Pages

Wednesday 6 June 2018

Page 46 of SOYAYYAR MU

*SOYAYYAR MU👫*
          By Ganarious.
Page4⃣6⃣

√°•<> inayi mana fatan alkhairi,ya yan'uwa.

√°•<>inayi mana nasiha da mu yawaita yi *SADAKAH* da taimako.

√°•<> kuna iya tura shawarwarinku....
👉🏼ganarious98@gmail.com

Ko ganarious.blogspot.com/

A facebook, Aisha m gana.
      Thanks🤝🏼

    Bai mu'sa ba, ya shiga ciki.
Ya taras da mamme tana jera abinci a kan dinning table.
"Mamee babanmu ya iso,na ce masa ya shigo,shi kuma yace na sanar da ke tukun.
...."je ka, ka shigo da shi,ni zan shiga wanka ne.

  Bayan da mamee ta fito wankan,ta feshe jikinta turarukan jiki masu classic kamshi,ga kuma arabian humra da ta fara shafe jikin da shi.
Abaya ta fiddo, wanda Aunty Hauwa liman me @Afrikabaya ta aiko mata.
Tabi le'benta da tender kia,ta oriflame sa'anan ta laulaye kanta da mayafin abayan .
Duban kanta tayi a madubi tare da rayawa a zuci....."da fatan ba nayi bane don na burge wannan mutum..."
Tsuki tayi a yayinda ta nufi kofa don fitowa.
A falo mujaheed ne da Abba tare da mahaifinsu.
Da sallamanta ta shigo cikinsu tare da samun kujera ta  zauna.
A hankali ya da'go yana dubata...."inakwana ya fada.
Lafiya....kawai ta maida masa.ba tare da ta dubeshi ba.
Na zo ne muyi sallama da mujaheed ,na kuma tqbbatar komai yayi dai dai, duk da bani da damar yin haka.
Shiru tayi bata amsa shi ba.
ya ciro envelop ya mikawa mujaheed...."ga wannan, 20thousand ne a ciki, ka yi hakuri ba yawa..
Haba baba, da ma ka bar su...
A'a...akwai hakkinku a kaina, kaddara ce ta sa a lokacin baya baku sami abinda ya kamata ba,don haka ba zaka gane komai ba yanzu.
Toh baba na gode,Allah ya saka da alkhairi,ya kuma sanya albarka..
Cikin jin dadin furucinsa alhaji buba yace ameen.
...je ka ka kwaso min jakkuna da zakayi tafiya da su.
Toh baba...
Jakkuna biyu ya kawo gaba alhaji buba..."ga su baba.
Dubansa alhaji buba yayi..."iya kan su kenan,?
Eh....
Ka gama shirya kayan, ba abinda zaka ciro ko ka sa?
eh...baba,everything is set.
Hannun ya sa a aljuhu,ya fiddo padlock,ma su dan girma ya rufe jakkunan....sannan ya mikawa mujaheed makullan.
Cikin darawa....yace baba kwado kuma?
Kallonsa yayi ba tare da yace wani abu ba

....jirgi ne ai,ba abinda zai faru...
Ya dafa shi,Kar ka damu,haka dai nake son ka tafi makarantan.
Toh inn'shaa'Allah.
Bayan nan ya shiga yi masa nasiha,daga baya yayi masa addu'a.

Ya mike zai tafi abba ya rike masa hannu yana fadin baba ba za ka raka shi abujan ba?
Kai ya girgiza,tare da duban inda mamee take, wace tunda ta zauna a gurin ko uffan batayi ba.
....'ni zan tafi", ya fada
toh an gode ta maida masa ba tareda ta dubeshi ba.

Baba toh ka dakata mana mu ci abinci tare?...murmushi yayi "a'a.....a koshe nake.
Ido waje yace...baba ba kaci komai na sani.

Mikewa mamee tayi tana fadin ku zo kuci abinci mu kama hanya ko?!...

Gam-gam abba ya rike alhaji buba wai ala dole sai ya zo sun ci abinci tare,ba yanda alhaji babu bai yi masa ba da ya tafi shi ya ci abincin amman yaki,da'ga baya ma cewa yayi idan har be zo ya ci abincin ba shima din ba zai ci ba,ya fada hakan ne a shagwabe.
Mamee da mujaheed kam sun dade da isa gun dinning har ta fara zubawa mujaheed abincin sa.
Ganin da gaske abba yake yi yasa alhaji buba amincewa...."ok, toh muje '
kujerar da ke fuskantar ta mamee ya jawo masa,sanna shima ya zauna kusa dashi.
Mamee ta mike ta zuba masu abinci.
Sosai alhaji buba ya ci abincin,yana ci, yana satan kallonta.
Bai ankara ba,sai ganin yayi plate din sa ba komai,ashe ita gimbiyar tana lura da hakan.
Ta mike ta sake zuba masa wani abincin.
"Na gode ya fada,yana kallon fuskarta.

Bayan da sun kammala cin abincin mamee ta yi kira blessing da ta zo ta tsabtace gurin.
Mamee ta dauko jakarta tana me yiwa blessing sallama da fadin zamu kai mujaheed airpot.

