Pages

Sunday 29 December 2019

SOYAYYAR MU👫 58

SOYAYYAR MU👫🏻

      || Page 58 ||

By Aisha Gana (Ganarious)


Assalamu Alaikum Readers of Soyayyar mu!
Trust you are doing good. I'm so sorry for not continuing/updating you guys with the story.
By Allah's will, i will continue from where i stopped.
But! I really love to hear from you. If you can't drop your comment here, you can send your view to ganarious98@gmail.com
Thank🤗.

     *       *        *         *
Bayan da Dr. Abdul'Afeez ya tsawatar wa ilham, ya kuma kafa mata doka cewan kullum tazo tayi signing a gun sa, sabida ya tabbatar ta zo din.
    Hakan ya farantawa Hisham rai, ya jidadi sosai, ko babu komai zata chigaba da karatunta.
Ba shi kadai ba, har kawayenta, da Nura da abokansa kowa yayi farin ciki da haka. A yayinda ita kuwa ranta yayi baki. Ta raya a ran ta cewan ai kuwa Dr. Abdul'Afeez bai isa ya sanya ta abinda bata yi niya ba. Don haka baza ta je din ba, sai dai yayi duk abinda zai yi.
Washe gari su yusrah sun kammala shiri, ita kadai ce suke jira, wankan ma ta ki yi balle ta sanya kaya, nan suka shiga yimata magana,suna roko da lallashin ta, amman ta ki sauraron su!
Haka lectures din ranar ya wuce su, sabida ita, suma suka ki zuwa. Tou amma abin godiya shine a ranar ba ta da course din Dr.
          *    *     *        *
Tun bayan Sallar Asubahi, yake cikin Anashuwa, kallo daya zakayi masa ka fahimci hakan.
Sky blue shadda wanda ya sha aiki da dark blue zare ya ciro ya sa, bayan ya yi wanka ya bi ilahirin jikinsa da Arab oil perfume.
Abokan sa na ganin haka, suka soma zolayar sa. " yau fa zaka rudar da ya'yan turawa", kana sane wannan shirin naka na rudar da su.
Murmushi yayi ba tare da ya maida masu maganar ba.
Manya kayan al'adar malam bahaushe yana yiwa Hisham kyau sosai idan ya saka, duk ranar da zai saka su sai ka gan yan'mata har maza suna zu gunsa suna daukan hoto da shi.
 Bangaren su ilham kuwa, tun bayan sallar asubahi din, su Naziha suka shiga damuwa, suna shaku kar ilham tace baza je lectures din ba.
Haka kuwa ta faru! Ganin lokaci na kurewa bata shirya ba ya sanya su sanya ta a gaba, suna mita "Haba ilham, please don't do this.
Kallon su matayi ba, a fusace Amarah ta mike "tou ku tashi mu tafi, tunda dai ta nuna babu mahalukin da ya isa da ita"....
Duk jikin su yayi sanyi, hakan ya sa yusrah ta dafa kafadar ta "Haba ilham! Allah ma fa anai masa mafi munin laifufuka kuma da zarar ka roke shi zai yafe maka, balle mu.. Wannan abun fa kan ki kike cutarwa ba wani ba, kin sawa kanki damuwa, kin ki zuwa lectures gashi kina son ki batawa kanki suna gun malamin ki, don Allah ki manta da komai mu cigaba da rayuwar mu kamar da.
Kuka ta somayi! Nan suka shiga lallashin ta, sai da tayi me isar ta, sa'anan suka taimaka mata tayi wanka, ta fito sannan suka nufi cikin makarantar.
Tunda ya soma lectures ya ke duban hanya ko zata shigo, gashi har ya kusan gamawa bata iso ba, hakan ya sosa masa rai...
Yana matakin maimaita abinda ya koyar, ta shigo!
Ajiyar zuciya yayi, sai kawai ya tsinci kansa da farin ciki. Nan ya shiga maimaita duk abinda ya koyar har sai da wani malamin ya shigo.
   Itace ta farko da ta fara barin ajin, sa'anan sauran daliban.
A hanzarce ya fito shima, yana waige waige ko zai gan ta. Cikin nasara kuwa ya hange ta jingine da wani icce, don haka ya nufi gurin.
Da sallamar sa ya isa gurin, ta juyo ta dube shi ba tare da ta amsa ba! "How are you doing Aisha?" ya fada yana me kallon fuskarta
Ta dube shi sukayi ido hudu, sai ta dago ta tofa masa yawu!
A hankali ya sa tafin hannunsa ya goge. Ya sake duban cikin murmusawa yace.... Idan har hakan zai sa ki huce  ki yafe min, a shirye nake da amsan hakan, please.
Bata dube shi ba balle ta tamka masa, nan ya shiga bata hakuri..i'm so sorry Aisha.
Bai ankara ba ya ji kukan ta... Subhanalillah, har cikin ransa ya ke jin wannan kukan nata, ya rasa shin rungume ta zai yi ko me...
Cikin rudewa ya shiga bata hakuri, yanzun kam da karfi take kukan, duk masu wucewa sai kallon su keyi.
Suna a haka, Nura da tawagar sa suka iso! Shi din ma a rude ya karasa gab da ita da niyar ya rungu me ta, hannu ta sa ta ture shi.
A hasale ya karasa gaban Hisham "You son of bich" yana fadin haka yasa hanu ya ture shi a kirji. Ya kuma sake matsawa kusa da shi zai kai mashi duka Hisham ya rike hannunsa gam! "don't try that! I'll smash you" ya fada tare da ture masa hannun nan abokan Nura suka yo kansa ga baki dayansu suka shiga dukan sa!
Ganin su duka shi kadai ya sanya ilham shigowa tsakiyar su tana kokarin raba fadan, amma ko sauraronta basu yi ba, sai fadin take "Enough" "Enough"!! Enough of this! Duk da haka basu daina ba sai da masu kai da komawa suka raba fadan.
Kashe gari ma, sai da ya kusan gama lectures ta iso. Amman yau bai sami damar maimaici ba, sabida wani malamin zai shigan masu, kuma shi din ma yana da lecture.
Don haka bayan lectures bai sami ganin ta ba.

