai dai da ta dawo jiki ya sauka,ma'ana ta rsn rame,idanuwanta kuma sun shishige ciki...
Ya ya jiki kawai nace da ita,ta amsa min da alhamdulillah.

Mamee ta kara share hawaye tacigaba "Mamata kenan!..son kai da son zuciya ya hana na fahimci cewan tana cikin matsanacin hali...duk sabida halin da nake ciki.
Babana ya bukaci da ta nuna masa sakamakon rashin lafiyar da suka bata..
Tace ce masa ba wani abu bane face ciwon yunwa da ya kamata sosai..nan ya shiga fada..
Daga wannan lokacin itama yake saka ta gaba sai ta ci abinci.
Haka babana ya zama abin tausayi,baya nan baya can...ga tsufa ya fara kamashi.
   Watarana Babana ya matsamin da na fito falo,sabida idan zai fita guri me nisa sai ya matsamin na fito falon,wai na tsaya gun mutane gudun kada wani abu ya sake faruwa ba kowa kusa.
Mamata zaune tana baiwa baby muhammad madarars hajiya ta shigo da sallamarta,tana zama ta dubi mamata tace "kai..kai...kaiiii...!maman Aisha kin rame dayawa!..da fatan ba damuwa bac kika sanyawa kanki ba dai ko?
Mamata ta ta'be baki tace "Allah dai yayi mana sauki"
Ameen ...hajiya ta amsa,tana ci gaba da fadin don Allah ki cirewa kanki damuwa...itama Aishan addu'a zamuyi mata.

Yanne na da suke zaune  kasashe ketare sun hada kai suka zo lokaci daya..ciki harda dan hajiya...sun zo duba lafiyar mamata ne,su da matansu da kuma ya'yansu,har ilham ma an zo da ita..
tunda suka zo,babban yayana ta gun mamata yake jin takaici na..
ya baiwa iyayena laifi wai su suka bata ni...kallona ma baya sonyi,don duk saanda ya kalle ni sai yace dubeki,baki da maraba da yan gidan mahaukata...ya dinga tsuki kenan duk saanda ya hangi Babana ya shiga daki na ko ya fito daga dakin.
a ranar da yannena suka cike kwana hudu da zuwa,zaune suke a falon mama,ya'Abdurrahaman dan hajiya ya shigo,ya  sallami mama akan cewan  xasu tafi zaria da shi da matarsa da yara.don gaida iyayen matarsa....tayi masa addu'a da fatan su dawo lafiya.
ya shigo dakina don sallaman Baba,shima baba yayi masa a dawo lafiya.
Ya mike zai tafi,Baba ya tsaida shi yana tambayarsa da wata motan zai tafi?.
Ya amsawa baba.
Baba na ya mike ya ajiye baby Muhammad kusa dani,yana cewa ya'Abdurrahaman muje na baka makullin motan nan mercedes,sabida jiya akayimata services.
Yana fice wa baby muhammad ya fara kuka,kuma sosai yake kukan...daga kitchen mamata ta zo a guje,tana zuwa ta ganshi a gefe na,ko kallon inda shike nayi ba,balle na daukeshi..rai a bacce ta shiga fada tana fadin" ashe musuluncin ki bai cika ba!,ba ki tawakkali da abin da Allah ya rubuto!..nayi fada nayi lallashi duk baki hakura ba..toh yaya kike son muyi?ko so kike mu kamoshi a daura maki shi don dolensa?..haba Aisha!..ganin ki a haka,ya sanya mu cikin wani hali,amman duk da haka bai sa kin dai-daitu ba ko sai kin gan mun rasa ran mu tukan sa'anan hankalinki zai kwanta?
Haba...ke wace irin yarinya ce da bata tawakkali,baki yarda da kaddara ba!..fada mamata takeyi sosai hat tana sarkewa,niko kuka nasa mata.
Tana cikin magana ya'Abdul azeez ya shigo rai a bace,ya na kokarin riketa yana bata hankuri,ta ture masa hannu..tana nuna ni da yatsan tare fadin "yar nan sai ta kasheni tukun hankalinta zai kwanta,wai ace dan cikin ta......
...maganar da bata karasa ba kenan,ta da'fe kirjinta tana batun faduwa kasa,ya'Abdul azeez ya tareta yana fadin subhanalillahiii..mamah!
Ganin haka yasa na taso a hanzarce na zo gunsu ina fa din mama kiyi hakuri,ba zani sake ba!
Tuni ya 'abdul azeez ya dauke ta muka nufo waje.
Mamee kam kuka ya tsananta,wannan karon kukan da takeyi ya tabo zuciyar Hisham,shima din sai sharan hawaye yake yi.