Bayan da an fita da kayan mujaheed aka shirya su a mota mamee ta dube su tareda fadin mu ta fi ko?..
Gaba daya suka mike har alhaji buban....suka fito haraban gidan.
Mamee ta kai duban ta ga alhaji buba..."idan kana ra'ayin ganin wucewarsa,kana iya biyo mu"
Toh na gode,ya fada.

Mujaheed ne a gaba,tare da direba.
A yayinda mamee da alhaji buba ke gidan baya,abba ne a tsakaninsu.
tunda suka soma tafiya ba wanda yace wa wani kala,tsakanin mamee da alhaji buba.
Sai abba da yake yiwa mahaifinsa tambayoyi akai-akai....shi kuma mujaheed sai dai ya jiyo ya yi masu hoto.

ZAUne suke a gurin da aka tanada domin zaman jiran jirgi.
Kiran ilham ne ya shigo wayar mujaheed.
Dariya yayi yana fadin anty kenan.....na san zaki kira da zarar kin gan hotunan,...
Wasu hotuna ta gani..? Abba ya nemi sani.
Hotunan da nayi maku a mota, shi na tura mata ta whatsapp.

.....hello anty.!
Kuna tare ne dukan ku?
Eh....ya maida mata.
Ok,zan kira video call yanxu.

KAshe wayan tayi ta sake kira, wannan karon video call ne.
Bayan da mujaheed yayi pickin ta umurce shi da ya baiwa mahaifinta wayan.
Nan suka gaisa, daga nan ya baiwa abba,abba kuma ya baiwa mamee.
01:07pm jirgin ya tashi...don haka sukai harraman tafiya.
Wanna karo a gaban mota abba ya ka'me,mamee da alhaji buba ne  agidan baya.
Ganin lokacin sallah yayi,ya sa mamee ta umurci direba da ya nufi gidan aminiyarta watau hajiya safiya da su....bayan nan ta kira hajiya safiya ta sanar da ita zuwan su.

Mamee da abba ne suka shiga cikin gidan, a yayinda alhaji buba da direba ke cikin mota.
Hajiya safiya na da'ga saman bene ta hange su,don haka ta sakko da gudun,ganin ta a guje ya sanya yaranta biyo ta su ma a guje....ta isa ta rungume mamee...
"Barka barka....marhaba da zuwa
Yawwa kawa ta.... ya ya lafiyar yarana?
Ga sunan..!

Dariya mamee tayi tare da juya wa gun yaran.....yawwa ya'yana masu albarka,kuna lafiya?...
Hajiya safiya ta sa hannu ta rike mamee zuwa falon ta.
Sai da suka natsu sannan mamee ta dube hajiya safiya..."tare da ba'ko muke fa"
Tau....wanene wannan ba'kon kuma?
Uhmmm....dan fillo ne.
Cikin da'fe kirji tace "dan wa....??
Dan fillo,mamee ta maimaita.
Dan fillo fa kikace fa?
Kai mame ta da'ga mata.
Ina kika hadu da shi?
Dafa ta mamee tayi....'akwai labari,amman ki bari inn'shaa'Allah, asabar zani shigo na labarta maki domin kuwa muna kan hanya ne yanzun.
Cikin mamaki hajiya safiya ta mike..'bara na aika masa ya shigo,kar yayi tunanin an wulakantashi.
Dan me suna mus'ab ta kira.
ta umurce shi da ya tafi wajen gida ya shigo da wasu baki maza.
bai jima ba ya shigo...'wai sun tafi masallaci inji me gadi.
Je ka kayi jiransu,idan sun dawo sai ka shigo dasu.
nan mamee ta mike don gabatar da sallan azahar.tare da umurtan abba yaje yayi sallah shi ma.
Bayan ta idar hajiya safiya ta sanar da ita cewan abinci na kan dinning da ta tashi ta je fara ci.
sun fito zasu nufi dinning sukayi karo da mus'ab.....
...mummy na fada masa,shi kuma wai ba zai shigo ba.
Shikenan, shiga daki ka dauko min mayafina.
Mamee da abba kam sunyi nisa da fara cin abinci, sa'anan alhaji buba ya shigo.
Hajiya safiya tayi masa nuni da gun dinning tana fadin "bisimillah"
A'a....alhamdulillah, ya fada tareda yi mata godiya.
Haba don Allah....wallahi sabida ku na girka abincin.

Allah sarki,toh ayimin afuwa.! A koshe nake.
Ba yanda hajiya safiya batayi da shi ba, da yaci abinci shi ko ya ki.
Ganin ba shi da niya ya sanya ta zuba masa juice .

Ta dibi abinci a plate ta baiwa mus'ab ya kaiwa direban su mamee.
Bayan mamee ta gama cin abincin tayi kiran hajiya safiya gefa....'akwai fruits a gidan nan"
Eh....akwai
Ok, bara na hada masa fruits salad,nasan zai sha a mota,don tun karin safe ke cikin sa.
Har zuwa gun mota hajiya safiya tareda ya'yanta sukayiwa su mamee rakiya.

