Pages

Sunday 24 June 2018

Real 47 OF SOYAYYARMU

*SOYAYYAR MU👫*
        By Ganarious.

<><>Assalamu'alaikum yan uwa maza da mata. Inayi mana barka da shan ruwa,barkan mu da Sallah, ubangiji Allah shi karbi ibadun mu, shi amsa mana addu'o'in shi biya mana bukatocin mu shi kuma sakama mana da gidan aljanna...Allah ya nuna mana watannin ramadan masu zuwa(cikin raai da lafiya)
Allah ubangiji shi maimaita mana.
*Allahumma ameen*

*BARKAN MU DA SALLAH*🤝🏻

<><>special greetings to ganarious.blogspot.com/ followers and visitors💞

<><>makarantan soyayyarmu i heart u all.

<><> *Faty bayero*
          *Nazee yareema*
           *Hidayat yusuf*
           *Zuwairah shehu*
            *Rukky dogon daji*
             *Sis Salfat*
             *baby hajara*
              *haj. sa'adat mubi*
              *Aisha gana(namesake)*
*ganarious book series members*
*Hausa novels groups members*
Da sauran wa'anda Allah be bani ikon rubuta sunayensu ba,special greetings to u all.

*Mutan kenya ban mance ku ba,one love keep us 2geda*💞🤝🏻

        Page 4⃣7⃣(real)

          TUNA BAYA..
Aishah mustapha Buba, wace muka fi sani da ilham haifafan garin kaduna ce.

Ilham yarinya ce me kyan gaske,ga ilimin addini da ta zamani.
Ga kyan tarbiya da hali.
Babu mahalukin da zai kalli ilham,bai sake kallonta karo na biyu ko fiye da hakan ba.

Surar da ki'ran jikin ta kawai abin kallo ne ballantana  a kai ga fuskarta.

Fadin malam bahaushe '"mutum dan tara ne,bai cike goma ba"...toh tabbas akan ilham zani mu'sa wannan maganar domin kuwa ta cike goman,har ta goce.

Duk abinda ake so ga macen kirki da nuni ilham ta hada.

  Bayan mutuwan auren iyayenta suka rabu.
Mahaifinta bai kara wai-waiyansu ba, haka ma yan uwansa.
A lokacin cin da kakarta watau mahaifiyar mamee ta dauke ta zuwa kasar ladon, sai ta baro ta a can din domin halin ko in kula da mamee take nuna masu. Nan ta cigaba da karatun ta har sai da kakarta ta koma ga Allah sa'anan mamee ta dawo da ita gunta, sabida tsana da dan uwanta ke nuna mata  yana fadin itace sanadin mutuwar mahaifiyarsu.

Bayan da mamee ta farfado, ta dau na annabawa.sai tayi kokari ta yakinci zuciyarta ta dawo normal.
Makaranta masu kyau ta sanya ya'yanta.
Turkish international college ilham take zuwa,a yayinda sauran kannenta ta sanya su a *Imperial schools*.
Ita kuma mameen ta soma aikin lecturing a university dake cikin garin kaduna watau K.A.S.U.
Ilham da sauran kannenta sun samu kulawa da tarbiya fiye da zaton me karatu, mamee bata yi sakaci ko wai don aikinta ta dannewa yaranta hakkinsu.
Takan wa're lokaci tace masu "today is for u guys"....tana yi masu tambayoyi ko kuma a je yawon shakatawa,hakan yasa masu kusanci da shakuwa mussamma dan Autan ta wanda ta sangarta domin tausaya masa takai.
Da shike ilham tana da wayau a lokacin da iyayenta suka rabu,kuma ta wayi mahaifinta sabida tsananin so da shakuwa da ke tsakaninsu, don haka da ta kwana biyu ba ta ganshi ba,sai tana tambayar mamee  'ina baba na'?
"tun mamee na fadin babanki baya nan har ta kai ga cewa babanki ya mutu"
Bayan da ta girma ta fara mallakan hankalinta sai tacewa mamee "toh ta kai ta gun yan uwan babanta mana"
Zaunar da ita mamee tayi tareda da yi mata kashedi..."daga yau, idan ba kina son nayi fushi dake ba , kada ki kara furtawa cewan nakai ki gun yan uwan mahaifinki......kina jina ko?
Kai ta daga...
Yauwwa...don haka kiyi shiru da bakin ki.
Ilham ta ji alaman rashin gaskiya tattare da maganar mamee don haka tayi alkawarin fidda kanta daga wannan duhun da mamee ta sanyata.

         **         ***         ****
Bayan ilham ta kammala karatun ta, ta sakandiri mamee ta ba ta daman da ta zabi ko wace kasa take sha'awa da kuma son zuwa domin cigabawa da karatun ta.
Ilham ta ce wa mamee ba ta da zabi, don haka duk inda mameen take ra'ayi ya kuma kwanta mata a rai nan za ta je.
     *UNIVERSITY OF LONDON*(kings college), shine makarantar da mamee ta zaba da ilham ta je.

Cosmetic dermatology shine   course din da ilham ta ke ra'ayi, don daman tun tana yar karamarta take sha'awar  duk wani abu game da fatan jikin dan adam....a lokacin da    take sakandiri,ba ta aiki sai bincike da neman sanin duk wani abu da ya shafi fatan dan adam,kamar lafiyar fata,ciworwukan fata, da kuma yanda za'a magance da  dai sauransu..a bisa ga wannan dalilin yasan ta zabi fanin fata, don taimakawa matan nigeriA wanda yau burin su bai wuci su gan cewan fatan su na walkiyaa kyalli ba.