Mamee ta ci gaba "a kofar shigowa sashen mama mukayi karo da Babana,..cikin rudani yace lafiya?
Asibiti..Baba asibiti zani kaita kawai yayana yake fadi.
Family motar mu Baba ya fito da,yayana ya sanya mama a bayan motan,nima na shiga bayan,shima baba haka ya shigo muka zauna nan..yayana ke gaba yana tuki.
A hanyar mu ta zuwa asibiti kuwa ba abinda nakeyi sai kuka ina fadin mama ki yafemin nayi nadama,bazani sake ba kinji mama!..yayana kuwa sai masifa yake yana cewa kiyi fatan kar wani abu ya sameta,don kuwa idan haka ta faru bazani yi maki da sauki ba...sai da Baba ya tsawatar sa'anan yayi shiru.
Tunda muka shiga motan idonta a rufe numfashinta ma sama-sama...shima babana a hankali yake kiran sunanta,.muna shiga haraban asibitin ta rike min hannu gam..ta bude ido a hankali tana kallona tace..' kiyi hakuri..kiyi hakuri..ta fada,zata sake magana kenan ta saki hannuna tare da rufe idonta a hankali..
Read More »

Tuesday 16 January 2018

Page26 of *SOYAYYARMU*

*SOYAYYARMU*👫
     By A'ishah M.Gana
           *(Ganarious)*
Page2⃣6⃣

ZUciyata,ruhina har zuwa gangan jikina sun ki amincewan fillo zaiyi aure,har sai da suka gan yana shirin zuwa daurin aure.
   Kallonsa kawai nakeyi..ya gama shirinsa tsaf,yana sanya links din hannun rigansa ya juyo ya dube ni mukayi ido hudu..ya kai kimamin minti tara yana kallona ba tareda ya kifta idonsa ba,nima din shi nake kallo.
Ya yi taku zuwa bakin gado,inda nake zaune,ya zauna tare da  kama min yannuna yana me kallon yatsun...ya da'go ya dubeni kamar me tunani,yace "kiyi hankuri maman ilham"
Cikin girgiza kai nace shi kenan abinda zaka fa'da?
Abubuwa da yawa nake son fadamaki...sai kuma yayi shiru.
Nan na shiga yi masa kuka,..ya jayoni jikinsa yana me shafan gadon Bayana.
Muna a haka,wayarsa ta fara kara..a hankali ya da'ga wayar ya dubi screen din wayar sai kuma ya mayar ya ajiye tare da kankameni a jikinsa...
Wayar ta sake kara a karo na biyu,ba dubi inda wayar ba  ballantana ya dauka haka wayar yayita kara be dauka ba..

