Pages

Tuesday 21 April 2020

RIKICHI-8

RIKICHI.
Episode_8
     Assalamu Alaikum! Yan uwa masu bibiyar wannan labari, da fatan muna lafiya? Allah ubangiji Shi tsare mu, Shi kawo mana karshen wannan Annobar ta COVID19.

  Continuation.....
Sai bayan Sallar isha'i  Abba ya Shiga gida. Da shigar sa kuwa, ya nufi dakin Mummy Kai tsaye.

Ganin bata amsa masa sallamar sa ba ya sa nemi sanin ko lafiya?
Nan ta fashe da kuka, tana fadin "Matar Ka ce ke son Shiga tsakani na da uwa na" nan ta kwashe labarin karya, har abinda Bai faru ba ta fada masa, daga karshe ta fada masa Hafsat tayi Mata duka, kuma tayi alkawarin sai ta zubda Mata da ciki.... Duk a cikin sheshshekar kuka take maganar.
A fusace Abba ya Mike ya nufi dakin Hafsat, ya tarar da ita tana karatun Al'qura'ani me girma daga Alama tunda ta idar da sallan isha'in take karatun.
Nan ya tsinci kansa da samun guri ya sauna, ya na me kallon ta cikin sanyin jiki.
   Shiru_shiru Mummy bata jiyo hayaniya ba, nan ta Mike ta nufo dakin Hafsat din. A zaune ta tarar da Abba, ya kurawa Hafsat ido. Da Alama ma hankalinsa Baya jikin sa.. ihu ta saka, ta Shiga Kiran Abba Azzalumi wai Bai bi Mata hakkin ta ba.
Wani abin dubi kuwa shine, a duk lokacin da Abba yayiwa Hafsat cin mutunci, ko ya dake ta, Tou a ranar zuciyar sa zata rasa sukuni, barci ma bazai yi ba, sai dai yayita juye juye, daga karshe kuma ya biyo ta Yana me bata hakuri.
Wata sa'ain ya ce Baya sanin lokacin da yake yi Mata hakan, sai bayan idan yayi hankalinsa ke dawowa jikin sa. Hafsat takan sa masa kuka tace "ita dai ya maida ta garin su gun Yan uwan ta.

  Bayan Abinda ya wakana da zuwan su kakan mu, da sati biyu suka aiko wai Abban mu ya zo suna son ganinsa.
A ranar da ya isa, haj. Asabe ta aika Kiran kanwarta watau mahaifiyar Mummy kenan.
Bayan kowa ya iso, an zauna haj. Asabe ta kwashi dukkanin wulakanci da cin mutun da Mummy tayi masu da fada masu. Ta Kara da fadin tunda itace sanadin hada auren Abba da mummy, Tou tana son A yanzun Abba ya saki Mummy tunda abin na rashin mutunci ne..
 Wuf, mahaifiyar Mummy ta Mike, ta inda take Shiga ba tanan take fita na, ta wanke yar'uwarta tas_tas sa'anan ta Kara da cewa Abba Bai isa ya saki yar ta ba, tana fadin haka ta fisgi Jakarta ta barsu nan suna kallon kallon.
Abba dai hakuri kawai yake bawa Mummy hade da fadin, ba zai iya sakin mummy ba sabida tana dauke da juna biyu. Wannan shine sanadin da Kishiyar kakan mu, haj. Asabe sukayi hannun Riga da yar uwarta.