Dubu daya alhaji buba ya fito da shi,ya mikawa yara...'gashi ku sayi alawa ko'
Godiya suka yi.

Sai da sukayi ni'a...mamee ta cire tubular bowl me kyan gaske..
ta mikawa alhaji buba..."gashi kasha,please kar ka mu'sa, na san kana tattare da yunwa.
Kallonta yakeyi, ba tareda ya karba ba, be kuma ce wani abu ba.
Ta sake duban sa..."gashi ko?
Ajiyan zuciya yayi,sanan ya sa hannu ya karba.
Na gode kawai ya fada...tareda yin bismillahi, sannan ya soma sha.
Ya gama sha ya maida murfin kwanon ya rufe...."Alhamdulillah" ya fada.
Ya juya ya dubi mamee ....na gode ya sake fadi.
Bata amsa masa ba,ba ta kuma dubeshi ba,sai dannan wayarta takeyi.
Shi kuwa ya tsai da idon sa akanta, ganin ba'ta niyar yi masa ya sanya shi dukowa..."ni fa,ni fa......so nake na maida aurenmu, ko ma nace na maida shi.
Nan ba bata da'go ba.
......'fillonki ne fa ke magana'..
Shiru bata amsa ba.don haka ya fita harkan ta.
Suna shiga cikin garin kaduna, Alhaji buba yacewa direba zai sauka.
Guri ya samu yayi parking mota...
Alhaji buba ya dubi mamee...'na gode sosai... a nan ma bata amsa masa ba, don haka ya budekofan ya fito zuwa inda abba yake zaune.
Dubu daya yamika masa....'gashi, idan ka isa gida lafiya kayi changy ka dau dari biyar kabaiwa direba dari biya...nayi niyar ba ka abinda ya fi hakan sai dai bani da halin sa,don haka kayi hakuri da wannan wataran zan baka wanda ya fi wannan din.
Toh baba....na gode,ya fada cikin fara'a da jin dadin kyautan da mahaifinsa yayi masa.
Alhaji buba ya kai hannu ya shafa kansa..allah shi yi makaalbarka.
"Ameen.

Tunda mamee ta isa gida ta rasa sukuni, furucin fillo sai yawo yakai a kwakwalwanta da kunnenta.....
Kai da komowa takai....wayarta da ta soma kara ce ta ja hankalin ta zuwa kan gado inda ta ajiye shi.
A hankali tayi taku zuwa gurin.
..."kawa"
"Kun isa lafiya?
Lafiya lau alhamdulillah,.....ke ce nake son kira yanxun fa, sai gashi kin riga ni.
Ai dole na riga ki...tunda ku ka bar gida na nake girgan lokaci,don bani son na kira kuna tare da fillo.na kasa hakurin sai kin zo ki bani labari,don haka nayiwa wayata lodi,yanzun ke nake sauraro...
Dariya mamee tayi.....haba kawa, ki bari mana ina kallonki,kina kallona? Ai ya fi dadin labari.
"Na ki, wallahi ban yarda ba, ko so kike na kasa barci?
Toh toh....mamee ta fada, tare da soma bata labarin komai da ya faru da'ga kan soyayyan Hisham da ilham har izuwa yanzun.
..'ikon Allah.".....Allah da ikon yake,sai ya hade su acan bayan sun rabu watau Hisham da ilham kenan.
Ita kuma hajiya zubaida, bata daddara ba....ba ta tunanin mutuwar ta?
Mmmmm....kawai mamee ta fada,.
Gaskiya ku tashi tsaye da addu'a, domin kuwa da zarar tayi nasarar fitowa toh Allah kadai yasan abinda zata aika kuma..
Haka ne, shima din tsoransa kenan...
Nan suka shiga tattaunawa har sai da kudin hajiya safiya ya kare tas.!.

*Ya'Allah kaji kaina,ka kar6i tubana,domin kai ne me kar6an tuba,kuma me jin kai..AMEEN🙏🏼*

*ya'Allah ka yafe min zunubai na...AMEEN🙏🏼*

*ya'Allah ka gafarta min abinda na gabatar da abinda na jinkirta, day abinda nayi a boye, da abinda nayi a bayyane, da abinda kaine ka fini saninsa, domin kai ne me gabatarwa,kuma mai jinkirtawa, babu abin bautawa da gaskiya sai kai...AMEEN🙏🏼*

*ya'ALLAH ina neman tsarinka da'ga tsoro da rowa da mummunar rayuwa da fitinar kirji da azabar kabari..AMEEN🙏🏼*

*ya'Allah kajikansa, kayi masa rahama, kayi masa afuwa,kuma ka girmama masaukinsa,kuma ka yawalta mashigarsa kuma ka wanke shi da ruwan sanyi da ra'6akuma ka tsrkake farin tufafinsa daga dauda kuma ka canja masa gidan da yafi gidansa da iyalin sa suka  fi iyalansa, da matar da tafi matarsa, kuma ka shigar dashi aljanna kuma ka kiyaye shi daga fitinar kabari da azabar wuta...AMEEN🙏🏼*
*Allahumma ameen ya'rabbil alameen*🙏🏼

No comments:

Post a Comment

Designed by Jide Ogunsanya.