Read More »

Thursday 26 December 2019

RIKICHI 4

RIKICHI
Episode 4
     By Aisha Gana (Ganarious)

||if you're interested in the continuation of SOYAYYAR MU, please send a message to ganarious98@gmail.com  thank you||

   Ciwon kakan mu yaki ci, ya ki cinyewa. Gashi ba wanda ya taimaka masu cikin yan' uwa ko mutan gari.
Sun nemi taimako har sun gaji. Haka yana matukar bakantawa Hajiya Asabe rai, sai ta kuma fara rayawa a ranta, cewan akwai sa hannun mutane. Daga nan kuma duk wayewar gari sai tayi ta maganganu,tana bace bace.
  Tafiya tayi nisa, anzo lokacin da abin ci yake gagaran su a gidan,duk da manya ya'yan sun mike da nemowa!
Shekarun mahaifinsu hudu a kwance, sai ranar wata alhamis ,da yammaci yace ga garin ku nan.
  Rayuwar yunwa da talauci su abba suka tsinci kansu da shi. Yayunsa mata da kannensa, suk wace ta sami miji ba ta bata lokaci.... Mazan kuwa ko wannensu ya dage da nema, daga mai zuwa yin dakko, sai masu tura baroo da dai sauran su.
Abban mu na cike shakaru Ashirin, ya shiga garin minna nemawa kansa aikin. Cikin nasara kuwa ya sami aikin wanke motoci, sai dai shi a gidan mutumin da ya dauke shi aiki zai zauna sabida mutumin ya bukatan a wanke masa mota ko wace safiya kamin ya tafi aiki.
    Alhaji yunus, shine wanda ya dauki Abban mu aiki, matar sa daya da kuma dan su kwaya daya tak! Alhaji yunus mutun ne me kirki da daraja dan Adam.
Idan me karatu zai gan yanda yake wasa ya kuma sakewa abba ka ce ko dan'uwan sa na jini ne!
Nan da nan abba ya goge kamar ba shi ba. Tou yana samun lafiyayar abinci ga kuma kwanciyar hankali.
Albashin abba naira hamsin  ne a lokacin (A lokacin kudi na da darajansa), bayan albashin, su suke ciyat da shi, su kuma tafafar da shi. Haka idan anyi hutu za shi ganin gida, matar alhaji yunus zata dibi kayar sawan ta, da na dan ta hade da na alhaji yunus din ta bawa abba ya kaiwa yan uwan sa! Ba kaya kadai ba har da su mayukan shafawa, sabulai da dai sauran su.