Kwankwasar kofar da mukaji ya sashi mikewa.
Ilham ce tsaye,ya dauke ta yana cillata sama yana mata wasa..a ajiyeta saman gado kenan tace  masa ai Anakiransa a falo don haka ya fita zuwa falon.
..yana fita safiya ta shigo..."mutane na jiran ango yafito su tafi daurin aure,ashe yana nan yana shan zuma"
Ta'be baki nayi nace 'al'amarin fillo yakan dauremin kai,kamar me iska'
Kila baza'a rasa ba fadin safiya...tana rufe baki,ya shigo rike da Mujaheed,sul-sul safiya ya fice.
Ya karaso inda nake yace kin gama ganin kwaliyan..?
Dubansa nayi da dan harara nace"ai daman ba ni kayiwa ba"
Dariya yayi ya rungumeni,yayimin ra'da akune"wannan kwaliyan taki ce ke kadai"..
Ganin yana rungume dani yasa mujaheed nata ihun ya kankame babansa,ya sake ni ya kamoshi suna wasa itama ilham ta shiga,sai na tsinci kaina cikin farin ciki,rabon da na gan haka...
ya ki zuwa gun daurin aure,yan uwasa suka wakilce shi..sai karfe biyar fillo ya fita,shima din don suna ta damunsa da kira ne.

Tun bayan ficewarsa ban sake ganinsa ba har yan biki sun watse.
Abu kamar wasa har kwana shidda ban sa fillo a ido ba,idan kuma na kira wayarsa ba'a dauka.
Hankalina ya fara tashi,don haka na sanar da safiya,ta bani hankuri takuma bani shawaran da na shiga cikin gida gun yan'uwansa ko mamarsa,ba za su rasa labarin sa ba...haka kuwa nayi,sashen goggoji na nufa tayi farin cikin ganina tana me tanbayata ko nayi mata yaji ne don rabon da ta ganni tun biki na saura sati daya.
Nima cikin farin ciki nace  goggoji nayi haka ne sabida yan rugga sun daina sona ,na rasa laifin me nayi masu.
"Bakiyi masu komaiba"tace dani.
Zaune nake na rasa ta inda zan fara tambayarka ko ta gan fillo...can dabara ta fadomin nace "amarya ta kawo maki gaisuwa kuwa?"
Eh...ai basu jima da barin nan din ba.
Gaba na  naji yayi ras!
Shiru nayi na dan lokaci,sannan nace "sun kyauta.
Daga nan sashen binta na nufa....ko zama banyi ba nace "wai inane sashen amaryanku?
Kamar ya ya fa? Ta tambayeni cikin mamaki
abinda na fada farko shi na sake mai-maita mata.
"Kina nufin  kice bakisan ba'a estate gidan ta yake ba.
A'a wallahi,ban san komai game da ita ba,..a ina gidan ta yake tau?
Na manta da sunar anguwan, cewan binta.

Jiki a mace na koma sashe na ina me tunane-tunane.
Abu kamar wasa,muna batun wata,ba fillo ba alamun fillo,na shiga rudani,na kasa samun sukuni..na rasa wa zan fadawa naji sanyi..safiya ce ta fado min a rai,don haka na dauki wayata na kirata.bugu daya ta dauka...tana fadin hello! Na fashe da kuka.
Ta shiga lallashi tana fadin ki kwantar da hankalinki ki fadamin abinda ke faruwa...
Na dan tsagaita kukan na sanar da ita.
Tayi shiru na dan lokaci,daga baya tace"Gaskiya wannan maganar ya kamata a kaishi gun iyaye.!
Da sauri na girguza kai kamar tana gurin,nace  a a .....kiyayya zai shiga tsakani su.
...tauuu kuma sai a kyaleshi ya na shiga hakinki?ai wannan cin amanace...gaskiya ba zai yiyu ba.
Don Allah safiya kar ki fadawa kowa,pls and pls ina rokonki.
Hmmm...gaskiya banyi alkawari ba,idan dai har maganar ta hanani sukuni,touh fa zan shigo kaduna gobe.
Da haka na dinga bata hankuri,mukayi sallama.

