Pages

Monday 25 June 2018

Page48 of SOYAYYAR MU

*SOYAYYAR MU👫*
         By Ganarious
Page4⃣8⃣

  Sannu a hankali, shakuwa me karfi ta fara shiga tsakanin ilham da nura.

Ilham yarinya ce me fasaha da basira,da zaran ta fara abu, ko da ranar ce farkon farawar ta, sai ka gan ta gwanance.
Duk wani activities na makarantan, tana participating...hakan yasa tayi suna cikin kankanin lokaci, ba a makaranta kadai ba har sauran universities da suke kasar ladon,domin kuwa dayawa mutanen kasan da dalibai mamaki sukeyi wai bakar fata, daga africa itace *miss king's college*...wanda a tarihin wannan makaranta,basu ma baiwa bakin fata daman yin contesting ballantana a zabe shi
Sai kan ilham,kuma mafi abin mamaki wai yar'year one.

Muslim students activities organization(M.S.A.o), wanda mu anan nigeria, mu ka fi sani da (M.S.S),ta makarantan kings college sunyi marhaba da hidima da gudumuwar da ilham take bada wa,a dalilinta yan mata da dama sun soma zuwa gurin taron M.S.A.o, sabida hikima da takan yi anfani dashi idan zatayi tunatarwa.wasu kuwa sabida jin dadin kira'an ta suke hallarar gurin.

Shuwagabannin M.S.A.O, malamai da dalibai sun zauna yin meeting akan cewan wai ko za'a baiwa ilham Amiran makarantat....amman kuma akwai wace take rike da mukamin kuma yar aji biyu ce.
Wasun su sun hangi rashin adalci, idan akayi hakan duk da abinda ilham take gudanarwa a wannan organization din, Amiran bata yin rabinsa.
Ganin ba wata mukami da zasu bata, yasanya sunyi tunanin kirkiran mukamin da babu shi kuma wanda zai zo daya da ta Amiran, don nada ilham da wannan mukamin.

A haka ilham ta cigaba da haskawa a kings college ,duk inda ka shiga ilham,wasu suce kanwar ameer ,ba bu ranar da za'a wayi gari mutane biyu ko fiye da hakan basu yi mata zancen Ameer din ba,don haka ta matsu ta gan wannan Ameer din.

Da haka har aka shiga semestern karshe,daga wannan semestern zata shiga shekara ta biyu.
A yayinda daga wannan hutun za'a tura su nura training.
A wannan semestan ne kuma wadanda suka tafi training din zasu dawo makaranta.
Wata daya ilham tayi a gida nigeria,sa'anan ta koma kings college.

A satin da tayi resuming, ta fito lectures sai ta nufi department dinsu kawayenta watau naziha da Amarah.
Daga nesa ta hange su zaune, a saman kujerun da aka tanada don zaman dalibai.
Tana zama ta soma nishi sama sama....'yunwa'.....wayyoooo cikina,yunwa nake ji
Dariya suka shiga yi mata sabida yanayin da take maganat
"yusrah ta tafi nema mana abinci".....cewan Amarah,tana gama fadin haka,,, wasu gayu kuma dalibai suka iso gurinsu da sallamansu,daga alama musulmai ne.

Dukkaninsu idonsu na kan ilham,a yayinda suka nema guri suka zauna.
....'"Ammmmm.....don Allah tambaya muke,daya da'ga cikinsu ya fada yana duban ilham.
Bata amsa ba, sai ta'be baki tayi, tana dubansa.

Hakan ya bashi daman cigaba da maganarsa..."don Allah ke kanwar Abbakar ce?
Yau kuma da abbakar nayi kama?......oh ni! Wannan fuskan tawa me kama da ta mutane,mutanen ma maza wai....
Abbakar deen fa nake nufi.
Daga Ameer,yanzun kuma Abbakar.....ta fada tana me tafa yatsunta.
Nan su naziha suka fashe da dariya.
Dubansu tayi tace "ni ba kanwar Abbakar bace,asalima nice ta farko a gidanmu.
Cikin rashin yarda da maganarta waninsu ya fiddo wayarsa yayi kira....jim kadan akayi picking daga dayan bangaren.
Dukkanin mutan gurin suna jin abinda ake fadi a wayat,sabida loud mode ya sa.
....."guys how far"daga dayan bangaren ake fadin hakan.
""amman ka cika dan iska, ashe kanwarka ta sami addmission a nan kings din shine baka sanar da mu ba.

Wa ce ce kenan?

Ji ka da wata tambaya kuma? Wace kanwarka ke nan kings?

Kai.....wannan maganar banza kake fadi, ni fa na gaji da tambayoyin mutane,tun da muka yi resuming wasu ke kira na a waya suna tambayata......wai yaya yatinyar nan take?

Shiru sukayi gaba dayan su....."kana nufin kace ba kanwarka ko cousin dinka da aka kawo kings college?

Babu....ya fada a takaice,da haka suka shiga yin hira suna tambayarsa yaushe zai dawo.

Bayan. Sun gama waya da abokinsu,wanda suke ikirarin ya na kamah da ilham,suka mike tare dayiwa su ilham salllam da kuma ban hakuri.
Bayan sunyi nisa naziha ta dubi ilham tace...'ai kuwa yayan naki akwai cool voice"
Dariya su sake yi a karo na biyu.