A duk lokacin da me koyar da dan Alhaji yunus ya zo, sai abba ya dauko littafi shima ana koya ma shi.
Da Alhaji yunus ya lura da hakan sai ya tambayi Abba ko yana da ra'ayin karatu ne, amma yace eh, inason karatu sosai, sai dai hakan bazai samu a rayuwata ba!
Sabida me? Alhaji yunus ya nemi sani
Cikin sosa ke ya abba yace sabida shekaru na oga!
No! Shekaru ba za su taba hana ka karatu ba, idan dai kana da ra'ayin karatun ni me taimaka maka ne!
Nan abba ya nuna farin cikin sa, tare da fadin ya amince, zai yi karatun.
A cikin satin nan, Alhaji Yunus yai masa komai na makaranta. Sai da abba yayi kwala, sabida farin ciki, da kuma godiyar Allah da ya hada shi da mutun irin Alhaji yunus.
Abokan Abba da suka ji labari, dariya sukai ta yi masa, wai bashi da hankali.
Abba na akwai kaifin basira, duk da shekarunsa, kwakwalwarsa tana da kaifi. Ganin kwazon abba ya sa Alhaji Yunus yana ta tsallakar da shi daga wannan ajin zuwa wancan aji. Don haka shekaru biyu da rabi abba yayi a primary.
Da taimakon Allah da taimakon Alhaji yunus abba ya gama secondary cikin kankanin lokaci, yana gamawa Alhaji Yunus ya nema masa aikin yi ya kuma nema masa gida.
Bai jima da fara aikin ba suka maida shi portacort, yana aiki kuma yana zuwa makaranta watau university kenan.
    Cikin kankani lokacin Allah ya Azurta abba. Hakan ko bai sa ya manta yan'uwansa ba, duk bayan kwana biyu yake yi masu aike, ko kuma ya zo da kansa.
Abba ya gina masallatai, ya gyaran gidan su, yayi kannesa maza gida sa'anan matan ya basu jari.
Ganin haka ya sa mutanen gari kawo masa tayin ya'yansu.
  A portacourt din abba ya hadu da "Hafsat"
A ranar wata asabar, da sanyi safiya abba ya fito zai tafi gun aikinsa, sai ya hange ta saman keke, da alama tana motsa jiki ne. Tana isowa dai dai gun sa ya tsayar da ita, bayan gaisuwa bada bata lokaci ba abba ya shigar da kansa domin kuwa idon sa na kaiwa kanta ya ji babu wace yake so sai ita.
Murmushi tayi masa, hade da fadin zanyi tunani.
Read More »

Saturday 21 December 2019

A REMEDY FOR DAMAGED HAIR.

A REMEDY FOR DAMAGED HAIR.
  Using Avocado for hair mask prevents your hair from damaging.
Avocado paste helps in hydrating, repairing, strengthen and boosting shine and softens dull hair.

Things you need.
1. Fresh of one ripe avocado.
2. One teaspoon of raw honey.
3. 2 teaspoon of virgin coconut oil.

How to use.
~Mash the avocado in a bowl until a paste is formed.

~Add honey and coconut oil and mix.

~Apply mixture to hair and leave for 30 minutes.

~ Rinse out with warm water and towel dry.
Read More »

Wednesday 18 December 2019

RIKICHI 3

      RIKICHI episode 3
Assalamu Alaikum Ganarious Blog viewers🙋! I appreciates you all.

if really my stories are interesting, please drop your comments.
You can also email me at ganarious98@gmail.com

       *****************
Cikin barci ana kwankwaso min kofa. A hankali na bude idanuwa na, hade da yin yar siririyar tsaki a yayinda nake saukowa daga saman gadon.
"bana fada maku idan ina barci a daina tashina ba? Na fada a yayinda na bude kofar.
   Anty ce tace a ta'da ke, dazun ta aiko kofar a rufe sai tace a kyaleki, Abba ma ya dawo yayi tambayarki mun fada masa kina barci, shine yace idan kin tashi ace maki ki kira shi a waya ku gaisa. Yanzun kuma kinyi bakuwa, shine Anty tace na tado ki, kiyi sallah.
Tunda ta faro maganar bata tsaya ba, sai da ta kai karshe, ni kuwa na tsira mata ido.
Yanzun bakuwar ta zo?
Tun dazun fa ta zo, don har tayi sallah a dakin Anty.
   Ina take yanzun?
Tana falon Anty.
Ok, je ki gani nan zuwa!
   Daman da nayi wanka ban sanya komai a jikina ba, bada dogon rigan da na zira kawai, don haka na sanya kaya hade da undies sa'anan na fito zuwa falon Anty.