Watarana misalin karfe Tara na dare, Hafsat ce zaune da Dan ta Sameer suna kallo, sai suka ji an bugo kofa da karfin tsiya, a lokaci daya ita da Dan ta suka juya a firgice suna duban me shigowa.
Batare da tasan hawa da sauka ba, ta ki Duka na sauka a jikin ta, sai da ya tabbata tayi ligi-ligi sannan ya juya ya fita abinsa..
A inda ya barta nan take, ta kasa daga ko da yatsa ne, Dan yaron ta kuwa sai kuka yakeyi Yana me shafan fuskarta. Suna a haka Abba ya shigo a lokacin misali karfe biyu da rabi na dare. Cikin sanyi jiki ya karaso gunta, ya daga ta zuwa bathroom ya yi Mata wanka sa'anan ya sanya Mata Kaya. Ya Shiga kitchen Babu Abinci don haka ya hado Mata fura da Nono... Ya zo zai bata, ta ki amsa, sai hawaye da ke zubowa daga idanuwarta. Tun hawayen na zubowa tana kukan zuci yar kuka ya kubuce Mata tanayi da karfi. Abba ya rikice, nan ya durkusa Kan gwiwansa ya Shiga bata hakuri tare da Neman afuwanta, ya kuma yi Mata alkawari komai zai zo karshe, ta dunga yi masa addua' kawai.
Abba yayi lallashi akan ta sha nonon, sabida cikin jikin ta, Amma ta ki...sai da ta gan Yana hawaye sa'anan ta bude Baki tana amsa, Yana bata Yana ba Dan ta Sameer.
Sameer ne kawai yayi bacci a cikin su, Abba tagumi yayi hade da kurawa Abba ido, a haka gari ya waye su.
A kofar fita Abba yayi Karo da Mummy, ta Harare shi tare da fadin daga ina Ka fito.
Kallo bata ishe Shi ba ya sa Kai ya nufi masallaci.
Hafsat ce kishingide tana tunanin yanda rayuwa ta sauya Mata....tayi ajiya zuci hade da fadin Allah ya kawo min karshen wannan abun.
 Kwankwasa kofar da akayi ne ya farfado da ita daga duniyar tunanin da takeyi.
A tunanin ta Mummy ce, don haka ta gyara kwanciyarta.
Sai dai kuma idan da mummy ce idan ta kwankwasa ba'a bude ba, sai ta Shiga zuba Ashar, Tou Amma wannan kwankwasan ta sha banban sabida a natse ma akeyin da, don haka ta Mike ta bude kofa.
Kanuwar mahaifiyar ta ce tsaye, da wata Mata da bata waye ta ba. Ta daka tsale, sai a jikin kanuwar mahaifiyarta din, ta rungume ta kam, tana me farin ciki, nan kuma ta fashe da kuka.
Bayan sun natsu, kanuwar mahaifiyarta ta dube ta tare da tamabayar ta "yaya nagan duk kin lalace? Ko duk cikin be"
Batayi wata wata ba, ta kwashe duk abinda ke faruwa ta fada Mata.
Kuka sosai kanuwar mahaifiyar ta ta Shiga yi, Hafsat da bakuwa su suka koma suna bata hakuri, da Kar tayi shiru. Jim kadan ta Mike ta Shiga hada kayan Hafsat "Ko awa daya Bani fatan ki Kara a wannan gidan" ta fada.
Cikin kankanin lokaci suka dibi iya kayan da kawai Hafsat zatayi anfani da su, sa'anan suka fice.
Hafsat tana son Abba, tana kuma tausaya masa, Babu kamar yaya Sameer... Jikinta yayi matukar sanyi ganin zata barshi  a wannan gidan.
Amma kam wani abin al'ajabin shine duk yanda Mummy tayi tayi Don gani ta Shiga tsakanin Ya Sameer da Abba, abin ya Kiya... Asalima duk sa'anda ta dauko zancen ya Sameer, idan ransa ya Kai dubu Duka suke bacci, daga karshe yayi Mata kashedi da Ya Sameer, da ta gane haka sai ta dunga manafurcin son da a gaban abba, a bayansa kuwa sai tayi ta musguna masa.
Bayan tafiyar Hafsat rayuwa Ya Sameer ya Shiga garari, mummy bata kaunar ta bude idon ta ta gan Shi..
hakan ya Yan uwansa matsa masa da ya Kara aure sabida Baya zqman gida, balle yasan abinda ke wakana da Sameer.
A lokacin mummy ta haifi yarta ta farko "Hadizatu" Shi kuma abba ya Kara aure.
Read More »
Designed by Jide Ogunsanya.