A ka'idan kings college ko nace department din da ya shafi masu yin karatun fatan dan adam. A ko wani karshen semesta suna gayyatan manyan likitocin fata,da kuma malaman university daga kasashe daban daban,domin su zo su baiwa dalibai shawarwari.

  Ranar jumma'a, ita ce ranar da dukkanin dalibai, ma'ana daga ajin farko zuwa karshe za su hadu a babban dakin taro ta makarantan kings college domin sauraron shawarwarin wadannan mutanen da hukumar makaranta ta gayyato.
   A ranar ilham ta wayi gari da matsanancin ciwon mara, don haka ta yanke cewan baza ta halarci wannan taron ba.
Hidayat wacce suke daki daya,kuma department daya, ta kammala shirin ta tsaf. Duban ilham tayi tare da fadin "tashi mana ko a dad-dafene mu tafi"....

"ki tafi kawai ,bazan iya zuwa   ba"
Toh shikenan,Allah ya baki lafiya,ni na tafi...
Bayan da Hidayat ta fita daki, kai tsaye dakin su naziha ta nufa domin sanar masu halin da ilham take ciki.

Lafiyayyan abinci suka shirya mata, sa'anan suka nufi dakin ta rike da magunguna.
Kwance take tana bacci, Amarah ta sa hannu ta tayarda ita...."tashi ki yi breakfast ki sha magani,ki yi wankanki sai ki koma ki kwanta,
Da taimakonsu ta mike zaune,suka shiga bata abinci a baki....uhmmmm ilham yar'gata son kowa.

Bayan da ta gama ci,ta sha magani sai ta dan jingi ne da bango, jim kadan ta mike kamar wace aka tsakala.
Ta fada bayi tayo wanka sharp sharp,tana fitowa ta bi jikin ta da madarar turare ba tare da ta shafa mai ba.
Doguwar riga me kyaun gaske ta fiddo ta sanya a jikin ta,sa'anan ta bi lebbanta  da tsadaddiyar lip-balm dinta da take ji dashi.
Bin ta kawai da ido su naziha suke, sai da suka gan ta dauki jakka, sa'anan amara tace ba'a shafa mai ba, balle powder.

Kar ku damu....see u guys later ta fada a yayinda take hanzarin fita daga dakin.


Toh jira mu mana,muyi maki rakiya....cewan naziha.

Nop.....na hutassheku.

Sauri saur, gudu gudu takeyi, tana me nishi sama sama.
Daga wajen dakin taron take jin jawabi, daga alama, ba'a jima da farawa ba.

Tsaye tayi tana huci tukun,tana me busar da iska daga bakinta.
Sai da ta sami, natsuwa sa'anan ta kunna kai dakin taron.
Ta ko'ina jama'a, duk sunyi occupying kujerun, sai waige waige takeyi tana neman inda babu wani ko wata amman kuma a gaba,sabida ta ki jinin zaman baya,kuma kujerun bayan ne kawai. Empty.
Tana waigowa gefenta, ta hangi wasu empty kujeru a layi na uku, don haka ta nufi gurin.
Kafin ta shiga can inda empty seats din suke,dolenta ta bi gaban wasu dalibai domin kuwa kujerun a tsakiya suke.

A hankali ta dunga furta excuse me, su kuma suna janye kafarsu don bata damar wucewa. Da shike dayawan su sun waye ta,wadannda kawai basu san da ita ba sune wadanda suka dawo daga training.

Mutane hudu zuwa biyar da suke zaune daga farkon layin sun janye kafarsu don ta sami damar wucewa,da haka ta gifta ta gabansu tana fadin excuse me,idan kuma ta gifta sai tace thank you.
Da haka ta isa ga kujera ya shida,inda ba kowa zaune nan,ta so zama anan din, amman kujerar ta biyar da ta bakwai duk maza ne ke zaune akansu, don haka ta yanke shawaran karasawa can karshe inda ta hangi mace zaune.
Tana zuwa ta kujeran ta bakwai tace "excuse me"...ta dai gan sa'anda ya daga kafarsa,ta zo dai dai gaban sa zata gifta sai ta jita a kasa tifff....
"ta da'go tace masa oh sorry"....sa'anan ta mike ta karasa ta zauna.
Tana zama abinda ya faru ya soma dawo mata.....amman dai kamar kafa ya samin fa,da saninsa kenan,,don har ina ce masa sorry maimakon ya amsa sai kawai, ya da'ga min gira har da murmushinsa....nan zuciyar ta shiga rayamata cewan da saninsa ta fadi
Ya ja tsaki tare da mike wa a hasale ta dauki jakarta.
Ta nufi gunsa, tana isa ta daga jakar sama ta kwada masa a. Kai
Nan hankulan kowa ya dawo kansu,duk kowa ya da'go yana dubansu.
  "dan iska kawai"....ta fada rai bace,shi ko banda kallonta, ba abinda yake yi.

Doctorn da ke jawabi,yai shiru yana duban su, nan daya daga cikin malaman kings college ya mike..."the both of you should walk out of the hall"

No comments:

Post a Comment

Designed by Jide Ogunsanya.