   Da sallamata na shiga, ganin ko wacece yasa na dan murmusa hade da fadin "Ayyah, ashe ke ce kika zo, sannu da zuwa"
Itama cikin Anashuwa ta amsa "eh ni ce, ina yini"
Lafiya lau, ya gida?
Lafiya lau suke, ta maida min martani, nan dai muka yi yan gaishe gaishe, bayan nan sai kuma mukayi shiru dukan mu.
 Mun dan dauki lokaci, ba wace ta kara cewa ufan, bayan gaisuwart, daga bisani  nace mata tou ya ya zancen maganar?
  Eh daman shi ya kawo ni.
Okey, tashi muje daki na, sabida kar yaran nan su zo suna damun mu.
Har ta mike nace "oh! Dan bani minti shida nayi sallah"
Murmushi tayi tare da fadin babu damuwa, na umurci layu ta kwaso mata hoto albums din mu.

Bayan na idar da sallah muka shige dakina wanda yake tashin kamshi ta alfarma! Gashi sanyi A.C ya garwaye dakin.
Tou bisimillah, ke nake sauraro, ha fadi hakan A yayin da nake gyara zamana.
  Da farko dai sunana maryam Idris isah, nayi karatun primary da secondary a El-Amin da ke garin Minna. Mahaifina Alhaji idris haifafen garin Suleja ne, mahaifita kuwa yar garin kontagora ce sunarta Amina, mu kuma muna kiran ta da Umma.
 
        **************
TUNA BAYA(asalin labari)
         **************
Mahaifin Alhaji Idris a lokacin shine Sarkin Noma, yana da dan arziki dai dai gwargwado. Matansa biyu, da hajiya Asabe da Hajiya Larai.
Hajiya Asabe itace babba, ya'yanta goma sha Uku, maza biyu, mata goma sha daya.
Sai hajiya Larai, mahaifiyar Alhaji idris kenan, me ya'ya bakwai. Uku maza hudu mata.
Alhaji idris na da kimamin shekaru goma sha biyu zuwa uku, mahaifin su ya sanya su a primary, ba'a shekare ba mahaifin nasu ya soma ciwo. A wannan shekaran basu samu natsuwar yin gona ba, gashi sun sayar da anfanin gonar su don nemawa mahaifinsu magani.
Sun je asibitoci ba iyaka, amma an kasa gano ciwon, daga karshe likitoci sun basu shawara da su koma gargajiya.
Read More »

Saturday 14 December 2019

RIKICHI2

RIKICHI 2
  By Ganarious

  Duk ranar Asabar aiki muke a gidan mu kamar baza'a yi ba kuma.
Sakamakon irin baccin da nake ji, na haye kan gado bayan da na idar da sallar Asubahi.
Kamar minti talatin da kwanciyata naji saukan hannun a jikina ana bugu na, a firgice na mike, duk da na riga da nasan ko wacece.
.....tashi don ubanki, yau duk aikin gidan nan kece zakiyi su.
A sanyaye na sauko kan gado zan nufi hanyar toilet.
Ta fizgo..hade da fadin shegen wankan nan da zai dauke ki awa da awanin baza kiyi shi ba sai kin gama min aiki. ... Wuce kije ki gama komai har breakfast, kamin yara su tashi.
Cikin rashin damuwa na karasa gun wardrob domin sauya kayan bacci, zuwa ta aikin gida. lokuta da dama idan dai abba yayi sakamakon fita, ire iren abubuwan da ke faruwa kenan, idan da sabo na saba.
Tunda na fito daga dakina har na kai kicin ban hadu da kowa ba hatta masu aiki duk suna daki.
Sai da na kammala komai, sa'anan Rahama da Hauwa suka fito, ko waccensu da dar-dar takeyi. Na wuce ta tsakiyansu ba tare da na tamkamasu ba.
Dakin yara na nufa, na hada masu ruwan zafi nayi masu wanka tare da sanya masu kayan islamiya sannan muka fito na hada masu abin kari.
Suna tsaka da ci, anty ta fito.
"Sannu da aiki zee"
Yauwa anty kin tashi?
Eh! Kin gama aikin ne?