Washe gari na shirya yara na kwashe su zuwa sashen goggoji..kafin mu karasa cikin gidan ta na hangi wata katuwar mota,anyi parking a kofar gidan da ganin wannan motan kasan masu shi sun jiku da kudi..
Ina sallama yara suka shiga ciki da gudu,domin hayewa cinyar goggoji,daman haka sukeyi idan dai mun zo nan.
..ras! Kirjina yayi,ganun mutanen da ke zaune a falon.
Fillo da amaryasa hajiya zubaida..nayi sallama na karasa cikin falon na zauna,mujaheed ya sakko ya nufi gun babansa ya kankameshi...shi kuma ya dauke shi yana masa wasa yana satan kallona.
Daga shi har haj.zubaidan basuyi min magana ba nima ban masu ba.
Kokari nake,ina me dannne zuciyata ka da su  fahimci wani daga gareni,sai dai fillo ya samin ido...tun yana satan kallona har ya kai ga tsaida idonsa gareni,duk na tsargu hakan ya sa na mike na shige bedroom din goggoji.
Da shiga ta fillo yayi sallama ya shigo,ya yi tsaye yana kallona nima kuwa shi nake kallo.muna haka hajiya Zubaida tayi sallama itama ta shigo.ta sami guri ta zauna sa'anan ta dubi fillo tace masa"my one ka ba mu guri zamuyi magana"
Da kamar ba zai fita ba,sai kuma ya fice.
ta dube ni tayi murmushi me dauke da sako..tace"da fatan kina lafiya?
Kallonta kawai nakeyi.
Ta tabe baki tace anyway ba ma sai kin amsa ba..kawai so nake na sanar da ke cewan fa yanzun fillo nawa ne...ni kadai nikadai ke dashi.
Idan har kina son kanki da arziki,kiyi ga'ba abinki,ki yanke duk wani abu da zai hada ku..da fatan zaki fahimce ni?
Tana kaiwa nan ta mike ta fice daga dakin....tana isa falo sukayi sallama da goggoji .
   
    Maganar hajiya Zubaida ya wo yakai a kaina..da zarar na zauna sai kawai ya fadomin.
Yau ma safiyace na kira,na sanar da ita maganar hajiya Zubaida,wannan karon hankuri ta bani tace "...ai na fada maki, kingan maganata ta fara fitowa ko? Suna iyayin komai akan abinda suke so,don haka sai kin hada da addu'o'i,ki tashi tasye da ibada...yanzun haka ba yinsa bane.
kai safiya...ya na sane,da saninsa yake min haka...
Ki kara hakuri,inn shaa Allahu zan samu lokaci na shigo kaduna mu tattauna.

Tunda cikina ya shiga wata bakwai nake ciwon mara,kullum cikin ciwo nake..yau lafiya gobe ba lafiya,sai nake ji kamar zan haihu....gashi na rame,na lallace,kammanina ya canza.
Binta ce kawai ta san halinda nake ciki,cikin ya  uwan fillo don haka kullum tana gurina,ga tausayi.

Zaune nake ina ta tunane,yara kuma suna wasar su sai jinayi anyi sallama..fillo ne ya shigo.mujaheed ya nufe shi ya dauke shi,zai ajiye shi ya kama kuka wai baza shi sauka ba,sai ya nufi cikin daki dashi ba tare da yayimin magana ba hakan yasa ni mikewa na bi bayansa.
Gun wardrob dinsa yake tsaye,da alama yana nema abu ne.na zauna  saman gadon har ya gama abinda yake.
..muna hada ido na dauke kai..shima ya dauke kai yayi hanyar fita.
Da sauri nace"inason zamuyi wata magana da kai fa.
tsak ya tsaya sa'anan ya dawo baya.
Gyaran murya nayi nace..ni fa cikin duhu nake!..shin a wani matsayi nake ne?,yau don Allah bani aron lokacinka ka fitar dani daga wannan duhun..watakila zan fahimce ka.
Kallona yake,bashi da niyar yin magana...haka ya bani damar ci gabawa da magana.
Don Allah yau ka fadamani laifin da nayi maka ni da yarana,ka guje mu baka damu halinda nake ciki ba balantana abinda ke ciki na.
Baka damu da ci da shan mu ba,balle hakina..baka  tunanin wannan yayi kama da cin amana?
Har zuwa lokacin shirun dai yayi bai amsani ba.
Nan kuka ya zomin..ina fadin ka amsa ni mana! Me nayi maka haka!,yau watan ka daya da sati biyu kenan rabon da ka tako wannan gidan,ko baka zo don ni ba ka zo don yaranka..
Sai da kukan ya tsananta sa'anan yayi gyaran murya yace "bakiyi min komai ba.
Abubuwa ne sukayimin yawa,ina kuma zirga zirgan gyaran gidana,da man nufi na idan komai yayi saiti sai na zo na kwashe ku mukoma can din,sabida kar ki gan kamar an shiga hakinki.