Daloli masu yawan gaske mahaifin mamee ya baiwa ilham ba tare da mamee ta sani ba.
  Ya kuma gargade ta da kar ta sa ke ta nunawa mamee kudin.
Yan'uwa da abokan arziki duk sun kawo na kudin sallaman ilham.
Ganin irin kudi da abin arziki da ilham ta samu ya sanya mamee ta sallame ta ba tare da ta bata wani abu ba.
"wadannan kudaden da kika samu,sun isheki har zuwa wani shekaran ma"..fadin mamee.
Dariya ilham tayi....a ranta kuwa fadin take ,kadan kika gani ai.
A tare suka tafi da mameen, sai da ta gan cewan ta kammala komai game da registration din makarantat, sa'anan ta yo gida.

Tunda ilham ta saka kafarta a kings college, dalibai har malamai ke kaunarta.
Ilham ta kasance tauraruwa a sararin samaniya..
Dalibai da malamai da dama sun sha tsai da ta a hanya, suna neman sanin ko ita kanwar  *AMEER* ce?
Tun tana maida masu a'a, har ya kai ga idan suka tambaye ta a maimakon ta amsa ,sai ta tambayesu wai yaya wannan AMEER din yake ne?

Wataran ta fito daga dakin karatu, watau labrary, rike da takardun ta,bata ankara ba sukayi karo wani.
Ta duka ta dauki takardun ta da suka zube,ta da'go da niyar bashi hakuri sai tagan irin kallon renin hankali da yake yi mata.
Siririya tsuki tayi tare da ratsa ta gefen sa.
Har tayi nisa da tafiyat,sai gashi ya biyo ta da dan gudu gudunsa,a gabanta yayi tsaye...
"watau sabida kingan yayank i yana yiwa mutanen renin wayau son ransa ba tare da an taka masa birki ba,shi ya baki daman ke ma kiyi ko?...sabida rashin tarbiya,kin bangaji mutun kuma kinyi tafiyarki ba tareda kin iya furta sorry ba?...toh wallahi ki bincika kiji ko shi yayan naki bai isa yayi da ni ba ballantana ke..

Kallonsa take,.....murya kasa kasa tace "Amman dai lafiyarka kalau?,...daga kun gan kamani sai kuyi concluding cewan wannan dan'uwa nane,har kake cin zarafi akansa??.....
Shiru yayi yana dubanta .
Ta cigaba da fadin da alama, akwai kiyayya a tsakaninku, don haka kai tsaidashi can atsakaninku......excuse me ta fada tayi wucewarta.

Daga wannan lokacin,duk sa'anda zata shiga labrary, toh zata tarar da wannan bawan Allahn.
A hankali ya soma yi mata magana tana basarwa, har ta  kai ga amsa masa.
Ganin kulawa da shakuwa na neman shiga tsaninsu,sai ta nema da san ko shi wanene, sabida yanayinsa da komai nasa da takama yake yinsa.

Hidayat yar'year 2,wace suke daki daya da ilham tana karanta dermatologysurgeon ne,ganin course daya suke karantawa da *NURA* kuma mataki daya suke, ya baiwa ilham daman bin ta kanta domin sanin wanene Nura.

Zaune suke kowanensu na ninke kaya.
"yauwwa sis, don Allah ko kinsan wani da ake kira nura a department din ku?"
Nura Abubakar kike nufi?....

Eh toh, ban san surname dinsa ba gaskiya.
Tabbas shi din kike nufi.
Watakila......

Kwarai kuwa nasan Nura...ai nura sananne ne,ba dalibi ko malamin da bai san da zamansa a wannan makarantan ba.

Matsowa kusa da ita ilham tayi..."yauwa fadamin duk wani abu da kika sani game dashi"

Shi dai Nura yan asalin kasar najeriya ne,amman anan aka haife su,anan suka tashi har girman su.
Mahaifinsa yana daya daga cikin board management na wannan makarantan.
Su biyu iyayensu suka haifa, da shi da kanwarsa.a bisa ga wannan dalilin yasanya sun sangarta su,,ba wani tarbiyan kirki sai ta rashin mutunci.
  Nura baya ganin girman kowa, ganin yake kowa na karkashinsa, ga shegen daukan kai da miskilanci.
   A takaice dai, Nura miskiline,ga rashin Son karatu.
Kamata yayi ace yana can tare da yan uwan da suka tafi traininng a  kasar jamani,amman sabida bai sa   kai ba aka maida shi baya.

Kamar yaya ,an maidashi baya sai kace sekandiri skul?........ilham ce ke wannan tambayar.

Derma-surgeon cours ne da sai an shekara hudu ana karatunsa...ka'idan wannan cous din shine dalibai zasuyi shekaran farko da ta biyu a makaranta,shekaransu ta ukun sai a tura su wata asibitin sauya fata dake kasar germany don yin training.
Toh kafin a turasu, sai an bincika sakamakon jarabawan daliban tun daga shekararsu ta farko.
Wadan da basu cancanci zuwa ba,sai a maida su baya su sake maimata wannan shekaran,toh abinda ya riski nura kenan.ganin yake sabida matsayin mahaifinsa ba yanda za'ayi dashi a wannan makarantan.
Bashi da lokacin yin karatu sai adawa da Amirullah na wannan makarantan,kamar annabi da kafiri suke.
Yanzun mun dawo sa'o'in juna,a yayinda abokan tafiyarsa duk suna can a yayinda shi kuma yana nan damu sai wata shekara.

Cikin tausayawa ilham tace "Ayyah......har na tausaya masa..
Uhmmmmmm....don dai bakisan halinsa bane.

No comments:

Post a Comment

Designed by Jide Ogunsanya.