Eh, na gama, na bata amsa.
Yauwa ko ke fa! Idan banyi maki haka ba baza ki iya komai ba wai ke yar gata.

Mmmh... Wallahi Anty ke ce dai kike ganin ban iya komai ba.
 Shikenan, a hado min nawa abin karin.
Na nufi kitchen na hado mata. Thanks ta fada hade da murmushi.
Je ki dakina ki tado Amira ta yi kari, amman kiyi mata brush tukun kamin ku fito, kinsan ta da rigimar ta!
Na mike zan tafi dakin ta, sai kuma tace masu aiki fa, kin kai masu abin karin su kuwa?
A'a, idan su Layu sun gama zasu mika masu.

No! Ke ce zaki kai masu, ta fada ba tare da ta dube ni ba.
Kai...Anty!
Eh... Har su Rahama ma kece zaki kai masu, training nake baki idan kinyi aure gidan yawa shikenan kin huta.

Bayan kowa yayi break, anyi wanka, anty ta kwashi yara don ta sauke su a islamiya, ita kuma ta wuce gun kitso daga nan.
Suna wuce wa na fada bayi, nayi wanka.
Rahama! Rahama!!
Na'am Anty zee gani.
 Don Allah ku daura abincin rana da wuri,ni zan kwanta kuma kar wace ta tashe ni
Tana wucewa na haye saman gado sai bacci.
Read More »

Friday 13 December 2019

UNIQUE TONING SOAP

Cry no more!
Here we teaches you how u can do it yourself organic glowing soap that make your skin look like African-American lady.
Things you needed.
*Licorice powder
*Sandal wood powder
*Turmeric powder
*Cinnamon powder
*Miracle powder
*Rice powder
*Arbutin powder
Kojic powder
*gluthane powder
Snowwhite powder
*vitamin oil
*carrot oil
*coconut oil
*glycerin
*Honey
*lime juice
*lemon juice
*Aloevera gel.
*ghana soap.
*yoruba soap.


Procedure!
In a clean mota, put your ghana soap and yoruba soap, add all the above mention ingredients and pound thoroughly until mixed and smooth.

Read More »

RIKICHI 1

RIKICHI

 Bismillahir rahmanir rahim.

Da sauri da sauri ta ke tafiyar, wanda dayawan mutane da basu san ta ba, su ke dauka salo da yanga ce.

  Marhaba da isowa gimbiya ranki shi dade.... Wata murya ta fada hade da fadin "karaso ciki mana"

Ah'ah sauri nake, gobe idan da rai da lafiya zan dawo.

Ki shigo mana, idan na karasa wankewa wannan sai na wanke maki?

Ban tsaya sauraronta ba, nayi tafiya ta. Jiran nake motoci da su adaidata sahu su tsakaita na tsallaka zuwa dayan gefen titi. Sai faman waige waige nake ina mai kallon hagu da dama ta, ban ankara ba sai jin nayi an taba  min kafadata.
A firgice na waiga. Hade da fadin subhanalillah! Nan ta ke na shiga yiwa Allah tasbihi.
Kallon kallon muke yi a yayinda ababe da dama suke ta aukuwa a zuciya ta "yau kam nayi gamo da aljana"
   Maganar ta ce ta farfado da ni. "i m very sorry, bani masaniyar zaki tsorota haka, tun da kika fito daga saloon din nake maki sallama, amma da kamar baki ji ni ba, shi yasa na biyo ki
 Ba komai, na fada hade da yin ajiyar zuci.
  Ta nisa, sa'anan ta dube ni cikin ido "taimako nake son kiyi mun"
Cike da mamaki nace 'taimako?

Ta daga kai' alamar eh kenan
Cike da mamaki nake kallonta, sabida batayi kama da wace ke neman taimako ko wace iri bace. "wace irin taimako kenan?  Na nemi sani.

Mmhhh.... Ban san daga inda zan faro maki ba, amma ina ganin sai na baki labarin kaina tukun sa'anan zaki fahimce ni.
Na dubi agogon hannuna, sannan na dube ta yanzun dai ina kan hanyata ne, amman ga lambar wayata da addireshi na, sai ki neme ni. Tayi godiya sa'anan mukayi sallama.
Read More »
Designed by Jide Ogunsanya.