na tsai da kukan nace "ka sami gida fa kace?
gira ya da'ga sannan yace eh..
cikin bacin rai nace wannan kuma fa ,ba gida bane??
Wannan giidanki ne,wancan din kuma gida na ne.!as far as kina matata kuma kina son ganin ko zama dani,toh fa zaki tattara naki da yara ku dawo gidana.
A fusace na da'ga masa hannun tare da fadin kaiii...macuci!ni kake fadawa haka??mahaifina zakayiwa butulci? Toh wallahi baka isa ba!.
Idona ya rufe sabida bacin rai asalima ban taba bacin rai irinta ranar ba, na shiga zaginsa...
ya mike zai fita,gefe na kuwa kayan wasan mujaheed ne,na dauke su ina ta jifan sa da shi har ya fice.

KUKA nakeyi sosai raina ya baci,tunda nake da fillo ban taba jin na tsane shi ba sai a ranar duk da abinda yaKe min bana jin haushinsa.
Sai nake ganin baiyi wa babana adalci ba.
Ina kuka ina shirya kayana da na yara,na hada muka nufi gida.

Mamata ta rude ganin ina kuka,ta shiga tambayata abina ya faru,amman kuka bai barni nayi mata bayani ba, don haka ta fita harkata har sai da nayi me isata nayi shiru.
Read More »

Sunday 14 January 2018

Page25 of SIYAYYARMU.👫

SOYAYYARMU 👫
   By A'isha M.Gana
         (Ganarious)
2⃣5⃣
Assalam...da fatan muna  lafiya ya yan'uwa...ina me bada hankuri akan rashin typing kwana biyu.

👉🏼Ganarious.blogspot.com/ and drop ur comments and opinions,

Safiya bata koma a ranar ba,dolenta ta kwana sabida yanayin da tagan na shiga.
Yanda nagan sa'fiyah,haka na gan dare...ban rintsa ba sai tunane tunane.
    Washegari da sassafe Babana ya nufi"my precious Estate"...ya tarat fillo ba ya garin don haka ya nufi gida ko nace sashen  Baba Lamido shima baya sun tafi rugga da sauran yan uwansa,hakan ya sashi barin sako,cewan idan sun dawo yana son ganinsu,domin kuwa ance a ranar zasu dawo.

Mamata tayi lallashi,tayi fa'da,tayi fushi..daga karshe kuma ta koma lallashi akan naci abinci,ko da shayi ne....a lokacin ko ruwa bana marmari balle waishi naci abinci,ganin naki sauraron kowa ya sanya safiya kiran mamanta.
Tana isowa,safiya ta sanar da ita abinda ke faruwa.
Itama fa'da ta shiga yi,tayi fadan kamar baza ta bari ba,da'ga karshen ta koma lallashi da nasihohi tana bani magana,....hajiya ce ta shigo rike da tire a hannunta ta dire a gamanmu tareda fadin Bissimillah.
Ganin bani da niyar tashi,yasanta rikoni na zauna sa'anan ta debi abincin tana bani a baki.

Bayan sallah magrib Baba lamido tare da mahaifin fillon,mallam yakubu suka iso gidan mu.
...baba lamido ne ya fara magana bayan sun gaisa,yake ce wa babana "lafiya dai ko??anceka zo neman mu.
Babana ya numfasa yace "a gaskiya ba lafiya"
Gaba dayn suka hada baki da fadin "tauww"
...Buba ne ko?
Kai kawai mahaifina ya da'ga sa'anan ya kwashe komai ya sanar dasu.
Salati baba lamido yayi yana ta'fa hannuwansa.."ai ni ban san yar'nan bata san da zancen auransa ba"fadin baba lamido.
Mahaifin fillo yasa baki da fadin"...wannan lamarin da ban mamaki yake"..mu dai ya same mu kwanakin baya yace  alhaji dauda ya bashi aiki  da kuma babban matsayi..
Daganan kuma ya bashi yarsa,yana sanar da mu, mukace ya tafi ya sanar da kai,duk abinda kace shi za'ayi..
..kwana biyu a tsakani yace sun umurce shi da ya turo magabatar,..mu kuma hankalinmu be bamu mu tambayeshi shawaran da ka bashi ba..
a haka dai suka tattauna,daga karshe suka shigo cikin gida muka gaisa,..sun kuma tausayamin ganin halin da nake ciki.

  A ranar da fillo ya dawo suka taso shi gaba,gidanmu suka zo.
Anyi kirana zuwa falon Babana inda suke zaune.
Mu hada ido,naji faduwar gaba,shi kuwa sai bi na yake da ido.
Na sami guri na zauna tare da gaida su.

Babana ne ya fara magana,yana me tambayar fillo ko da laifin da tayi maka??
Yace a'a.
Tauw meye yi zafi da zaka kara aure baka sanar da ita ba,balle ka nemi shawaranta?..na san aure nufin Allah ne, kamata yayi ka sanar da ita ba wai taji labari a waje ba.
Shiru fillo yayi,bai ce komai ba.
Nan babana ya shiga yi masa fada,ya nuna masa bacin ransa sosai...yayi masa kashedi da'ga karshe yayi masa nasihah..
bayan sati daya, a lokacin auren fillo da hajiya zubaida saura sati biyu,don haka babana ya sa anyimin gyaran gida an kuma canza komai na gidan sannan na koma gida..
Tunda kuwa na koma nake ganin sauyin hali da  ga mutan gidan,da mata har mazan...ba kamar yusuf da salisu(Lamido karami),ba su kaunar ganina.na rasa dalili kiyayya har yara na.

A zatona idan na dawo zamantakewarmu da fillo zai dawo kamar baya,amma ina!! Sai abinda ya karu..ko magana ba ya son yimin.
Watara na lura kafafuna sun kumbura sai nayi tunanin da nayi excersice  ,na kwashi yara muka nufi sashen binta ,bamu tarar da ita ba,daga na  sai sashen Baba Lamido,nan na tarar da Binta da su fadimatu,halima,bingel da dai sauransu,gidan cike yake da yan'uwa daga ruggansu...cikin fara'a na gaishe su ina fadin yau me akeyi ne da ba'a gayyaceni ba.
..yooh kina nufin kice baki san abinda ya kawo mu ba?..fadin Hauwa
Hauwan diyar kanin Mahaifin fillo ne.
A'a wallahi ban sani ba.
Sai wata a cikinsu tace "tau biki muka zo,dan uwan mu zai kara aure"
Gaba naji yayi ras!.ashe fa satin bikin kenan muke..
Zama nayi ina binsu da ido suko sai bushashansu sukeyi,ba tare da sun yimin magana ba,ko sun sanyani a harkansu ba....sai dai idan andauki lokaci Binta ta waigo ko ta zo inda nake tace sannunki mezan baki ki ci?
Ana haka fada ya hargitse tsakanin Hisham da Mahmud (dan Hauwa) ...ganin Hisham a kasa,mahmud na kai masa duka ya sanya ilham zuwa ta kama mahmud ta samasa hankori ta cije shi,dai dai nan salisu watau Lamido karami ya shigo.
..shigowar sa kuwa yayi dai dai da tsaga ihun mahmud sabida azaban cizo.
Lamido ya kama ilham ya zane ta,duk a idona...ya rike mahmud zuwa inda su hauwa ke zaune,tana ganin shaidar hakorin ilham ta taso tana zage-zage tare da bugewa ilham baki  tana fadin "yau sai na cire wannan hakorin..duk dai ban tanka ba sai kallonsu nake alhalin kuwa har araina nake jin abinda suke yi mata.
Lamido ya zo gurin,ita ko ilham sai kuka takeyi sabida bubbuge mata baki da hauwa tayi....mari lamido ya sake kai mata tare da tureta yana fadin "fita ki bawa mutane guri,ya tunkuda ta ta fadi kasa,na kasa jurewa na mike....kai Lamido,wannan wani irin cin zarafi ne? A gaba na kake yi wa yarinya haka? CIkin bacin rai nake maganar,a yayin da nake mikar da ilham daga kasa...." ai  kaine me barin gidan ka bata guri,ba ita...
Kamar jiraye yake danai wannan furucin,sai surutan banza yakeyi ta inda yake shiga,ba tanan yake fita ba....ha yana fadin shi wallahi ba zai kwana a Estate din ba,wai nayi masa gori.
Cikin bacin rai na koma sashena,ina me mamakin wadannan mutanen.
..daga wannan lokacin kannensa mata suka yanke hulda dani.

KWana uku to auren fillo,safiya ta iso...har zuwa wannan lokacin fillo bai ce min komai ba game da auransa balle yayimin bayanai ko ban hankuri,asalima tunda na dawo,hiran kirki bai taba hadani dashi ba...sai dai gaisuwar safe da kuma idan ya dawo nai masa sannu da dawowa.
...bayan mun natsu,safiya ke tanbayata inda za'a ba amarya ta zauna.
Cikin kwantar da murya nace"kin san kuwa har zuwa yanzun nan fillo bai ce min komai ba batun auren nan!..na sanar da ita irin zaman da mukeyi tun bayan dawowata,har yanda yan'uwansa suka juyamin baya.
Safiya kamar zatayi kuka sabida tausayi...ta shiga bani hankuri da magana masu shiga jiki...daga baya tace ki kuma dage da addu'o'i sosai sabida sanin da nayiwa Hajiya zubaida sai da haka....idan akan abinda take sone,ba shakkar yin komai ko da kuwa za'ayi fansan rai ne.
Ido waje nace daman kinsanta haka?
ta da'ga kai..tace na santa,mahaifinta da mahaifin mijina wa' da kani ne,uban su daya,kiwa da uwarsa.
Cikin kaguwa nace me kika sani game da ita?
Hmmm...idan nace zan baki labarin ta yau nan zamu kwana, amman kadan daga cikinsa shine hajiya zubaida wace ta kai kimamin shekaru 29,haifafn garin kaduna ce.ita kadai ce a gun iyayenta.
Babanta hamshakin mai kudine,yana da kanfunoni a nan kasar har ketare,kasancewan hajiya zubaida kadai ce suke da,ya sanya sun nuna mata so da ga'ta..ta taso cikin tarairaya,da ga'ta ga shagwaba.
Ba abinda ta sani sai takama da wulakanta mutane.gashi ta tsani talaka da talauci,haka take wulakanta masu aikace aikacen gidan wai don ta tsani talaka.
Iyayenta sun nuna mata ba abinda zata nema ko bukatu a duniyar nan ta rasa shi ko ya gagareta,ko da kuwa za'ayi fansar rai ne.sabida haka komai isa-isa takeyi,da kuma goyon bayansu.
Tarbiya kuwa ta rasa shi,sabida bata shakkar iyayenta balle dan adam...su suke shakkarta gudun bacin ranta.
a sanadiyar ita da mahaifiyarta yan'uwa da abokan arziki na mahaifin sun wareshi daban...mahaifiyarta kuwa akwai kokari gun shige-shige da bin bokaye da malamai don haka ina me baki shawara da ki rike addu'o'i su zaman maki takobi,ki kuma tashi tsaye da ibada domin kare kanki da'ga shairin hajiya zubaida da mahaifiyarta.Allah shi tsare.
Read More »
Designed by Jide Ogunsanya.